0% found this document useful (0 votes)
4K views186 pages

AUREN HUCE-HAUSHI

The document narrates a story involving characters such as Alhaji Sulaiman and Malam Bukar, who are engaged in discussions about marriage and familial relationships amidst cultural and spiritual contexts. It highlights the complexities of a proposed marriage between Musbahu and Zahra, facing opposition from Zahra's mother, which leads to emotional turmoil among the characters. The narrative is rich with cultural references, prayers, and the significance of community ties in the face of personal challenges.

Uploaded by

yayausee
Copyright
© © All Rights Reserved
Available Formats
Download as TXT, PDF, TXT or read online on Scribd
Download as txt, pdf, or txt
0% found this document useful (0 votes)
4K views186 pages

AUREN HUCE-HAUSHI

The document narrates a story involving characters such as Alhaji Sulaiman and Malam Bukar, who are engaged in discussions about marriage and familial relationships amidst cultural and spiritual contexts. It highlights the complexities of a proposed marriage between Musbahu and Zahra, facing opposition from Zahra's mother, which leads to emotional turmoil among the characters. The narrative is rich with cultural references, prayers, and the significance of community ties in the face of personal challenges.

Uploaded by

yayausee
Copyright
© © All Rights Reserved
Available Formats
Download as TXT, PDF, TXT or read online on Scribd
Download as txt, pdf, or txt
Download as txt, pdf, or txt
You are on page 1/ 186

❤️AUREN HUCE HAUSHI.

❤️

MAMAN FATIMAH.

DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIKAI SALATI DA DAUKAKA DA AMINCI SU TABBATA GA
FIYAYYAN HALITTA ANNABIN RAHAMA MUHAMMAD BIN ABDULLAHI DA ALAYENSA DA SAHABBANSA
WANDA SUKA BISHI HAR ZUWA TASHIN ALQIYAMA.

Wannan littafin kifkirarran labari ba'a yishi Dan wani ko wata ba duk abinda akaci
karo dashi Arashi ne kawai.

This Book is dedicated to you Ten sisters.


Allah ya Kara Mana zumunci.

Paga one

..........A hankali motar da shigo layin dai dai wani katafaren gate ta tsaya,
yanayin yanda take fidda wani Dan Kara alamune dake nuna motar tayi dogon zangon
tafiya, direban Bai Danna Horn ba bara a kaiga bude gate din gefen wata bishiyar
dorawar tururawa ya karasa da motar, wasu dattawa ne su buyi suka fito daga bayan
motar yayin da wani matashi ya fito daga mazaunin direba, Mika yayi dareban tare da
salati.
Kofar gidan suka nufo da kafarsu Dan matshin be yayi nocking kamar day biyu kafin
wani dattijo ya leko ta wata karamar kofa jikn gate din.
Da sauri ya bude kofar Yana fadin "A'a Alhaji barkan ku da zuwa kin Sha hanya
sannunku" tare da Basu hannu sukayi musabiha suna fadar "wlh kuwa malam Sani ya
muka sameku?".
Cikin fara'a yake fadar "Alhamdulillahi".
Kafin yayi gaba Yana cewa "Bari nayi Muku iso gurin Alhajin Allah ya taimaka Yana
nan".
Harabar gidan suka shiga suka rufawa malam Sani baya zuwa bangaren Mai gidan inda
yake ganawa da bakinsa.

Lokacin da suka karaso gurin kofar shi Kuma Malam sanin ya fito Yana fadin
"Bismillah ku shiga, sannunku".
Yayi gada da sauri Dan cika umarnin Alhajin na Kiran babban Amininsa na kankankan
Malam Bukar.
Da sallama suka shiga falon, Masha Allah komai najin dadin rayuwa akwai shi a falon
tamakar fadar wani sarkin.
Cikin fara'a da sakin fuska Alh Jafar Mai Yadi ya nufo bakin nasa Yana fadar "A'a!
Alhaji Sulaiman kune haka cikin wannan ranar ga nisa".
Amma kasan zuciyarsa mamaki ne fall a cikinta shi dai yasan ba wani abu daya taso
da zai kawosu a irin wannan lokacin a kalla suna da sauran kwanaki uku kafin duzo
duk da sun bada duk abinda ake da bukata lokacin kawai ake jira. Amma dai ko meye
Allah yasa Alkhairi ne.
Bayan gaishe gaishe na al'ada daya daga cikin 'ya'yan Ahj Jafar ne yayi sallama ya
shigo Yana gaishe da bakin Yana aje musu lemon da ruwa ya fita.
Wani matashin ne shima ya shigo da manyan warmers da wata yarinya da basket Mai
dauke da plates da cokula da cups Suma suka gaishe dasu suka fita.
Tunda aka Fara shigo da wannan karamar arzikin Alhaji sulaiman ya sadda Kai kasa
zuciyar idan tayi dubu to a bace take.
"Bismillah kuci abinci kafin mu shiga sallah tunda Azzahar ta gabato".
Alh Jafar ya fad'a Yana nufar kofar fita.
Bayan fitar Alhaji Jafar Alhaji Ismail ne ya kalli Yayansa Alhaji sulaiman "Nifa
duk na rude wallahi har na rasa ta inda zamu Fara fad'a musu irin wannan magana
duba da irin karamcin wannan bawan Allah".
Ya fad'a yana Jan siririn tsaki.
Dan matashin daya tukosu ne yayi magana "wlh Daddy naso kun hakura da zuwa ita
Hajiyar tazo da kanta ta fad'a musu abinda ta kulla, ni ban taba ganin irin wannan
ba anyi Abu cikin mutunta juna har an kawo wannan gabar Amma Rana tsaka irin wanna
ta taso Babu Dadi ni wallahi tausayin Musbahun nakeyi ya shiga wani hali Amma ita
ko a jikinta".
Shi dai Alhaji sulaiman Bai Kara magana ba haka Bai ko kalli abincin ba duk da
yunwa da yakeji leonm da ruwa kawai ya sha, Alhaji isma'il da Al-Amin ne sukaci
abincin suka fita zuwa masallacin kofar gidan.
Tare suka shigo gidan bayan idar da sallar har da Malam bukar domin shine limamin
masallacin.
Sabuwar gaisawa suka karayi Amma wannan lokacin Al-Amin Bai biyosu ba.
Alhaji sulaiman ne yayi Qarfin halin Fara magana Yana kallon Malam Bukar "Dan Allah
malam ayi hakuri da abinda mukazo dashi WALLAHI badan Nan gidan bane Babu abinda
zai Kara dawo Dani garin Nan".
Yayi shiru ya kasa karasa maganar saboda wani abu daya tsaya Masa a makogwaronsa
yana masa tukuki.
Shima Alhaji Jafar wani abune ya tsirga masa har tafin kafarsa ga wata irin faduwar
gaba taba gaira ba dalili.
Shiru falon ya dauka na wucin gadi kafin Malam Bukar ya magantu "Alhaji ka Fadi ko
menene ba wata matsala ita rayuwa ba yanda Bata zuwarwa bawa ko Dadi ko akasin
hakan, Kuma duk musulmin kwarai ai yasan kaddara, ba damuwa ai and Zama daya".
Alhaji Ismail ne ya karbi maganar ganin yayan nasa bashi da niyyar cigaba da
maganar.
"Ayi hakuri Malam kan maganar auren yaron gurinmu ne da yarinyar gurinku, wata
fitina ta taso yau kwana uku kenan ana Abu daya mahaifiyarsa ta kafe kaida fata
Bata amince ya auri Zahra ba duk yanda mukaso gyara abun ya gagara karshe ma cewa
tayi idan har Musbahu ya auri Zahra Bata yafe Masa nononta daya sha munyi munyi da
fad'a Mana dalilinta na wannan cin zarafin Amma ta kekashe taki fad'a karshema abun
ya zamar Mata lalura kamar ta jinni". Tunda ya Fara kora bayani Alhaji Jafar ke
maimaita Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, domin duk wani karfin gwaiwarsa ya
Kare wannan wace irin musiba ce kullum idan auren yarinyar nan ya taso sai an Sami
wani akasin ya taso shi Lamarin Nan ya rasa yanda zeyi dashi.
Malama Bukar ma rasa abin fad'a yayi duk wani kuzarinsa ya Kare.
Yayin da su Alh Sulaiman suketa nanata ban hakuri.
Cikin muna juriya da dattako Malam Bukar yace "haba Alhaji ba komai kasan komai
nufi ne na Allah Daman Bai Qaddari shine mijinta ba, Allah yasa hakan yafi musu
Alkhairi su duka'.
Gaba data suka amsa da Amin.
"Amma dai Abu baiyi Dadi ba wallahi ba Baki nayi musu ba Amma kafin a Sami Mai
nagaratr yarinyar Nan zasu Dade suna nema" cewar Alhj Ismail.
Har gurin mota suka raka bakin, har suka daga bakinsu Bai Dena bada hakuri ba.
Bayan tafiyarsu falon su Malam suka dawo jiki a sanyaye duk Lamarin ya cakule
wannan wace irin kaddara ce ke bibiyar karamar yarinya haka aure dai dai har uku
ana fasawa.
Cikin nuna damuwa Alhaji Jafar ya kalli Malam Bukar yace "malam inshallah Allahu
wannan karon zan aurar da Fatima tunda Naga lamarin bana arzki bane ko meye in Sha
Allah sai Naga bayansa'.

Tunda Alh ya Fara magana Malam Bukar ke girgiza Kai shima lamarin ya kaishi makura
yasan lamarin yarinyar akwai magauta a cikin Amma ganin an samu rata Mai yawa a
tsakani ya dauka abun ya wuce ne.
Cikin nuna alhini Malam ya kalli amininsa yace "Dan Allah Alh kayi hakuri kada kayi
Abu cikin fushi da kace zaka aurar da ita kada azo ayi aikin Dana sani".
Kujerar dake daura da Malam din ya zauna kafin ya sauke ajiyar zuciya.
"Ko daya banyi fushi da ikon Allah ba kawai dai na gaji da wannan wasan ne kullum
na Zama karamin mutum saina Raba I.V na daurin sure azo ace an fasa wasu ma sai su
zageni ace Dan bani na haifi Fatima ba na saka ido ana Mata wannan cin zarafin wlh
da banyi alkawarin daina hada auren zumunci ba da yau ba sai gobe ba zan aurawa
Abdul Hakeem ita. Amma yanzu ma Bata baci ba ka nemi shawarar Mahmud na Nan gurinka
idan ya amince na bashi auren ta".
Cikin kaduwa Malam Bukar ya kalli Alh Jafar yace
"Wane Mahmud din, ba dai na Nan gurina ba?".
Cikin yadda da Kai Alh Jafar yace "shifa nake nufi ko akwai wani Mai wannan sunan
a gurinka?".
Gargiza Kai Malam din yayi tare da fadar "Babu, Amma Alhaji al'marin Mahmud ba
boyayye bane a gurinka kada duniya ta zagemu fa".
Gyara Zama Alhajin yayi kafi ya fuskanci amininsa sosai.
Wallahi Malam bana gudun duk abinda za'a fad'a na yaba da nutsuwarsa idan kaga
ba'ayi ba to shima Allah Bai nufi mijinta bane Amma na jima Ina yiwa 'ya'yana
sha'awarsa".
Kai kawai Malam yake jinjinawa shi lamarin duk yazo Masa a baibai ya jima Yana
nazari akan lamarin Fadima kullum Abu daya yake gani mijinta ba Nan kusa take ba
bil hasal ma wani lamari yake gani Mai girma dangane da mijin nata da wani irin
Haske Amma koda Wasa Bai taba fadawa Alhajin ba sai dai Yana yawaita saka
almajiransa gurin yi Mata addu'a.
Sun jima suna kullawa da kwancewa a tsakaninsu daga karshe suka tsaya a malam ya
tambayi ra'ayin yaron idan yana so la'ba'as.
_______

A hankali take sakkowa daga stair din tamkar wani dawisu Tasha make-up da wata
gawon Mai azabar kyau Sai karamar pos a hannunta daga bayanta 'yan Mata ne su biyu
ko wacce Tasha nata gayun, tun kafin su karasa sakkowa kamshinta Mai saka nutsuwa
ya gauraye ilahirin falon.
Falon a Cike yake da jama'a kowa ka gani ta amsa sunanta sai tsirarun yara.
Da sauri wata ta matso gurin su tana rangada buda, tana fadar "Masha Allah Amarya
Allah ya kade hau da bala'i ya bada zaman lafiya Hajiya Zahra suga bayi farin banza
jikar hardon fulanin Mubi jikar larabawan Jodan da larabawan madinatul munawwara
kaga musu kyawun asali Amarya a gidan Mushahu alherin Allah yakai Miki".
Wata daga cikin matan dake zaune ta tashi ta sunga zubawa marokiyar kudin ita Kuma
tana Kara Koda Amarya Zahra.
Aunty Hasana ce ta fito daga wani Dan korido ta karaso tana kallon kanwar ta ta,
tana Kara tasbihi ga ubangiji daya halicci wannan kyakykyawar surar.
Hannaun Zahra ta rike tana kallon Baba Tabawa Mai aikinta yanda ta zage tana jero
kirari kamar wata marokiya.
Dan murmushi tayi tana fadar "Masha Allah, Baba Tabawa yaushe Kika Zama marokiya
bani da labari?"
Dariya tayi tana fadar " ai ko ban iya ba na koya mu Abu namu bikin uwar dakina
guda kinsan biki na d farar kaza balbela ba gayya ce ba, yakuwar kan kabari kenan
baking cikin 'yan taushe, murucin kna dutse Baki fito ba sai da kika shirya"

Dariya sukayi gaba daya, har gurin da zasuyi bridal shower din kawar Aunty Hasana
da Baba Tabawa suka raka Zahra.
Sun chashe, sunyi hotuna kamar ba gobe sai dai duk Wanda yasan Zahra yasa Bata
cikin walwala haka nan take Jin wata irin faduwar gaba da rashin dadin zuciya Amma
ita kanta Bata San taka maimai me yake damunta ba gashi tun jiya take neman wayar
Mushahun ta kasa samun shi, haka ta abokinsa Deeni itama shiru a yanda sukayi dasu
yau ne ranar da zasuzo Dan har hotel din da zsau zauna sun Kama mukullan ma suna
hannun magaji.
Dadin dadawa yau sukayi za'a kawo ya'yan yayar shi da wasu cussing dinsa.
Sai gurin karfe Tara suka Gama shagalinsu, Zahra Bata koma saman ba inda akayi musu
masauki Sai ta nufi bed room din Aunty Hasana na kasa dakin ba kowa sai kamshin
freshner da turaren wuta yake tashi ga danyi AC ya gauraye dakin. Head din ta cire
ta aje kan bed side locker kusa lamp, gadon ta hau ta kwanta lamo kamar ba mutum
akai Dan ko kwakwkwarwn motsi Bata sonyi wata irin kasala ce ta sauko Mata.
Ta jima a dakin kafin taji alamun bude kofar Bata daga Kai taga ko wanene ba
kamshin da taji ne ya sanar da ita Auntyn ce.
Kusa da ita ta zauna tana Kai hannu jikin.wuyanta tare da tambayar "me yake
damunki? tun safe Ina Kula da mood dinki Sam bakya cikin nutsuwa".
Ta fad'a tana kafe Zahrar da Ido.
Yunkurawa tayi ta tashi zaune tare da fadar "Nima bansan me yake damuna ba wlh
Aunty Sam bana Jin dadin zuciya ta sai zafi take min Kuma gabana sai faduwa
yakeyi".
Ta karasa fad'a tana shashhshekar kuka kasa -kasa.
"Meye Kuma abin kuka? keda zakiyi farin cikin Allah ya kawo lokacin bikin ba kamar
lokutan baya ba da aka dunga samun akasi".
Kanta ta kifa a jiki Auntyn taci gaba da kukan ta marar sauti.
Bata hanata sai tayi Mai isarta kafin ta Sami zarafin magana.
"Aunty wlh Ina ji a jikina kamar wannan ma za'a Sami matsalar kinsan jiya saida
nayi irin mafarkin da nakeyi idan za'a fasa aurena".
Ta fad'a tana Kara goge kwallar data ciko Mata Ido.
Kallon ta kawai Aunty Hasana take ita fa lamarin yarinyar Nan Yana Bata tsoro kada
fa namijin Aljani ya aure ta suna zaune Basu Gane ba.
Karo biyu ana saka bikinta abun Yana lalacewa toga wannan ma, itama fa kawai
daurewa tajeyi tunda Zahra ta fad'a Mata Musbahun Bai kira ba Bai kumazo ba ba wani
Kuma nasa da yazo alhalin ba haka aka tsara abunba, Amma sai tayi ta maza tace.
"Haba Zahra ya Zaki ringa fadar irin wannan maganar kiyi addu'a ba abinda zai Sami
aurenki wannan karon sai Alkhairi, Ina ga da abinda ya hanasu karasowar har yanzu
ki jira zuwa gobe Mana maza kiyi sallah kici abinci a sakonki can ki dauko zuwa an
jima sai kiyi amfani dashi.

_________'
GIDAN MLM BUKAR

Bayan idar da sallar insha'i Malam da sauran manyan Almajiransa suna Zama ana
karatun littatafan fiqihu da hadisan Manzon Allah s.a.w.w, a Nan cikin baban
falonsa ake karatun an kwata shi sosai a zuba kujeru na alfarma, saida aka Gama
karatun sannan sukaci abinci kamar yanda aka Saba kafin Kuma kowa ya nufi nasa
gurin duk da makarantar ta Sami cigaba sosai kamar ba makarantar amajirai ba anyi
Mata tsari sosai a zamanace Dan har hostel garesu sama da kasa da gurin koyon
sana'a Kuma ana musu abinci basa zuwa bara, sannan akwai malamai da aka dauka suna
koyar da karatun boko tun daga mataki primary, junior, zuwa senior, secondary suna
kokarin Fara turo dalibansu zuwa manyan makarantu, sun Sami wannan cigaban ne
karkashin wata kungiyar NGO ne.
Lokacin da Mahmud da Habib zasu fita Malam yayi gyaran murya duk su biyun suka
juyo, Mahmud yayiwa alama daya dawo shi Kuma Habib ya fice..
Nan kusa da Malam ya zauna ta lakwashe kafafuwansa kamar zaman daukar karatu.
A hankali Malam yake Kare masa kallo shi kadai yasa abinda yake kissimawa a
zuciyarsa sai Kuma Allah daya hallice shi.
Sun dauki kamar minti uku a haka kafin Malam ya magantu.
"Mahmud"
Malam ya Kira sunansa.
Cikin ladabi ya amsa Masa da "na'am Malam".
"Kasan dalilin dayasa nayi kiranka?".
Cikin ladabi ya amsa da "A'a"
Cikin wani irin yanayi Malam yace "wani nauyin Kuka aka Dora min Wanda na rasa ta
inda zan Fara maka bayani".
Zamansa ya gyara Yana Kara fuskacin Malam din Yana fadin "Malam ka fad'a min ko
menene ni maiyi maka biyayya ne In Sha Allah".
"Ai kasan gidan Alhaji Jafar nawa za'ayi bikin yarinyar gurinsa ko?"
Kai ya gyada Masa tare da cewa "Eh na Sani ba Zahra za'a aurar ba?"
"Eh ita fa, to an samu wata matsala ne wadda ta haddasa kasa auren a wannan karon
ma kamar lokutan baya Amma wannan sai yafi na bayan Muni domin kuwa saura ba kaiwa
ga Fara bikin Amma wannan Saida abun ya kurace har an saka yarinyar a lalle sun
Fara duk kwaramniyar su ta Mata a lissafi saura kwana uku daurin aure sukace sun
fasa, shine shi Alhajin yace na meni shawararka idan ka amince zaka iya auren
yarinyar ya baka za'a daura muku aure ranar juma'a inshallah Allahu".
Da sauri Mahmud ya dago Yana kallon Malama bakinsa har rawa yake yama kasa furta
maganar dazai fad'a Kai ya shiga girgizawa dafa shi Malam din yayi Yana fadin "ka
nutsu bazamuyi maka dole ba idan bass sonta sai a nemi wata mafutar"
Da kyar ya tattaro nutsuwarsa ya kalli malam yace
"Ba haka nake nufi ba, gani nayi yaushe nakai matsayin da za'a bani irin wannan
yarinyar aure kamar tafi karfina ni almajiri ne wanda ban aje ba banba wani ajiya
ba, kuma tana da ilimi Mai zurfi ba lallai ta yadda ta zauna dani ba".

"Ba wannan nake son jiba daga bakinka fadin Kai ko wanene ba taso ba Alhaji shi
yafi sanin Kai ko waye amsa muke bukata zaka iya aurenta ko bazaka iya ba ?".
Cikin alamar sarewa yace "wane ni ice bana son wannan yarinya na karba na gode
Allah ya saka da Alkhairi".
Ya fad'a cikin wata irin murya Mai sanyi.
"A'a kaje ka nutsu kayi shawara sai ka fad'a min duk huku cin daka yanke, tashi
kaje dare ya farayi".
Yunkurawa yayi ya tashi Yana fadar "sai da fade"
"Allah ya tashe mu lafiya" cewar Malam.

Daga falon malam Mahmud bakin titi ya nufa inda yake tunanin ganin Habib Yana son
ya karbi lifan dinsa zaije wata unguwa.
Gurin Ashiru Mai shayi ya Fara zuwa baya nan sai su salisu da Bashir Suma duk
mutanen Mahmud ne hannu ya Basu saka gaisa sannan ya tambayesu Habib wani ne daga
can gefe yace "ai yanzu ko runhu ka rike yana gurin Ubaidat kasan mutumin naka Yana
neman dauko dala ba gammo".
Ya karasa fad'a Yana dariya Bashir ne yace "ko wani Abu ne Naga ko Zama bakayi ba"
Da tsaki yayi Yana Dan dafe kujerar kusa dashi Yana fadar "wlh lifan dinsa zan
karba zan danje unguwa".
"Kai haba saboda lifan kake wannan zagaye zagayen ga nawa kayi amfani dashi mana".
Ya fad'a Yana Miko Masa makullin ya karba Yana godiya.
Kai tsaye zaranda hotel ya nufa.❤️ AUREN HUCE HAUSHI❤️

MAMAN FATIMAH.

✨Page two✨
________
Safa da marwa take tun bayan gama sallar insha'in ta, ta Kira layin wayar tafi sau
shurin masaki Amma ta kasa samun Wanda take nema, gumi ne yake fama tsatsato Mata
daga goshinta, ta kasa zaune ta kasa tsaye.
Gafen gadonta ta koma ta zauna Kara kiran tayi cikin ikon Allah sai Kiran ya shiga
da sauri ta nufi kofar toilet dinta na daki ta shige.
Bata tsaya amsa sallamar wadda ta Kira din ba ta Fara magana "Asabe me yake faruwa
ne tun jiya nake neman wayarki Bata shiga Ina cikin tashin hankali komai fa Yana
nema dagulewa, ba alamun nasara a wannan karon tunda komai ya kankama".
Shiru tayi tana sauraran wadda ta Kira Asube ta jima tana sauraran ta kafin tayi
dariya tace "haba yanzu naji magana da har hankalina ya tashi ki rike sauran
maganar sai kin shigo gobe ma karasa".
Ta kashe wayar ta bude kofar toilet din ta fito cikin farin ciki da walwala sabanin
yanda ta shiga.

___
Mahmud.
Ya jima a cikin hotel din kafin ya fito zuwa gurin securities din da alama sun saba
sosai Dan yanda suke bashi girma sai abin ya baka mamaki makullin lifan din Wanda
ya barwa ya miki Masa tare da fadar
"Yallabai an zubo petrol din".
Lokaci daya Kuma Yana Miko Masa kudi, kallon na mine yayi masa.
"Kudin sunyi yawa ne a sayan man Saida naje na duba maga yawansu". Ya fad'a Cike da
ladabi, hannunsa ya zura a aljihun wandon jikinsa ya dauko wasu ya Kara Masa,
sannan ya Kuma dauko wasu ya bashi alamar ya baiwa abokan aikinsa.
Godiya suka dunga jero Masa Dan inda sabo sun saba da Alkhairinsa.
Kai tsaye gurin Ashiru Mai shayin ya nufa duk da dare ya Fara Amma yasan yanzu 'yan
term din nasa Basu Isa tafiya gida ba Dan sukan Kai har daya na dare suna hira.

Makullin lifan din ya mikawa Bashir Yana fad'a "Jazakumullahu khairan".


Habib ne yace "Wai Dan Allah Ina kaje a rufe wayarka tun dazu nake nemanka fa daga
inje in dawo kawai na nemeka na rasa sai su Salisu ne sukace kazo nemana ka wuce
unguwa".

Kusa da Habib din ya zauna na fadin "wash Allah wlh duk na gaji".
"Da kayi aikin me".
Cewar Habib.
"Bari kawai ba aikin da nayi Amma Wanda yake fuskantoni ba sauki kazo muje gida
akwai sakonka da Malam ya bani na baka".
Ya fad'a Yana kikewa tare da mikawa su Bashir hannu yayi gaba gurin lifan din
Habib.
Dakinsu Mahmud ya bude daki ne madaidaici da gado guda biyu da wardrobe ta jikin
bango sai mirror irin na croom din Nan da AC, kasan dakin shimfide da tayil,
lokacin da akazo aikin NGOs din ne aka yiwa Malam nashi falon da Kuma irin wadannan
dakunan guda uku sai Kuma dakunan Yara almajirai sama da kasa.
Dakin sai kamshi yakeyi, sau da yawa Habib kanshi Yana mamakin wasu abubuwan na
Mahmud sai dai ba fuskar da ze tambaye shi duk kuwa da amincin dake tsakaninsu.
Saida Mahmud yayi wanka ya saka kayan barci sannan ya
Zauna a gefen gadon Yana fuskantar Habib kafin yace.
"Kai inaga fa nan da kwana uku zan ankwance".
Ya fad'a yana wani killer smile.
Zabura Habib yayi ya tashi zaune sosai Yana fadar
"Kamar Yaya?"
"Kamar yanda na fad'a maka, tsayar Dani da Malam yayi kenan yace Alh Jafar ya bani
auren yarinyar Nan da ake bikinta wadda Abdul Hakeem ya kawo Mana IV last week".
"Ban Gane ba bafa ta Yaya hakan zata faru?"
Kafada ya dage alamun shima Bai Sani ba.
"Dan Allah kayi min bayani yanda zan fahimta a sakani a duhu wallahi".
"Iya abinda na Sani kenan kawai ance an bani idan inaso inyi shawara".
Cikin madaukakin mamaki Habib yace "to Kai ya kace masa?'
"Me zance kuwa na karba na gode, kasan har abada ba jayayya tsanina dasu iyayene
sak, sun min abinda kowane uba yakewa dansa sun min gata sun Kula Dani lokacin da
bana Gane gabas bane Gane yamma bana Gane fari bana Gane Baki,
Sun zamar min garkuwar data Hana kowane harbi ya sokeni, Toni kuwa wanen irin
butulu ne da zan watsa musu kasa a Ido sufa sun san waye ni Amma suka runtse idonsu
suka bani basu nuna min kyama ba, sannan ka dubi yarinyar da aka bani diamond ce fa
a cikin gold kasan bani da abinda zan tunkari irin wannan yarinyar da sunan soyayya
bare har aje ga maganar aure".
Tunda ya fara magana Habib yake Masa kallom mamaki Yana jinjina karfin ikon Allah,
lallai wani lamarin sai Allah.
Da kyar ya Sami zarafin fadin "Masha Allah! Allah ya Sanya Alkhairi Abu yayi Dadi
amma fa ka daina fadar Wai baka da abinda zaka tunkare ta wlh kafin wanna lagwanin
Wanda zata aura say millions shi har wani namiji ne kawai Abu daya Sani yana da
kudi mu Kuma bamu dasu Amma muna da abinda bashi dashi".
"Kamar Yaya me muke da shi Wanda shi bashi dashi? ka duba fa kaga irin yanda yake
shiga babban yaro ne ga manyan motoci mu Ina muka gansu"
Dan karamin tsaki Habib yayi Yana fadain "ana gabas kana yamma ana maganar nagarta
da mutunci da cikar Kamala da siffar mazantaka kana wata maganar, mu an fad'a maka
haka zamu dawwama bazamyu arzikin ba".
Dariya Mahmud yayi "maida wukar abin Bai Kai haka ba ko Daman haushinsa kakeji ne
ban sani ba?"
Habib tsayawa yayi galala Yana kallon Mahmud kafin ya karayin wani tsakin "Allah ya
sauwake zanji haushinsa Ina ruwana dashi kawai da Daman can no banga dacewar su ba
Kai Nifa idan Malam yasa Yara suyi Mata addu'a har cewa nake suyi Mata addu'a Allah
ya Bata gwarzon miji na nunawa sa'a".
"Amma wallahi Habib baka da mutunci shi wannan ba gwarzo bane?"
"Ina fa namiji Yana rausaya kamar mace".
"Kaga Yi closing din wanna chapter din yayi zamuyi da wannan lamarin kaga dai komai
fa Sai a hankali Dan abinda nake Sami daga wannan organization din ba Isa wannan
shidimar zasuyi ba ga yarinyar Mai zafi ni kamar ma tsoronta nakeji fa".
Ya fad'a Yana dariya.
Sun jima suna tattaunawa yanda zasu bullowa lamarin.

_______

Tunda garin Allah ya waye Amma take ta kaiwa da kawowa tsakanin kitchen da dakinta
zuwa dakin Baki, Saida aka kammala abincin breakfast aka babba mutane sannan ta
samu ta koma daki inda ta samu kanwar Babarta Inna Maimuna a uwar daki.
Kallonta tayi "Asma'u ya kamata ki karya kinsan Ina tunanin zuwa anjima gidan ze
Fara cika bazaki Sami damar Zama kici wanti abun karki ba, waini ina Hajiya Mama ne
Naga yau Bata leko ba?"
"Tana bangaren Alhaji Nima nayi wannan tunanin Amma ai lafiya ita keyin shiru".
"Hakan ne Kam".
Cewar Inna maimuna.

******
Katagum road

A dakin Aunty Hasana Zahra ta kwana ita da Autart Haneefa, sai kusan goma ta tashi
daga barci wayarta ta Fara dubawa ta tarar da missed calls rababa Amma Sam babu
nasa ko na wani daya dangance shi, duk na kawayen da abokanin arziki Bata bi
rakansu ba ta shiga toilet wanka tayi, lokacin data fito Sajida ta Samu a dakin ta
shigo Mata da breakfast dinta nan, tunda ta fito Sajida ke kallon ta har ta karaso
gurin mirror inda sajidar ke zauna murmushi Zahra tayi Mata tana fadin "wannan
kallon fa ko na canza Miki ne?".

Kai ta gyada Mata "gaskiya Kam ba haka na Saba ganinki ba, meye yake faruwa ne?
nifa tun jiya nake nema Deeni da wannan cussing din na Mushahu Aliyu, ta Aliyun
tana shiga ba'a dagawa Amma su sauran wayoyinsu switch off".
Da rausayar da kanta tayi tana Dan watsa hannuwa "wallahi bani da masaniyar me yake
faruwa nima hakan take kamar ke Amma nasan dai kome aje ciki yau dole su shigo
garin. Ni wallahi da Aunty Hasana zata yadda da an hakura da wannan mother's day
din nifa duk abin ya fice min daga Rai gani nake shima wannan aure ba yuwuwa zaiyi
ba nasan dole da wata a kasa ai ba haka muka tsara abubuwan ba Amma kin ko daya fa
basuyi attending ba".
Ta karasa maganar idanunta na cikowa da hawaye.
Hannunta Sajida ta kamo ta rike tana fadar. "Hqba Bestie kada kiyi Kika in Sha
Allah ba wani matsala sai Alkhairi kada ki Bata lokacin farin cikinki mana".

Aunty Hasana ce ta shigo da sauri alamar wani Abu zata dauka turus tayi tana fadar
"ke me zan gani Zahra kukan dai? haba you have to be very strong Mana kada ki yadda
aga rauninki a kowane janibi ki Zama jaruma Mai iya fuskantar ko wane kalubale,
kada ki kara saka damuwa a zuciyarki zan fita Amma in Sha Allah bazan Dade ba ki
shirya kuje sama naji suna cigiyarki".

A bangaren Mahmud kuwa bayan anyi sallar Asuba a masallaci ya zauna yayi azkar
dinsa Saida gari ya Fara haske sannan ya fito lokacin su Malam sun Gama karatun da
sukeyi da maza magidanta.
Da sallama ya shiga falon nasa lokacin Abubakar Yana mayar da littatafan
mazauninsu, sai da ya zauna sannan ya Dan rankwafa Yana gaishe da malam, Amma sai
ya moko Masa hannu sukayi musabiha Yana fadin. "hakan shine sunnar Annabin Rahama
Muhammad s.aw.w."

Shiru falon ya dauka bayan fitar Abubakar Malam Bai tofa ba haka Mahmud shima,
Malam ne ya kauda shirun "Ya ake cikin Mahamuda wace shawara ka yanke?".

"Ba damu Baba Malam na karba na gode ayi min godiya Allah yasa hakan yafi
Alkhairi".
"Allahumma Amin. Allah ya Sanya Alkhairi ya Baku zuri'a Mai Albarka Allah yasa ace
gara da akayi hakan"
A zuciyarsa yake ta amsawa da Amin.
Harya yunkura zai tashi Malam yace "koma ka zauna, Ina zaka bamuyi maganar inda
zaka ajeta ba da sauran shirye-shirye".
Sadda Kai yayi haka Nan yaji wani irin nauyin malam din ya taso Masa.
Kansa Yana kallon kasa yace "so nake muyi shawara dasu Habib yanda muka yanke saiya
fad'a maka".
"A'a ba haka za'ayi ba nizan bada sadaki da kayan goro da alewa sai Kuma shaddoji
da za'a kawo an jima Suma dinkakkune tunda abun yazo a kurace, sai Kuma gidan Nan
na Hayin Banki mukullin na gurin Binya tun jiya na bashi nace yau zakuje a duba
abinda za'ayi Masa".
Mahmud kasa magana yayi shi wannan gatan har yayi Masa yawa komai anyi Masa.
Rarrafawa yayi kamar yaro har gaban Baba Malam ya rinka godiya har Saida yayi Masa
fad'a.

********
Amma ce da Inna a uwar dakin Ammar bayan dawowar Ammar daga bangaren Alhaji cikin
tashin hankali Innar ta kalli Ammar tana fadin ke Asama'u wace irin magana ce
wannan yaushe hakan ta faru duk bamu da masaniya?"
Dan nisawa Ammar tayi.
"Wallahi Nima ban sani ba Amma yace kada yaji kada ya gani naja bakina nayi shiru
yana zargin kowaye yake lalata lamarin auren yarinyar Nan na kusa yake tunda yace
min Malam Bukar ne yayi binciken Dan haka bazai cewa kowa komai ba har sai bayan
daura auren tukunna".
"Ya fad'a Miki waye mijin?"
Kai ta girgaiza Mata alamar A'a.
Nifa Ina gudun garin AUREN HUCE HAUSHI a kwaso bara gurbi Wanda za'azo ana Mana
dariya".
"Gaskiya bana tunanin haka Inna mu bita da addu'a kawai Allah ya Zama gatanta yasa
albarka a ciki.
❤️ AUREN HUCE HAUSHI❤️
Story & written
By
✨MAMAN FATIMAH.✨

INA MIQA SAKON TA'AZIYYATA GA 'YAN UWANA


HAJIYA MARIYA ALIYU ( JIMMAN ADO)
HAJIYA BILKISU ALIYU (UMMA IKKI)
HABIBA ALIYU (UMMA HABIBA)
Na rasuwar mahaifinsu ALHAJI ALI DAN HAYA MAGAMA KAZAURE.
Allah ya jikansa ya jaddadda Rahama a gareshi tare da sauran musulmi.

Page three 🔷

.............. Tunda Mahmud ya fito daga gurin Baba Malam yake nazarin yanda zai
bullowa lamarin, baya son ko kadan a Sami kurkure, guri ya Sami nesa da makarantar
kasancewar Alhamis ce Yara basa karatun safe sai ya zamana yawancin su suna dakunan
su.
Waya ya Ciro daga aljihun wandonsa yayi dialing din number Bata jima tana ringing
ba kada daga magana ya Fara "kana jina Sameer sakon Dana turo maka kada a samu
kuskure kayi kokarin ganin komai yayi yanda ya kamata fa".
Dan Jim yayi alamun ana fad'a Masa wani abu
"Ok to shi kenan take care".
Ya kashe wayar.
__

Nama ne da kayan miya ake ta shigo dasu cikin gidan da manyan kuloli sabbi Hajiya
mama ce a kofar kitchen din na tsakar gida tana bada umarnin abinda za'ayi, yaran
dake shigo da kayan ta kalla "wannan fa daga Ina?".
Magaji ne ya Bata amsa kafin yaron data tambaya ya fad'a Mata "tare muke Mama na
abincin bakin Abba ne".
"Ikon Allah Naga ai an kawo wasu da sassafe dazu gasu nan har an kusa Gama
aikinsu".
"Eh to shi dai yace a kawo wadannan ma".
Magajin ya fad'a Yana shiga dakin Amma.
"Kai dawa Kuma kake tafiya kana magana"
Cewar Inna maimuna.
Kusa da ita ya zauna Yana fadin "nida Hajiya mama ne kayan miya ne da Naman rago
Dana kaji Abba ya Kara badawa aka kawo shine take magana ko yayi yawa kame?"
Dan murmushi Amma tayi "Abban Nan naku baya son a zauna lafiya wallahi magaji
kamar zai aurar da Yara uku sai irin wannan shidima yake haka".
Kai magajin ya jinjina "Amma kenan kin manta yanda Abba keson Zahra ai kawai kowa
ya zuba Ido ana auren uwar masu gida tab ai kowa sai yasan anayi Yasin, ki Bari
kawai Ammah Nan zan kawo nama a ajiye min".
Ya fad'a Yana dariya ya nufi kofar fita saboda sallamar wasu Mata da yaji a kofar
dakin.

___

Daki Mahmud ya koma ya samu Habib a tsaye a tsakar dakin da alama daga wanka ya
fito, saida ya Gama wayar sannan ya kalli Mahmud.
"Wai ina kaje ne? Naga fitowarka daga gurin Baba Malam kafin na saka caji na nemeka
na rasa, Bilya ne ya kirani Wai mu sameshi a hayin Banki shi Yana can yaje da masu
aiki su duba yanda za'ayi gyaran"
Dan Dafe Kai Mahmud yayi ya Dan fesar da numfashi.
"Ikon Allah Wai Daman kamar jira kuke ace za'ayi min auren Nan kowa sai rawar jiki
yake yi, daga fad'a shine har ya want kwashi jiki da masu aiki ya tafi tun garin
Bai Gama watstsakewa ba".

"Naka wasa ne Alaji, aini yanzu haka mun Gama magana dasu Bashir sunce mun gasu Nan
zuwa har suna cewa shegen zurfin ciki ne da Kai baka fad'a musu ba jiya ko kunya
kakeji irin ta Mata".
Ya karasa maganar Yana dariya.
Har ya nufi gurin mirror ya tsaya "kaji na manta ba Salis yace na tura Masa
cikakken sunan da ze saka a IV da zeyi a waya ya turawa friends na kusa".
"Ok ba matsala ka tura Masa kawai da sunan aika Sani ba saina maimaita make ba".

Misalin karfe Sha daya na safe wata bakar Hilux sabuwa kar ta dira a kofar gidan
Malam Bukar.
Lokacin yaran sun firfito suna sugogin su masu wanki nayi masu wasa nayi Amma idan
ba fada maka akayi bazaka taba cewa yaran Almajirai bane kowa cikin tsabta Kuma a
lokacin anyi hutun makarantar book shi yasa basayi tunda suma tsarin makarantar
gwamnati suke bi.
Mutane biyu be suka fito daga motar da sauri 'yan samarin dake kusa taso da sauri
suna fadin barkan ki da zuwa kasancewar sun saba dasu sosai sune wadanda suke kawo
musu tallafi daga organization din.
Da sauri suka bude musu falon saukar bakin Malam kafin wani ya shiga ya fadawa
Malam din.

Ba jimawa Malam din ya fito suka gaisa a mutunce, sannan suka gabarwa da kayan
abincin da suka kawo sannan suka gabatar Masa da bukatar daukar Mahmud zuwa wani
taron karawa juna Sani na makarantun tsangaya Wanda za'ayi a kano, tunda shine
Wanda suka dauka aiki a Nan tsangayar yake wakiltar su kuma gobe juma'a za'ayi
taron na Rana daya ne kawai.
Dan Jim malam din yayi kafin yace " Ikon Allah malam Sameeru ga koshi ga kwanan
yunwa WALLAHI shi Mahmudan dai baze Sami damar halartar taron nan naku ba, domin a
goben in Sha Allah za'a daura Masa Aure".
Cikin wani irin madaukakin mamaki Sameer dake kusa da Malam din Kuma jagaban
tafiyar ya kalli Malam Yana cewa.
"Aure! Kuma Malam?".
Kai ya jinjina Masa alamar tabbatarwa, "yanzu haka suna can gidan da ze zauna ana
dudduba gyaran da za'a Masa duk da gidan Bai jima da kammaluwa ba kasan kullum abin
duniya sabuntashi akeyi".
Kai ya jinjina ya hadiye wani yawu da kyar shifa duk ya shiga rudu meye hakan Wai
Kuma.

Fara'ar dole Sameer ya kirkiro Yana kallon Malam yana fadar "Masha Allah Abu yayi
Dadi to ai mu wannan lamarin namu ne munzo a dai dai kenan tunda Abu ne na
ma'aikacin mu koma kunya zatayi Masa malam kada kuyi komai yanzu zanyi waya za'ayi
duk abinda ya kamata tun daga abinda ango ze saka har abinda za'aci duk Yana
karkashin kularmu tunda mu yakewa aiki, Kuma zamu zauna sai an daura auren damu in
Sha Allah. Maganar taron Kuma sai dai a daga zuwa wani lokacin Dan bamaso wani yayi
missing gaskiya".
Tunda Sameer ya Fara Kora bayani malam ke jinjina Kai saida yake Aya sannan ya Sami
zarafin magana.
"To malam sameeru anyi haka abin fa da yawa kids bakuzo da Shirin wannan abun ba
kunzo Kuma kuyi ya kuyi makarbiya ai da wahala abun".
Dariya Sameer din yayi Yana fadar "malam ba abunda ze gagara kungiyoyin masu
karfi ne, yanzu ma ga wannan saboda biyan sadaki".
Ya aje Masa cheque na Banki suka Mike Yana fadar "Bari na Nemo shi a waya sai muje
muji meye shirye-shiryen nasu, a huta lfy".
Suka kad'a suka fita.

_____
Kyakykyawan guri ne Aunty Hasana ta kama inda za'ayi mother's day din gurin ya
kayatu ba karya kudi dai an kashe su gurin Kama event center din, anyi taron Mata
'yan gayu kamar ba gobe amarya tasha kyau kamar a dauke ba boye.
Ga wani slow music da mc din ya saka na wakar Amarya da ango kowa ka gani cikin
nishadi yake sabanin Amarya da Yayarta Banda ta Riga ta gayyato mutane harda
wadanda sukayo Mata tafiyayya sukazo da ba abinda ze saka tayi wannan taron to Amma
mutum Bai Tara Sani ga Allah ba.
An raba kayayyaki na alfarma na bikin, sai magariba taron ya tashi, zuwa yanzu 'yan
Qananan maganganu sun Fara fita a tsakanin kawayen Zahra tunda har zuwa lokacin ba
wani duriyar Ango ko wani nasa, sai Dan kus-kus ake abinda yafi bada mamaki bai
wuce ganin anata faman programs ba normal.

Su Mahmud Basu samu kansu ban sai bayan sallar insha'i lokacin suka zauna Dan wuni
guda suna ta faman sunturi daga can zuwa can abin dai ba sauki dan su sameer suna
zuwa gidan suka babbago aikin da sai anyi sati ba'a Gama ba Dan sunce tsarin gidan
gaba daya za'a sake, basunda ta cewa tunda oganninsu ne sai godiya suka dunga
zubawa harda su Bashir.
Gurin karfe goma malam ya Kira Mahmud a waya yace yazo cikin gida ya same shi.
Saida ya leka falon iya Abu suka gaisa tana faman jansa tana ita ce ta karfen Dan
haka ita zata koma sabon gidan a kawo Amarya nan.
Da haka ya karasa turakar malam Yana zaune a falo Yana sauraren wa'azi a TV, yayi
sallama Malam din ya bashi izinin shiga, Nan kasa ya zauna Yana gaishe da malam
din.Wasu manyan ledoji malam din ya nunawa Mahmd Yana fadin.

"Dauko wadan can kayan ka duba daya Wanda nasa a kawo maka ne biyun Kuma wadannan
masu kungiyar ne ta taimakon tsangayu suka kawo ga lemuka can da ruwan roba sun
kawo yafi catoon dari sunce kada ayi abinci ma duk za'a kawo, har na rasa da wane
bakin zan gode musu, sai dai Ina rokon Ubangiji s.w.w yafi mu yabawa, naji su
Habibu ma sun ce sun dauko aiki Mai yawa a wancan gidan ko?"
"Eh wallahi munyi-munyi su Bari suka Kiya Wai haka aikin Qungiyar yake in dai kana
musu aiki idan wani Abu ya sameka Mai Dadi ko marar dadi su zasu tsaya maka".
"Alhaji yace min kun shiga dazu bayan sallar magariba har da bakin kunyi Masa
godiya, kun kyauta haka ake so".

Lokacin Mahmud ya koma dakinsu Habib baya Nan gurin da yake aje makullin lifan
dinsa ya duba ya kuwa you sa'a yana nan, lodojin ya zube a kan gado ya dauki
makullin ya rufe dakin ya hau mashin din yayi gaba.
Bai dawo ba sai kusan Sha biyu da rabi har lokacin kuma Habib baya dakin yasan suna
can suna kujuba kujuba.

Yauma Zahra taso kwana a dakin Aunty Hasana saboda tana bukatar kadaicewa Amma
Sajida ta matsa Mata da mita Saida suka tafi Amma fa zuciyarta Bata da nutsuwa
gashi tana ankare da Aunty Hasana tun jiya da dare a taje can gida cikin gari Bata
da nutsuwa ko alama Amma tana ta kokarin ta basar sai dai ko Yaya mutum ya shiga
damuwa indai kayi Masa farin Sani zaka fahimta, ita Abu mafi Bata mamaki yanda
aketa kwaramniyar bikin ba wani canji sai dai abunda baza'a rasa ba duk da Daman ba
wata muguwar bidi'a ba ta had'a, walima ce kawai Bata Sami ba saboda tace ita malam
Tijjani Ahmad zeyi Mata Kuma bayanan yana Umara.
Tunda tayi sallah ta kasa tashi daga gurin tana kallon su Sajida sunata sabgarsu,
Amma ita da wata irin faduwar gaba ta tashi ta rasa nutsuwarta kwata kwata da kyar
ta tsahi sauko kasa gurin Aunty Hasana a fall ta sameta tana hadawa Abbansu Haidar
break fast.
Gurin dining din ta karasa tana gaishe shi sannan gaida Auntyn.
Dakin Auntyn ta shiga kwanciya tayi tana ta faman sakawa da kwancewa zuwa yanzu dai
tasan tabbas da matsala sai dai yanda ba Wanda ya fad'a Mata shi yasa itama ta
zubawa sarautar Allah Ido taga iya karshen film din tasan ko menene yau dai za'a
yita ta Kare tunda yau ne deadline duk wata kunbiya kunbiya za'a zazzageta.

Tun karfe goma Mai yiwa Amarya make up tazo Amma kememe Zahra tace ita bataso a
kyaleta aka dunga yiwa kawayenta, ganin guri ze kure ne Sajida take ta fadawa Aunty
Hasana Saida tazo sannan akayi Mata light makeup Amma fa duk da hakan tayi karshen
kyau, farin material ne ta sakata Mai touching din sky blue sai aka daura Mata head
shima sky blue din takalman da pos din duk sky blue din ne.
Wani san sanyan kyau tayi na ban mamaki, komai na Zahra Mai kyau lallai zaharar ce
Dan duk cikin kawayen Bata da mahad'i.

A babban masallacin juma'a za'a daura auren Masha Allah, ango ya fito Shar abokansa
sai mamakinsa suke Basu taba sanin kyawunsa da cikar haibarsa ya Kai haka ba sai
daya fito sun Sha mamakin kwarai har wasu suka Fara kokonto a kansa, Yana kallon
yanda idanun sukayi Masa caa.
Dan dakakkiyar getzener ta saka ga takalman da agogo ga hula, Sam bazaka taba cewa
Wai alamajirin malam bane ba, ga wani irin kamshin tunda ta tumkaro taron
abokanensa kamshin ya hade gurin.
Daga gefe sameer ne da abokinsa Naraddeen suna tsaye lokacin da Mahmud ya fito
Sameer ya kalli Naraddeen din yace "wallahi wannan guy kwallon Dan duniya ne na
rasa Gane kan alkiblar daya kalla Wai aure zai daura shi kadai kamar marara gata,
ni so nake Naga karshen wannan wasan kwaikwayon nasa.
Daga inda yake tsaye ya kafe Sameer da Ido ko Bai fad'a ba yasan me yake nufi tun
jiya yake tuhumarsa aka zuwa da abokinsa da yayi duk da ya nuna Masa wannan ba wata
matsala bace Amma har yanzu Yana hukunta shida idanunsa.

Masha Allah dubban mutane ne suka shaida daurin Auren FATIMAH ZAHRA AHMAD SANI da
Angonta MAHMUD MUHAMMAD DANGE akan sadaki dubu dari uku lakadan ba ajalan ba.

Daurin aure daya bawa dubun mutane mamaki bare wadanda sukazo daga bangaren Mushahu
sunyi mamaki kwarai sunan Amarya dai shine Amma ba mijin daya gayyato su bane yayin
da yan unguwa ya Zama abin kasawa a faifai ana yawo dashi, da yawa na ganin beken
Alhaji Jafar na aurawa bakon da ba'asan asalinsa ba yarinya kamar Zahra yayin da
wasu ke fadar ai Dan ba 'yarsa bace shi yasa yayin wannan danyan aikin.
.......
❤️AUREN HUCE HAUSHI ❤️

Page four🔷

___________''

Wata marokiya ce irin dattawan Nan da suke bin manyan marok'a ta biyo tawagar masu
dawowa zuwa gida kasancewar gidan ba nisa daga masallacin juma'ar, itace ta
rangad'a guda har sau uku ta Kara da fadin "Alkawarin Allah ya tabbata an daura
auren Fatima Zahara'u da zukeken Angonta Mahmud Ubangiji Allah ya bada zaman lafiya
da kazantar daki Bata shara ba, munzo much arziki mubar arziki a gurinsa.
Kamar saukar aradu haka maganar ta shiga kunnen Hajiya mama, batasan lokacin data
tsallake mutanen falonta ta fito ba dankwalinta a hannu, tana fadin "me naji ana
fad'a wa aka daurawa aure da Mahmud naji kowa".
"Eh haka ne Kam Alkawarin Allah ya ciki Zahara'u ta Zama matar Mahamuda"
Ta debo wata gudar ta Kara rabsawa.
Dai dai lokacin Hajiya kaltume aminiyar Ammah ta fito ta dukulawa wannan marokiyar
kudi sannan ta Mika Mata babbar leda Mai abincin biki har da ruwa da lemo.
Cikin rashin nutsuwa Hajiya mama ta nufi dakin Amma ko sallama Babu ta Fara fadar
"Hajiya kinji abinda naji ko kunnena ne ya jiyo min ba dai dai ba?".
Kallonta duk 'yan dakin suke kafin Ammar tace Mata "nima haka naji kamar yanda
kikaji sai dai ko shirme takeyi ita Mai rokon tunda ba sanin su tayi ba".
"Eh gaskiya Kam sai dai hakan".
Ta juya ta koma daki. Bata zauna a falon ba uwar daki ta wuce, Asabe ce ta rufa
Mata baya, a tsaye ta sameta ta Goya hannu a baya tana Dan Kai kawo a tsakanin gado
da madubi.
Waiwayowa tayi tana kallon Asaben kafin ta zauna a bakin gado, kusa da ita Asaben
itama ta zauna.
Tana fadar "Haba Hajiya Dan Allah ki nutsu bana son ki bada wata baraka a sabgar
Nan keda na fad'a Miki Daman malam na BANDE yace wannan karon aure sai anyi Amma ba
da Mushahun ba, Amma abinda yake daure min Kai malam na banden yace Wanda zata
aura a nesa yake Kuma yaga haske so sai akan lamarin duk yanda yaso ya Bata lamarin
abin Bai yuwu ba shine nace kawai a kyale tunda dai Wanda muke son a fasa da shin
din aikin ya yuwu, nasan dai da wuya ta Sami irin Wanda ta rasa a bay".
"Haka ne Amma abin dubawar waye wannan din sanan me yasa aka kudundune zance? Wai
fa Dan munafurci Hajiya Asma'u cewa tayi Bata Sani ba ke kin yarda Alhaji ze aurar
da Zahra Bata da masaniya, ko meye ma dai kyawaun ya kare a auren Hadi tunda nasan
ba wani sai Mushahun shi Kuma ya Kara gaba kamar sauran".
Ta fad'a tana kwafa, mikewa tayi tana gafar "Bari na fita sai Naga kul uwar daka".
"Allah ya taimaki uwar dakina, aikinki Yana kyau".
Asabe ta fad'a tana mikewa itama.
**********
Daga gurin daurin aure Kai tsaye gidan gonar Alhaji Jafar suka wuce har tawagar
angon bisa umarnin Alhajin tun safe ya turo Mai sunasa (magaji) yaje ya fadawa Baba
malam.
Anci an Sha kamar ba gobe mutane sunyi mamakin irin wannan karamar arzikin dan duk
zarin mutum sai dai yaci ya Bari ruwa da lemo kuwa kamar banza.
Abokan Mahmud kuwa sai Dan biki suke Masa.
A gidan malam ma Masha Allah anci an Sha Yara sun san ana biki a gidansu, Iya Abu
ma tayi nata taron komai baja baja makotanta ma sunsan ana hidimar arzki a gidan
Kuma Suma sunzo Mata harda masu riko abin arzikinsu su kawo Mata.

******** A guje Faruq ya Fado falon Aunty Hasana,danta ne na uku Yana rungume da
babbar rigarsa ta daurin aure daya saka Yana Fadi "Aunty Zahra wallahi Naga mijinki
ba wannan Uncle din bane na kano wallahi wanna yafi shi kyau Baki gani ba yanda
yake rabawa marok'a kudi ba, Kuma Dan gayu ne sosai Naga Uncle Abdul Hakeem ma ya
rugume shi Yana ta dariya, Dana tambayi Auncle Imam yace min sunansa uncle Mahmud".
Tunda ya shigo Yana karadin Nan ta zuba masa Ido tana sauraren abinda yake fad'a,
kana ganinsa kasan har zuciyarsa abinda yake fad'a din gaskiya ne, wani irin
gingirin taji kanta yayi mata, nan ta sulale ta kwanta kan kujerar ta saka hannunta
ta rufe fuskarta wasu hawaye na zubo Mata masu zafi.
Sajida da Amatu suka nufi gurin Faruq din suna neman Karin bayani.
Yayin da wasu da yawa suke ta sabgar ciye ciyensu Dan Suma Kam an kawo koma enough.
Kamar yanda ya fad'a haka Suma ya mayar musu Dan su harda Karin bayanin yayi musu
kasancewarsa Mai surutun tsiya.
A hankali Sajida ta kamo hannun Zahra Dan Bata fatan wani daga cikin bakinsu su
fuskanci an samu matsala gaskiya, kamar masu you shawara suka shiga dakin Auntyn
saboda Nan ne baza'a shigo ba.
Bakin gadon ta zaunar da Zahra ita Kuma ta janyo stool ta zauna har lokacin Bata
saki hannunta ba,tana Jin yanda ilahirin jikinta yake rawa.
Hannun ta Kara jimkewa cikin nata tana fadar.
"Cool down Mana bestie haba take it easy, kada ki tada hankalinki Taya Zaki kama
maganar faruq kinsan dai ba wani hankali ya Gama Masa jiki ba".
Kai ta shiga girgizawa cikin muryar Kuka tace.
"Wallahi Saji akwai matsala kema Kuma kin sani sai dai kik'i fad'a idan ba matsala
Ina su Maryam da mukayi dasu zasu zo tun kwana ukunda suka wuce Ina shi kanshi uban
gayyar ina su Deeni dasu Aliyu, kowa ka Kira sai dai kaji switch off baka haka ba".
Ta fad'a tana fashewa da wani irin Kika.mai taba zuciya.
"Kiyi shiru Dan Allah kada ki janyo hankalin mutane Mana kinga ga Amatu can zataji
dasu ki nutsu har muji meye gaskiyar maganar Mana".
"Ki barni nayi kuka wallahi na gaji nikenan kullum matsala daga wannan sai waccan
na rasa a Ina matsalar take ni wallahi bana son kowa ma a kyakeni haka Nan bana son
auren, bana so wallahi ni nagaji Allah Jordan zan tafi bazan zauna ba, bazan Kara
Zama a kasar nan ba".
Ta fusge hannunta daga na Sajida ta yunkura ta tashi ita dai Sajida Bata San ta
Yaya akayi ba sai ganin Zahra tayi ta kifa kan gadon tana wata irin fuzga da gudu
ta karasa kusa da ita tana jijjigata tana fashewa da kuka tana fadin "ki tashi Dan
Allah wayyo Allah na".
Baba Tabawa ce ta bude kofar ta shigo, Dan tunda tana kusa dasu Faruq ya shigo da
wannan maganar duk da tasani Dan Aunty Hasana Bata rufe Mata komai ba ta fad'a Mata
tun jiya, shi yasa data ga sun nufo dakin hankalinta ya kasa kwanciya ta biyo su
tasan koya Sajida zatayi Mata kalamai ba kamar ita ba tunda abinda babba ya hango
yaro koya hau iccen rimi bazai gano ba.
Turus tayi tana kallon Sajida dake Kuka bil hakki tan jijjiga Zahrar.
Da sauri ta karaso tana fadar "ke 'yan Nan menene haka?".
Hawaye jage-jage Sajida ta dago tana fadar "wlh Baba Tabawa kawai tana kuka tana
maganganu tana tashi kawai sai Naga ta yanke jiki ta Fadi?.
Wani ruwa Baba Tabawar ta dauko a kan bedside fregde din Nan ta zubawa Zahrar a
fuska Amma shiru ta Kara watsa Mata Nan ma shiru cikin tashin hankali ta lalubo Yar
wayarta rakani toilet ta mikawa Sajida "ungo maza Kira min Aunty zakiga an saka
Maman Ali yi sauri".
Bugu biyu Auntyn ta dauka tare da sallama, gani Sajida ta rasa me zatace ne yasa ta
mikawa Baba Tabawa wayar.
Can Kuma tana ta faman" hello Baba"
Abinda taji kenan lokacin data Kara wayar a kunne cikin sauri Baba tace "yi sauri
ki turo a Kai Zahara'u asibiti wallahi gata Nan a suma min yayyafa ruwa a banza".
Bata jira taji me za'a fad'a ba ta kashe wayar.

Abdul Hakeem Aunty Hasana ta lalubo a waya lokacin suna tsaye shi da Mahmud suna
magana wayar Abdul Hakeem dince ta Fara ringing Sunan Aunty Hasana ya gani ya daga
har zai Fara Mata abunda ya saba ta tsayar dashi tana fadin "Dan Allah maza kaje
gidana ka dauko Zahra ku wuce asibiti mu hadu a can wai Suma tayi"
Kit ta kashe wayar.
"Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un yake ta Nanatawa da sauri Mahmud ya tambaye
shi "lafiya meya faru".
"Bari kawai ba komai Ina zuwa yayi gaba da sauri jikinsa har rawa yake Yana tafe
Yana laluben key din motarsa. Da sauri Mahmud ya biyo bayansa' Sam baiji key din ba
sai daga baya ya tuna tana hannun mustapha yaje gari ya dawo.
Tsaki yayi daidai lokaci da Mahmud din ya karaso Yana fadar"Dan Allah Wai menene
Naga duk a rude".
"Bari kawai Wai Zahra ce ba lfy zan kaita ASIBITI".
Kallon yayiwa Abdul Hakeem din kafin yace "shine Kuma zakaqi fad'a min".
Hannu yasa ya yafito Sameer, cikin bada umarni yace
"Dauko motar can kuje da Abdul zaku Kai madam asibiti". Ya juya ya koma gurin su
Habib.
Har sukaje gidan Auntyn Abdul Hakeem Bai daina mamakin Mahmud ba, yanayin yanda
yayi maganar kawai kasan da abinda ya taka umarni fa ya bada, su dai a zahiri ai
Sameer ne uban gidan Mahmud tunda kowa yasan aikin NGO's ya kawo shi garin har suka
hadu da Mahmud din suka dauke shi yake musu aiki a sauran makarantun tsangayun na
cikin gari Dana kauye.
Da sauri Abdul Hakeem din shiga gidan Auntyn ta kofar baya gurin kitchen ya shiga
koridon dakunan barcinta.
A tsaye cirko cirko ya samu su Baba Tabawar har lokacin numfashinta Bai dawo ba.
Da sauri ya karasa gaban gadon yasa hannu ya dauketa kamar wata Baby yayi waje da
ita. Sajida da Baba Suka rufa Masa baya.
Da sauri Sameer ya bude Masa seat din baya ya sakata Sajida ta shiga ita da Baba
shima Abdul Hakeem ya shiga gaba da gudu Sameer ya fizgi motar. Saida ya daidaita a
titin sannan ya kalli Abdul Hakeem din "ina muka nufa?".
"F.M.C zamuje tunda yafi kusa".

Nan da Nan aba karbeta likitoci suka rufu a kanta, suna Nan tsaye Aunty Hasana tazo
ita da Inna maimuna sai Hajiya kaltume.
Suma tsayawa sukayi a gurin Baba Tabawa tana maida musu yanda akayi ita dai Sajida
ba baka sai sharar hawaye take.

Su Abdul Hakeem suna suna gefe daga zuwansu Mahmud ya Kira akai sau biyar idan ya
Kira Sameer sai ya Kira Abdul Hakeem, daga Jon yanayinsa kasan Yana cikin damuwa
abinda ya Kara daure Abdul Hakeem Kai yandq Sameer yake amsa wayar Mahmud cikin
kulawa da bada girma.
Sun dauki a kalla minti arba'in kafin babban likitan ya fito sannan sauran Suma
suka fito.
Su Abdul Hakeem sun bin bayan likitan kamar yanda ya bukata Amma ganin an gungoro
Zahrar a gadon daukar marasa lafiya yasa suka nufe ta da sauri suda su Aunty
Hasana.
Wanda ya turo gadon ne yace "ai ta farfado ba wata matsala ana so ne dai ta samu
hutu sosai jininta ne yaso Hawa Amma cikin ikon Allah anyi controlling dinsa".
"Oh no 'yasu Allah ka dubi lamarin wannan 'yar maraiya duk da Bata tashi da rashin
gata ba sai yanzu ka kawo Mata Tata jarabawar Allah ka shiga cikin lamarinta".
Aunty Hasana ta fad'a itama tana goge hawaye.
Baba Tabawa dasu Sajida suka amsa da "ameen ya Rabbi"
Dakin 'yan da'i da'a aka kaita tunda tana bukatar isolation.
Saida komai ya Zama dai dai an saka Mata drip sannansu Sameer sukaje gurin likitan.
Fad'a yayi so sai akan yanda akayi har karamar yarinya kamar wannan damuwa tayi
Mata yawa har har take barazana ga lafiyar ta.

A can gidan biki Kuma Amma ta rasa inda su Hasana da Inna suka tafi Dan hankalinta
Bai kawo Mata Hajiya kaltume ma Bata Nan ba sai da abokiyar zamanta tazo sannna ta
fuskanci itama Bata Nan din wayarta ta dauko ta Kira Hasana, lokacin tana zaune
gaban gadon da aka kwantar da Zahrar.
Sunan Ammah ta gani sai lokacin ta tuna Ashe Bata fad'a Mata ba.
" Assalamu Alaikum Ammah".
"Wa'alaiki Salam warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu, wai Ina Kika tafi ne babu ke
Inna maimuna ma Bata Nan Hajiya kaltume ma banganta ba".

Dan Jim tayi har Saida Ammah tace "kina jina?"


"Eh inaji Ammah duk muna tare dasu, muna Nan gurin Zahra Bata Jin dadi ne Amman da
sauki yan haka barci take".
"Wane irin zance ne wannan kamar Bata Jin dadi Kinga Hasana fadi min gaskiya yanzu
kina Ina?".
" Muna F.M.C wlh jikin da sauki sosai kawai sunce ana dai San ta huta ne, kada ki
tada hankalin Dan Allah".
"To Allah ya kyau Amma Ina hankali ze kwanta".
Waje Aunty Hasanar ta fito gurin su Baba tabawa da sajida tace
"Baba tabawa Dan Allah kuje gida da sajida tasan inda aka aje abubuwan da zasu bawa
kawayensu tunda yau zasu wuce sai ki fad'a musu tana gida gurin Abba, ta kalli
Sajida ke Kuma duk tmbayar da saying Miki kice Baki Sani ba mu barsu a haka".
Kudi ta mikawa Baba tabawan sannan ta karasa gurinsu Inna maimuna da Hajiya
kaltume, Suma bayi tayi musu na Kiran Ammah tace suje gidan Dan hankalinta ya
kwanta.

*********
Da kyar Amma ta Bari akayi sallar magariba ta shiga bangaren Alhaji Jafar ta same
shi da Hassan da Abdul Hakeem suna magana akan Zahra Hassan Yana ta mitar meyasa
Abban yayi haka ai da hakuri kawai akayi har lokacin da Allah ze kawo Mata wani.
Dan murmushinsu na manya yayi Yana "fadin wannan ma in Sha Allah Babu Dana Sani a
cikinsa ni nasan nagartar Dana gani tare da yaron yasa na bashi, Kuma ko bayan
Raina zakuce na fad'a muku".
Jiki ba kwari Amma ta gaishe da Alhajin tana Masa ban gajiya tare da godiya.
Sannan ta Dora da fadin "Dan Allah ko zaka Bari naje Naga jikin nata?"
Tsai yayi Yana kallon ta "da kinyi hakurin zuwa Suma da anjima zasu taho gida yanzu
ma daga cen muke ko zuwan mu Bai isar ba?"
Cikin Jin nauyinsa tace "A'a ya badatar"
Ta tashi ta nufi kofa da kallo Abban ya bita ita kanta tausayi take sashi da gani
zuciyar ta ba Dadi.
Da sallama suka shiga dakin lokacin Aunty Hasana tana sallar insha'i ita Kuma zahra
farkawarta kenan tana kokarin tantance Wai inane ma Nan din inda ta gani idan dai
ba gizo idanunta ke Mata ba kamar asibiti.
Sallamar ce ta katse Mata tunani ta Dan dago kanta kadan sukayi arba dashi Ido
cikin Ido da sauri ta runtse idanunta zuciyar ta na wata irin bugawa tana ambaton
Allah a zuciyar ta, meya kawo wannan dodon nata gurinta, Kara rufe idanun tayi it
fa wallahi zata iya rantsewa Allah duk duniya ba idanun da suke figitata kamar
nasa.

❤️ AUREN HUCE HAUSHI ❤️

Strory
&
Written
By
MAMAN FATIMAH

Page five

_______ Shiru dakin ya dauka har zawan lokacin da Aunty Hasana ta idar da
sallar.
Dan juyowa tayi kadan tana fadin "wa'alaikumus Salam warahamatullahi ta'ala
wabarakatuhu, sannunku da zuwa Bismillah ga kujeru nan ku zauna".
"To mun gode Aunty" Sameer ya fada.
Cikin ladabi da mutuntawa suka gaishe ta tare da tambayar Mai jikin, ta amsa
musu da sauki, sai kuma dakin ya Kara daukar shuru Zahra dai tunda ta rufe ido Bata
Kara gigin budewa ba, ita ji take duk ya cika dakin ita tun ganinta na farko dashi
a duniya ya birkita Mata lissafi, Kuma saboda Allah meya kawo shi gurinta asibiti
duk da tasan mutumin Ya Abdul Hakeem ne Amma sai taga kamar ba sai yayi Masa Kara
ba, ko Kuma yazo wata sagbar ne asibitni ya Sami labarin shine ya shigo ya dubata.
Magaji ne ya shigo dakin da sallama sai Kuma ya Dan tsaya baiyi tunanin ganinsa ba
Sam da fara'a ya karaso Yana fadin "Ashe Kuna Nan ai tare muke da Ya Abdul Hakeem
ma".
"Ok" abinda Mahmud ya fad'a kenan
Shi Kuma Magajin ya karasa gurin Auntyn Yana gaishe ta.
Abdul Hakeem ne ya shigo Yana rike da wayarsa a hannu da sauri ya karasa gurinsu
Mahmud din Yana fadin "A'a angon ne da kansa" Yana Mika masa hannu.
Saroro Aunty Hasana tayi ita wace iri ce kawai dai taga sun shigo sun gaisa wallahi
Sam Bata kawo ba ita da akace Mata Alamajirin Baba malam ne ai ta dauka irin wannan
gaddawan ne, yo ta Ina wadannan sukayi wani Kama da kolaye ai ita zallar ilimi ta
gano da wayewa a tattare dasu.
Hanyar wajen ta nufa tana janye da hannun magaji duk sai taji kunya ta kamata Ashe
sukanta ne.
Ita kuwa Mai gayya Mai aikin ai tana jin an ambaci ango ta bude idonta girjinta
Yana wata irin dokawa "ango a nan to waye a tsakaninsu da suka shigo tare?
Abdul Hakeem ne ya kalli gurin gadon Yana fadi.
"Masha Allah! Ashe kin tashi, ya jikin?"
Ya fad'a Yana karasawa jikin garon Sameer ma Dan matsawa yayi Yana dubata Kai kawai
ta gyada musu, tana kallon Ya Abdul Hakeem din, kallo irin na neman Karin bayani.
Yi yayi kamar Bai Gane ba ya juya yana yiwa Sameer magana suka fita.
Har suka fice Bai dago ba Yana ta faman tab'a waya sai da ya Mula Dan kan shi
sannan ya tashi ya tunkari gadon.
"Ya jikin?"
Ya fad'a Kai tsaye, Bai Kuma jira ta amsa ba Dan ko kwakwkwaran motsi ta kasa sai
tunanin da yake Mata Kai komo.
"Badai wannan bane ake nufin an daura min auren dashi Amman da Naga ta kaina".
Shine ya katse tunaninta.
"Ki kwantar da hankalinki ki daina saka damuwa a ranki da kannan shekarunki, ki
kuma dagawa Ammah í nata hankalin, idan nine bakya so ba damuwa Nima kusan hakan
take. Amma kada mu watsawa iyayen mu kasa a ido Mana tun yanzu gara ki nutsu ki
kwantar da hankalinki daga baya sai a duba Mai yuwuwa tunda nasan bazaki so Zama
da almajiri marar karatun boko mai zurfi, ga karqncin wayewa ga rashin madafa ta
yau da kullum, Nima kasada ce tasa na yarda da tayin da akayi min tunda Naga nema
ake a tozarta min da iyayen a kunyata su a idon duniya aci mutuncin su".
Ita da'i ko motsin kirki ta kasa da gaske gani take duk ya cika dakin, ga wani
fitinan kamshinsa duk ya cika Mata hanci.

A bazato taji ya Dan shafi gefen fuskarta idan ba kunnenta ne suka jiyo Mata ba
da'i dai ba sai taji kamar yace "my previous" a hankali sannan ya Mike Yana fadin
"Bari a kawo maganin ki saimu wuce gida tunda doctor yace zamu iya wucewa, Amman
yace ki rage yawan tunani Yana haddasa cututtuka".
Har dakin Amma Abdul Hakeem ya raka Zahra lokacin duk yawancin bakin sun tafi sai
'yan uwan Amma na Mubi Dana Jimeta sai Kuma Aunty Hasana da take dakon dawowar su,
ai tunda magaji ya Kara Kora Mata bayani akan Mahmud ta tafi daga asibitin tunda
Mai dungurungum din yazo ita bataga ta Zama ba.
Saida ta matsawa Zahrar tayi wanka Tasha tea da magungunan ta kwanta sannan tayi
haramar wucewa gida.

Sai wurin karfe Tara sannan Hajiya mama ta shigo dakin tana fadin "wallahi daga
idar da sallar ta barci ya dakeni sai Dana tashi zilai Mai wanke wanke take fad'a
min an dawo da Zahra har sun shigo sun duba ta".
"Wallahi kuwa ai jiki da sauki yanzu Tasha magani ta kwanta"
"To Allah ya Kara lfy, Wai Hajiya wanene mijin yarinyar Nan ne naji ana fadar Wai
cikin Almajiran baba Malam ne, shine nace haba yaushe Alhaji zeyi wannan danyen
aikin ya rasa bazai bawa aure Sai a cikin Almajirai".
Inna maimuna ce tace "ai mu Hajiya ko waye Alhaji Jafar ya aurawa Fatima wallahi
mun karba da hannu biyu mun gode tunda mun San har abada Babu cutarwa a tsakanin
Asama'u da dashi da ita Fatiman da abinda ya Haifa bamu taba ganin banbanci ba, Dan
haka mun karba da kyakykyawan niyyarsa Allah ta tabbatar Mana da Alkhairi".
Gaba daya suka amas "Amin"
Hajiya mamar ta Dan jima a dakin kafin ta koma dakinta.
Bayan Zahra tayi sallar Asuba ta gama Azkar dinta komawa tayi ta kwanta har lokacin
kanta Yana Mata ciwo kadan kadan, sai gurin takwas da rabi Inna maimuna ta tasheta
tana fad'a Mata tayi maza ta kimtsa Abbansu Yana nemanta.
A gurguje tayi wankan ta fito lokacin an kawo Mata kunun gyada da fanke, kunun
gyadar kawai tadan Sha kadan ta shafa lotion dinta ta saka doguwar rigar atamfa ko
dankwalin Bata daura ba ta fito cikin takunta na nutsuwa Wanda da yawa mutane ke
gani a matsayin yanga da jiji da Kai.
A tsakar gidan suka rinka gaisawa da tsirarun yan uwansu na Mubi da sauran
ma'aikatan gidan Mata.
Da sallama a bakinta ta shiga falon Abban nasu, tayi mamakin ganin kusan duk
'ya'yan Abban suna Nan sai su Ammah da Inna maimuna da kanwar Abban Maman lafia.

"Zo nan kusa dani Uwata".


Abban ya fad'a Yana murmushi, itama murmushin tayi ta karasa kusa dashi ta zauna
nata fadar "Abbana Ina kwana?".
"Lafiya kalau Alhamdulillahi Uwata".
Sannan ta juya tana gaishe da jama'ar gurin.
Said Kuma dakin yayi shiru.
Abban ne yacewa Imam "Mai sunan Malam ayi Mana addu'a".
Ya jima Yana addu'a sanan aka shafa. Sannan Abban ya Dora da cewa.
"Alhamdulillahi ala kulli halin, dole ne mu godewa Allah s.w.a a cikin kowane Hali
mutum ya Samu kansa, kowa yasan yanda lamarin Auren Uwata ya ringa kasancewa a baya
abune ba Mai dadin maimaitawa ba, to wannan karon ma tarihine yaso maimaita kansa
Amma na yanzu sai yafi sauran tada hankali ni Kuma Naga a wannan gab'ar bazan Kara
bada wata kafa ba wadda za'a dunga walagigi da rayuwar yarinya karama ba kamar
Uwata. Sunanta Ya kira Fatima dago ki kalleni, cikin girmamawa ta dago kanta kamar
yanda yayi Mata umarni. Hannunsa yasa ya nuna kansa yace kina ganin zan iya
zaluntar k?" Da sauri ta girgiza Kai hawaye na zubo mata.
Yace "To Fatima na daura Miki aure da bakon yaron Nan Mahmud na wajen Aminina Malam
Bukar". Duk da taji haka daga bakinsa a jiya Amma Bai hanata kara shiga rudu ba
saboda wannan taji daga bakin da bazeyi Mata karya ba, Nan da Nan ialahirin jikinta
ya shiga rawa wallahi ita a jiyan jinsa kawai take gani take kamar almara ce kawai.
Muryar Abbansu ce ta Kara katse Mata tunani "kiyi hakuri Uwata kowa da irin
jarabawar da ubangji yake Masa ki dauka taki jarabawar kenan, ki yadda da
kaddararki sai Ubangiji ya jibinci lamarinki wannan ba hadin kowa bane hadin Allah
ne, kiyiwan mininmi biyayya in Sha Allah zakici ribar rayuwa, ki cire yaron Nan
Musbahu daga zuciyarki ki rungumi abinda Allah ya baki. Allah yayi Miki albarka
yanda Kika yi min biyayya Allah ya Baki 'ya'ya Wanda zasuyi Miki biyayya kema,
Allah ya albarkaci aurenku ya tsone idon makiya da mahassada".

Hajiya mama ce ta fasa Kuka tana fadin "Haba Alhaji wannan wane irin danyan hukunci
ne? ya zaka dauki 'yar marainyar Allah ka baiwa Wanda ba'asan asalinsa ba, ai
duniya saita zage ka Dan Allah ka janye maganar Nan da wannan ba gara kaba salmaun
gidan Hajiya Dago ba tunda ya jima Yana son yarinyar Nan Amma ka Hana shi"
Kowa a falon kallonta yake ba Wanda ya tofa sai danta Hamza yace "haba mama menene
haka kikeyi Dan Allah kiyi shiru da wannan maganar salmanun me Allah ya sauwake me
za'a da wannan zuri'ar".
Hannu Abban ya dagawa Hamza Yana fadin "ya Isa haka tunda ka Bata amsa basai
nace komai ba, Amman ki rubuta ki aje in Sha Allah sai wannan auren ya Zama abin
kwatance Kuma abin alfahari duk Wanda ze zageni ya Dade Bai zageni ba, Kuma duk Mai
ganin zalunci ne yasa na aurawa Fatima Mahmud na barshi da Allah wallahil Azeem ban
taba kallon Uwata a matsayin 'yar wani ba kullum Ina Mata kallon 'yata malak malak
a makaranta ne kawai ban saka Mata sunana ba shima nayi haka ne Dan tasan nata
mahaifin ta rinka Yi musu addu'a".
Addu'a Abban yasa Imama yayi yaba kowa izinin tafiya Amma yace Ammah ta tsaya ita
da Hajiya mamar da Inna maimuna da Maman lafia.

Aunty Hasana ce ta kamo hannun Zahra zuwa dakin Ammah tana kuka, yarinyar tausayi
take Bata kamar yanda Abban ya fad'a ana walagigi da rayuwar ta.
Cikin bed room din Ammah suka wuce, bayan sun zauna ne Auntyn ta riko hannun Zahrar
"kiyi hakuri kinji Allah Yana sane da halin da kike ciki, Dan Allah kad'a ki
watsawa Abba kasa a Ido ki bijirewa auren nan wallahi irin wanna auren Yana albarka
fiye da tunanin".
Wasu sabbin hawayen ta goge. Cikin shashhshekar kuka tace "wallahi Aunty nifa
tsironsa nakeji idan muka hada Ido wani Abu nake gani a idonsa".
Sororo Auntyn tayi kafin tace "ban Gane ba tsoronss kamar Yaya, Daman kinsansa ne
runtuni?.
Kai ta gyada Mata alamar Eh.
"Allah ya kyauta" kawai Auntyn tace.
"Ko meme ma dai wannan tsakaninku ne kin gyarota can".
Ta Mike tana fadin "Bari na koma gida sai zuwa an jima zamu shigo da Sajida da
Amatu itama Bata tafi ba jiyan.

********Tun bayan suka dawo daga sallar Asuba Mahmud yake ta faman aiki a cikin
laptop dinsa, Yana kallon Sameer Yana kwasar barcin gajiya. Bai gama aikin ba sai
kusan karfe takwas na safe, kai tsaye toilet ya nufa ya jima a ciki kafin ya fito
daure da towel a kugunsa karami Kuma a hannunsa ya goge sumar kansa me baka sidik
Mai laushi Saida ya shirts cikin wani farin yadi filtex marara nauyi ya feda
turarensa Alburaq sannan yaje gefen bedside ya dauki wayarsa ya kunna.
Abinci ya bukata a kawo musu, yana Gama wayar Kira ya shigo sunan Habib ya gani, ya
daga da sallama daga cen Habib Fara fadar.
"Habe Dan Allah dukka tadawa Baba malam hankali baka kwana a gida ba abinda baka
Saba ba Koda wasa duk dare zaka dawo Amma jiya daga Bari kaje ka dawo shi kenan
kayi layar zana Kuma ka Kama ka kulle waya".
Dariya yayi Yana cewa "kana tunanin Kona bi dare nayi Gudun auren dole ko?"
Shima Habib din dariyar yayi.
"Ka Gudun Mana idan ka Isa mai wannan tsaleliyar Ina zaya ya barta koka gudu ka
dawo da kafarka, kawai da malam ne ya matsa yaji kana ina".
"Ok shi kenan Bari na kira shi Dan hankalinsa ya kwanta Ina Nan tare da Oga Sameer
shine ya rikeni nayi Masa wani aiki".
Yana kashe wayar ya nufi sofa ya zauna yana janyo stool din da aka Dora abincin.
"Oh ni Sameer yaushe na rikeka? ka rikeni dai ka Hanani tafiya ka barni da kame
kame ga madam can tana fama da kanta ba mataimaki gaskiya yau in Sha Allah sai
kano".
Ya fad'a yana nufar toilet shima.
Can hayin bankin suka Fara zuwa gurin masu aikin gidan Masha Allah aikin yayi nisa
kamar ba jiya aka Fara ba Sam an canzawa gidan fasali kamar bashi ba, duk abinda
ake bukata Sameer ya danka shi a hannun Binya.
Sannan suka nufi cikin gari.
Wani mall suka shiga Mahmud ya jido kayan fruits dasu kayan tea sai chocolates
dasu farm fresh yogurt da fresh milk. Leda uku aka cika manya Saida suka dauki
hanya Sameer ya kalli Mahmud yana fadin "wadannan kayan fa yallabai na waye".
"Dubiya zamu saika Bata tunda ni dai kowa yasan bani da kudin sayansu.

❤️ AUREN HUCE HAUSHI ❤️

🔷 Page six🔷

________Sun jima a gurin Baba Malam Yana yiwa Sameer godiyar dawainiyar da yasha
akan wannan lamarin, sannan yayiwa Baba Malam din sallama akan zai wuce sai hutu ya
Kare zasuzo da mutanen su suna son su kawo wasu ayyukan da za'ayi.
Har gurin mota Malam dasu Habib sukayi Masa rakiya, Baba malam Yana fadin "Bari
muyi addu'a".
Nan yaja doguwar addu'a akan Allah ya tsare hanya, har Sameer ya shiga mota ya fito
ya nufi Malam Wanda har ya Fara tafiya, sai Kuma yaja ya tsaya Yana jiran karasowar
Sameer din.
Dan risinawa yayi Yana fadin "ko za'a samu Wanda ze rakani na Kara dubo jikin
wannan yarinyar?"
Wani kallon kasan ido Mahmud ya bashi dashi "Wai yarinya".
"To! To! Masha Allah ai sai kuje da Mahmud din da Habibu kuga jikin, ai wannan
tunani ne Mai kyau.Nima na shiga da safe gurin Alhajin naji yata kwana".
Har cikin harabar gidan Sameer ya shiga da motar, Abdul Hakeem Habib ya Kira kafin
su shigo ma ya fito Nan Harabar gidan Yana jiransu.
Shi yayi musu jagora zuwa falon Abban, yayi murna sosai da ganinsu sun gaisa sosai
sun masa godiya sosai da karamcin da yayi musu, yaji dadi sosai Dan har ya ringa
tsokanar Sameer Yana fadar "wato tunda kazo gabatar da aikinku ban sake ganin
kafarka ba a gidan Nan sai yau dana baku Mata ko? Dan na lura baka da aminin daya
wuce Mahmud a garin nan. Masha Allah, Malam ya fada min duk Fadi tashin ku akan
lamarin Allah ya saka da Alkhairi yabar zumunci".
Suka Amma da "Amin ya Rabbi".
Mahmud Alhajin ya kalla Yana fadin "kayi hakuri fa Mahmud munyi maka nauyin kuka".
Kai ya gairgiza Yana fadin "ko daya wallahi ba komai nagode, Allah ya saka da
Alkhairi ya Kara lafiya Nisan kwana Mai albarka"
"Allahumma Amin. Allah yayi Albarka, ya baku zaman lafiya ya baku zuru'a Mai
Albarka, sai ayi ta hakuri da lamarin Mata fa. Abdul Hakeem ku shiga ciki su gaisa
da Iyayen nasu".

Wannan shine shigar Mahmud na biyu gidan, na farko lokacin da magaji yayi accident
da mashin suka shigo shida Abdul Hakeem da Hamza ya duba shi a dakin Ammah, dan ma
lokacin ba kowa a gidan sunje gaisuwar mutuwa.
Directly dakin Hajiya Mama Abdul ya nufa dasu, Zilai Mai musu wanke wanke ce tayi
zuruf ta shiga dakin Ammah.
Tana fadin "Ammah Ina Jin fa ga mijin Zahara'u Nan sun shiga dakin Mama shida Abdul
Hakeem da wasu inaga abokansa ne".
Ta juya ta fita.
Gyalen Inna maimuna Ammar ta dauka dake kusa da ita ta yafa a jikinta.
Da sallama Abdul Hakeem din ya shigo Yana fadin Bismillah ku shigo Mana, a nan kan
carpet a kasa suka zauna suna gaishe dasu Ammar tare da tambayar Mai jikin.
Abdul Hakeem ne yace " Inna mijin Zahra ne da ubangidansa suka shigo duba ta shi
yau ze wuce shine yace a rako shi ya Kara dubata da jikin nata".

"Kai Masha Allah an gode madallah Allah ya saka da Alkhairi ya maida ka gida
lafiya". Inna maimuna ta fada sannan ta kara da cewa "to waye angon nawa Dan nice
ta karfe ita wannan Farafarar ba wani abun azo a gani zata iya ba ni kuwa ko banza
na tuka maka tuwon dawa da man shanu ko ba haka ba?" Ta tambaye shi tana kallonsu.
Duk dariya sukayi Amma shi gogan Dan murmushi yayi kadan Yana basarwa.
Abdul Hakeem ne ya nuna Mahmud Yana cewa.
"Ga angon naki nan nagama kamar kunyarki yakeji"
"A'a! Masha Allah tubarakallah Mai gidan nawa wanke hannu daka taba ne, kaga dago
ka kalleni ni Kaka ce kada kaji wata kunya ta".
Kara sadda Kai yayi shifa duk jinsa yake wani iri Wai shine a zaune a dakin surukai
Ashe da gaske ana jin kunyar shi wallahi da ji yake kawai fada ake ba wani nauyin
da akeji Saida ya same shi yanzu yake gaskata hakan.
A kaikaice Ammah ta kalleshi "Masha Allah" ta fada a zuciyar ta, ita bataga wata
makusa ba a tare dashi Kuma idan ba idon tane yake Mata gizo ba sai taga duk cikin
Wanda zasu auri Zahrar a baya bataga Mai nagarat wannan yaron ba.
Albarka da nasiha dai ya Sha ta gurin Inna maimuna.
A haka suka fito daga dakin har suka fito compound din Abdul Hakeem Bai fito ba sai
duba agogo Sameer keyi Yana mita.
"Nifa bana son nayi Rana a tafiyar Nan gaskiya, Naga alamar kuma neman kuke kusa
nayi yamma ma".
Kafin Mahmud ya bashi amsa Abdul Hakeem din ya fito da sauri da key a hannunsa Yana
fadin "kuyi hakuri key din ne ba'a gani ba da wuri ku karaso ciki kafin Zahrar ta
fito ku gaisa".
Mahmud ne yace "Kai haba da an kyaketa ta huta ita da Bata da lafiyar kirki".
Karamin falo ne da kujeru masu kyau sosai da kayan kallon alama an tana deshi ne
saboda Yara Mata na gidan da Kuma dai dai kun Baki.
Bayan fitar Abdul Hakeem, Sameer ya kalli Mahmud.
"Dan Allah my man yaushe idonka ya koyi kunya? Naga sai wani sadda Kai kake, nifa
lamarinka ya Fara bani tsoro na rasa wace alkibla ka kalla kazo garin mutane ka
Mike kafa kana wata irin rayuwa a takure nace zan dauki mataki ka aje min sharadi,
da kasan bazan it's tsallakewa ba, yanzu Kuma Rana tsaka a tarko aure Kai kadai
kamar marar gata sai walagigi kake alhalin kana da madafa".
Tsaki yayi " kana da matsala wallahi ko me zance fada maka bazaka Gane ba, amma
idan lokaci yayi zaka fashinmta,yanzu duk bayanin da zanyi maka ba fashinmta zakayi
ba, kawai mu bar maganar kawaai"
Kanshin turaren ne ya alamta musu zuwanta. sallama tayi cikin siririyar muryarta.
Sameer ne ya amsa Mata sallamar a zahiri Dan shi Dan gogan a saman lebensa ta amsa
sallamar. Sameer din ne ya Dan Mike Yana fadar.
"Masha Allah jiki yayi sauki kam, "Bismillah". Yana nuna Mata kujerar gefen Mahmud.
Kai ta dangirgiza Masa tana dan murmushi kasa kasa.
A Nan kan carpet ta zauna daga gefe tana gaishe da su a jimlace.
"Lafiya kalau"
Sameer ya amsa Yana fadin "ya jikin naki?"
"Alhamdulillahi" ta amsa masa.
Sai Kuma duk sukayi shiru, ganin lokaci Yana qurewa Sameer ya Mike tare da kallon
Zahra Yana fadin " To madam bako zeyi halinsa Allah ya bada zaman lafiya. Amma fa
sai kina hakuri da halinsa gaskiya ba kirki ya cika ba Ina son idan na dawo Naga
canji na zahiri a tare dashi, sunan Sameer Sa'ad koko, zeyi miki cikakken bayanin
koni waye a gurinsa Allah ya bada zaman lafiya da zuri'a mai..albarka Allah yasa
next year by now muna bkin suna"
Da sauri Mahmud ya kalli Sameer a zuciyarsa Yana fadin "Allah ya shiryeka Sam baka
girma".

A hankali tace " Mun gode kwarai Allah ya tsare ya kiyaye hanya".
"Amin" ya amsa Yana kallon Mahmud.
"Ni zan wuce saina sake shigowa ayi kokarin ganin aikin Nan ya kammalu".
Ya fada Yana nufar kofar fita.
Sai lokacin Mahmud din yayi magana "pls ka jirani minti biyar Dan Allah".

"Idan ya wuce haka Kam...."


Ya fice ba tare daya karasa fada ba.

Tunda Sameer din ya fita take wasa da karamin zoben da yake hannunta. Bata dagon
kalle shi ba shi Kuma Bai tofa tasa ba amman idonsa Yana kanta, Kare Mata kallo
yake Yana fadar "Masha Allah tabarakakkahu ahasanil kaliqin".
Tsam ya taso daga inda yake ya sauko kasa inda take zaune.
"Ya jikin naki?".
Ta tsinkayi maganarsa kusa da ita daf Sam bataga lokacin daya taso ba.
Cikin daburcewa saboda kusancin nasu yayi matukar yawa ji tayi kamar ma iskar gurin
ta tsaya sai munfashinsa take shaqa kawai.
A mamakance taga yasa hannunsa ya dago fuskarta suka hada Ido hudu dashi. Da
sauri ta runtse idanunta zuciyarta na wata irin bugawa.
"Bude idon Kona Baki mamaki".
Marmar ta Fara da idon tana budewa a hankali Amma taki kallon nasa idon.
"Ya jikin?".
Ya Kara maiamaitawa, a hankali ta bude bakinta tace "da sauki"
Gamshin Lister mint ne ya daki fuskarsa. Banda Yana daf da ita ba yanda za'ayi yaji
abinda ta fada.
"Allah ya Kara lafiya".
"Ameen"
Ta fada.
Hannunsa ya cire daga fuskarta yana Dan furzar da iska daga bikinsa ya Mike tsaye,
a hankali ta sauke wani numfashi.
A bazata taji yace "bani wayarki"
Ba musu ta Mika masa, aljihu taga ya saka Yana fadin "ki shiga gida ki kwanta kiyi
barci sosai kada ki yawaita hayaniya ki samu hutu sosai, zan tambayi magaji idan
bakya hutawa yanda ya kamata ni Ina da inda zan kaiki ki samu isolation, tashi muje
ki shiga gida ana jirana".
Saida ta shige ciki kafin ya juya ya nufi gurin da Sameer da Abdul Hakeem suke suna
Hira.

Lokacin data shiga dakin ta Samu Aunty Hasana dasu sajida sunzo har da yaran duka.
Da guda ta karasa cikin suka rungume juna da Sajida Nan da Nan sai hawaye itama
sajidar kukan ta fara.
Ammah ce tace "Naga abinda ya isheni meye haka zaku tasa mutane a gaba Kuna kuka,
to kukan maganin me ze muku aikin Gama ai ya Riga ya Gama Saida hakuri da addu'a
kawai".
Uwar dakin Ammah suka shige.
Magaji ne yayi sallama ya shigo da manyan ledoji guda biyu niqi-niqi da kaya Auntyn
Hasan na tambayar"daga Ina?"
Ya fice da sauran Yana fadin "ina zuwa Aunty"
Wata ledar ya shigo da ita Yana fadar"kayan dubiya ne aka kawo Mata" ledar daya
kawo daga karshen ya bude rafar 'yan dari bibiyu hura biyu ya dauko daga saman
kayan, Aunty Hasana ya
Mikawa yana fadar "gashi nan inji abokin mijinta Wanda suka shigo dashi dazu".
Godiya su Inna maimuna sukayi tayi kamar Yana nan a gurin suna ta Saka albarka.

********* Bayan tafiyar Sameer can gurin aikin gidan suka wuce, ba karamin mamaki
Habib yayi ba har ya kasa hakuri ya tambayi Bilyaminu lokacin Mahmud Yana ciki.
"Dan Allah wane irin kudi gayen Nan ya bada haka Nan da Nan gidan ya juye ya Zama
kamar daukowa akayi daga wata kasar".
"Wallahi Nima bazance ga abinda ake kashewa ba, iya kudin aiki Dana abinci kawai
suke a hannuna, bakaga wash bakin fuska ba su biyu?'
"Eh nagansu"
Habib ya fada. "To ai tun jiya sukazo da komai na aikin bakaga Nata'ala ba shima
lebura ya koma kaga ai da malam shi yasa a Kira saboda 'yan gyare gyaren amman da
masu iyawar sukazo shima yaronsu ya koma".
Ya fada Yana dariya.
"Wallahi Bilya sai a kyaleka Kai kowama sai ka tab'a".
"Gaskiyar kenan ni wallahi burgeni ma yayi tunda baiyi zuciya ba ya tafi, ko banza
nasan Yana lure da koma Dan gyaran nasa aikin".

*****A bedroom din ammah Zahra ce da Sajida suke tattaunawa akan abinda ya
faru,sunyi iya nasu hasashen amma sun kasa gano bakin zare Sajida ce tace "nifa
Zahra Ina hasashen wani Abu akan lamarin ki"
"Kamar me kenan?"
Dan Jim tayi kafin tace "Anya ba asiri ake yiwa duk wani Wanda yazo da niyyar
aurenki ba? Ki tsaya kiyi nazarin abun Mana ko mafarkan da kike yi duk lokacin da
maganar aurenki ta taso abin dubawa ne"
Dan murmushi Zahrar tayi "kin jiki kema bestie wane irin asiri Kuma,ana zaune
lafiya to waye har ze bata lokacinsa da kudinsa gurin yi min wani Abu kawai daga
Allah ne kinsan kowa da yanda Allah make jarabtarsa ni tawace tazo a haka".
"Eh na yarda daga Allah ne bana inkari Amma akwai sanadi, inaga gobe ma zan wuce
duk da nacewa Umma sai Wednesday Amma na fasa wallahi Rimi zanje gurin Baban Umma
na fada Masa ai kinsan shi farin sani Kuma zeyi duk abinda ya kamata tunda ke wani
lokacin kanki ba Maths".
Kwarkwar tayi da ido Dan Allah Saji kada ki tafi ki Bari a Gama komai saiki tafin".
Wani kallo tayiwa Zahra "tafiya dole na tafi Amma zan dawo kwana kusa in Sha
Allah, kinsan Zama da Baffa yasa Ina Gane wasu abubuwan tunda Yana fadw min ire -
iren abubuwan da suka shafi sihiri Kinga yace min duk wani ciwon da yake da lokaci
misali ace kullun sai dare mutun yake kasa barci kinsan da matsala, ko ace mace duk
ranar girkinta Bata da lafiya ko duk ranar girkinta tana zubar da jini amma idan ta
Gama aikin shike nan sai ya dauke babu, ko kamar taki matsalar sai an saka Miki
ranar aure sai ana gaf da biki abun yake lalacewa, Kika sani ko Abban naku ma ya
Fara irin wannan tunanin ne yasa ya yanke wanna hukuncin cikin sirri ki tsaya kiyi
tunani Mana"
Sosai magungunan Sajida sun sakata a tunanin da Bata tabayi ba.
Sauke zazzafan numfashi tayi tana fadin "Allah ya kyauta ni duk kin sakani a tunani
wallahi"
Haba "Bestie ai kinsan ruwa baya tsami a banza me ake nema a gurin mace Allah Bai
Baki ba Amma sai an Yi abu kama-kama ya lalace zance da muka Dade munayj da Aunty
Hasana kenan jiya Kuma ta bain go ahead na naje na faduwa Baffan rimin, tace ma
zata fadawa Ammah, ma".
Kiran da Aunty Hasana tayi wa Sajida ne ya katse musu tattaunawar, ta tashi ta
fita.

Washe gari duk bakin Ammah suka tafi, Inna maimuna kadai suka Bari sai Amarya taje
dakinta zata koma gida.
Part din da bakin suka zauna Ammah tasa su Zilai suka gyara sosai tunda Daman nasu
Zahra ne, kafin yamma gurin yayi tas kamar ba'ayi wata dabdala a cikinsa ba.
Bayan sallar insha'i zahra da Sajida suka koma part din.
Suna zaune a kan gado Autan Ammah musaddiq ya shigo dakin da sallama hannunsa rike
da leda fara Mai kyau ya mikowa Zahra yana fadin "gashi Aunty inji wannan na gidan
Baba Malam din yace a kawo Miki Kuma yana duba ki, Kinga Nima ya bani".
Ya Mika nata 1 k din dake hannunsa.".
"To angode madallah".
Ledar Sajida ta dauka ta bude waya ta gani sabuwa kar a ciki.
"Wow gaskiya ba karya ke! Irin wannan babbar harka haka, Dan Allah Yi min bayani
naji yace wannan na gidan Baba malam din waye ko angon namu ne da ake Raina mana ya
Fara tsula Mana abun arziki haka?".
Baki ta Zahra ta zunbura.
"Nace Masa Ina bukatar sabuwar waya ne da zai kawo min, ni wallahi a mayar Masa".
Ta fada tana kokarin amsar ledar faga hannun sajidar.
"Ke tsaya da Allah yi min bayani yanda zan gane, Ina taking wayar naji kina wata
magana".

"Tana gurinsa tun safe ya karba ni bansan abinda zeyi da ita ba, ya dai ce na bashi
kawai ni kuma na bashin shine Kuma maimakon ya bani tawa shine ya Aiko min da
wannan".

Musaddiq Sajida ta kalla 'kai auta maza kaje kace tace ta gode Allah ya Kara nudi"
Sai da ya fita sannna ta juyo gurin Zahra. "Amman wallahi kin bani mamaki Allah ya
tarfawa garinki nono ki nemi ki Bata rawarki da tsalle to kici gaba har ki nuna
b'araka a gaban 'yan uba, Koda wasa kara ki Kara ba'a yiwa miji haka ko bakaso Abu
baka nunawa a gabansa, kika san da Yaya yayi sawo Miki danya faranta Miki Rai Amma
Zaki wani kwasale shi kice a mayar Masa kina son tun yanzu ki kashe Masa Gwiwa ko".
❤️ AUREN HUCE HAUSHI❤️

JINJINA TA MUSAMMAN GA MALAMAN MAKARANTA ALLAH YAYI JAGORA YA QARA BASIRA DA


JURIYAR SAUKEN NAUYIN DA AKA DORA MUKU NA AMANAR YARA QANANA✍️
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
This page is deducted to you Families of late Alhaji Isah Musa Bakin kasuwa
kazaure jigawa state.
🔷PAGE SEVEN🔷

_______Mika tayi tana salatin ma'aiki s a.w.w sannan ta Zoro kafafunta kasa, tunda
ta farka tasan tabbas karfe biyu tayi na sulsulin dare har ya zamar Mata jiki.
Dubanta ta kai inda Sajida ke kwance barcinta take sadidan cikin kwanciya hankali,
sai taji Ina ma ita ce haka, wasu hawayen ne suka ciko idanunta a hankali tace "Ya
Rabbi ga baiwarka Mai rauna ka jibinci lamarina dan Isar Manzon Allah s a.w.w.
kada ka barni da iyawata ka iya min da iyawarka kada ka Bari makiya su yi min
dariya ka bani rinjaye ka dorani akan duk Wanda yake son Hawa kaina".
Ta Mike tsam ta nufi toilet din cikin dakin sai Kuma ta fito saboda shaf ta manta
kafin su kwanta taga famfon ya dauke Kuma da alama ba'a kunna layinsu na tanki ba.
Cikin rashin tsoro ta bude kofar ta fita zuwa bayan part din Mama don ta kunno
ruwan, gurin ta dosa gadan gadan sai Kuma tayi turus, magana take jiyowa daga wurin
da sauri ta koma baya dan bata San abinda zata gani ba. Tana tsuma ita fa duk da
Bata da tsoro amma tana tsoron ganin abinda yafi karfin idonta ko Kuma wani mugun
abun.
Dole tayi hakurin yin sallar a koma ta kwanta tana ta sake-sake har kusan Asuba, ba
Kuma taji motsin wani na tada hankali ba.
Saida Sajida ta tashe ta lokacin har an Fara sallah a masallacin gidan nasu.
A gurguje tayo alwala da alama Sajida ce ta shigo da ruwan.
Bayan sunyi sallah zaman Azkar sukayi har lokacin da gari yayi shahhh alamar
wayewa, sannan suka koma suka kwanta. Dukkan su ba barci suke ba, Zahra ce ta danyi
tsaki kadan ta tashi zaune.
Kallonta Sajida tayi.
"Yaya Bestie akwai damuwa ne?"
Dan juyowa zahrar tayi tana kallon sajidar tana Kara wani tsakin "nifa wallahi na
fada Miki tsoron mutumin nan nakeji tun ranar Dana Fara ganinsa a gidan Baba malam
nake Jin wata irin shakkarsa. Dan Allah a haka zamu rayu bana ko son kallon
idanunsa? Kinsan wani tarin abin haushin jiya fa hannu yasa ya dago fuskata Wai
dole saina bude idona na kalle shi ko Kuma ya bani mamaki, Kuma fa ranar Nan a
asibiti har wani shafar min fuska yayi Yana fadar nayi hakuri da wannan hadin
shima ba so yake ba, kawai yayi biyaya ne tunda baze iya yiwa su Abba musu ba, amma
ni Ina iya fada musu bana so".
Baki Sajida ta rufe tana kunshe dariyar ta. Kai ta shiga girgizawa tana fadar
Babbar magana ki fadawa su Abba bakyaso! Wato ke ga marar ta ido ko? Shima har
yasan kimarsu da baze iya yin musu dasu ba saike ce marar kunya Zaki Fadi Baki so,
ki rabu dashi kwaai abinda nake so dake yanzu ki koyi dakewa a gaban nasa sannan
ki daina tsoron idanun nasa, Wai tsaya fada min menene a cikin idon nasa da yake
firgitaki duk girmanki da wayonki da wayewar ki?"
Wani shagwabe fuska tayi kamar Mai Shirin fasa kuka.
"Bazaki gabe ba, ni kaina bansan ya zanyi ba saboda shi fa na daina zuwa gidan Baba
malam tunda lokacin kullum Yana tare da shi kuma sai yayi ta kallona yana tsareni
da wadannan idunuwan nasa kamar Mai jin barci".
Yanzu dariya sosai Sajida keyi harda kwalla tana fadar Babbar magana tab kice abin
asali ya Samo shi ai kaya ne suka tsinke Masa a gidin kaba kece dai kike bulayi"
"Kamar yaya?"
"A'a bazakiji mutuwar sarki a bakina ba ai tunda an hada anyi Mai walahar...".
Sautin kiran waya ya dakatar da shegantakar da sajidar ke mata.
Wayar da aka kawo Mata jiya ce ta dauki kida, Sajida ce ta Mika hannu ta dauka M.M
DANGE ta gani Yana yawo akan screen din.
Zahra ta mikawa tana fadar oga ne da alama a Sha soyayya lfy. Tayi waje tana fadin
Bari naje nayiwa Ammah shara.
Bata daga Kiran ba har Saida ya kusa katsewa kana ta daga tasa a kunnenta. Daga can
taji Yana fadar "Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu".
A zuciyar ta a amsa Dan da gaske in dai zata ganshi ko taji maganarsa kasa samun
nutsuwa take.
Sake maimaita sallamar yayi, da kyar ta amsa masa tare da fadar " Ina kwana?"
Shiru taji ba'a amsa ba kamar ma an sauka daga layin, amma ga mamakinta tana
dubawa sai taga Yana nan, itama shirun tayi kudin sunata tafiya saita saka
handsfree ta aje wayar kusa da daga gefe tana kallon ikon Allah.
Saida ya mula Dan kansa "yace ya jikin naki I hope kin shan maganinki?"
"Eh" ta fada a takaice.
"Fine"yace shima a takaicen.
Ita mamaki ma yake Bata har wani turanci yake jefawa a magana kamar gaske.
"Sai an jima ta fada tana kokarin katse Kiran.
"Kada ki kuskurs ki kashe min Kira" ya fada in serious tongue.
Shiru tayi tana mamakinsa sai wata izza yake Mata kamar wani abin azo a gani.
Muryarshi ta tsinkaya Yana fadin ki bude data na turo Miki sako idan da abinda kike
bukatar ayi ko a Kara sai ki fada min, take care".
Kit ya kashe kiran.
"Kutt!" Ta fada "amman gayen nan yama Raina ni wlh Wai kada na kashe Masa waya"
Kwafa tayi "zakaga na kiraka ganin idon ka" ta Jafar da wayar tana mita.
Taso yin barci Amma ta kasa dole ta hakura, wayar ta Kara daukowa tana kare Mata
kallo.
Number din Hameeda ta Fara sakawa tunda taga sabon layi ne ya dauke natan, ga
mamakinta sai taga sunan Hameedar ya bayyana ba bata lokaci ta kira.
Tana ta ringing kamar baza'a dauka ba sai Kuma ta daga da sallama ai tana jin
muryar Zahra ta Fara mita "yanzu Dan Allah kin kyauta tun jiya nake neman layinki
Amma shiru na Kira Mama nace ta Baki tace min bakya Jin Dadi kina barci, wallahi
Kinga yanda hankalina ya tashi kuwa ki Bari lokacin da Sajida ta fada min halin da
ake ciki wallahi daba final muke ba Allah da barinta zanyi c/o na taho gida har
fada mukayi da Salma Wai ai sai inje na baiwa Mushahun hakuri ya dawo ya aure
maganganu dai gasu nan ki Bari kawai ai jibi zamu Gama in Sha Allah komai dare a
gida zan kwana".
"Allah ya yarda ki Bari kawai wallahi Ina cikin yanayi akwai damuwa Dan Allah kizo
ko naji sauki abubuwan".
Ta fada tana share hawaye, sukayi sallma Dan it ma Hameedar kukan take.
Wai ita Mushahu ya yiwa haka, duk wadanda suka fasa aurenta Bata taba Jin Wanda ya
Bata Mata Rai ya Kuma tsaya Mata kamar wannan ba ai ko wace irin matsala ce ita ya
kamata ya Fara fadawa ba ya yanke mu'amala da ita ba a lokacin da take matukar
bukatarsa ya manta shakuwar dake tsakanin su da alkawarirrikan da suka yiwa juna.

Kwantawa tayi tana tunanin baya a haka wani wahalallan barci yayi gaba da ita.

**********Tun Yana tsammanin ganin ta bude data ta duba sakon har ya cire Rai da
hakan.
Lambar Abdul Hakeem ya Kira sun jima suna waya kafin suyi sallama.
Laptop dinsa ya janyo yaci gaba da aiyukansa sai kusan azzahar ya Gama. toilet din
cikin dakin ya shiga ya dauro alwala,a masallacin hotel din Yaya sallah lokacin
daya fito Kiran Habib ya shigo Masa "Wai Dan Allah kana Ina ne tun dazu muke
nemanka kazo masu aikin hada furniture's din Nan ne suka Gama da cabinet din
kitchen".
"Ok gani Nan inaga kada kayi nisa zuwa an jima su Aunty zasuzo suga gurin"
Ya fada.
Yana nufar gurin da ya saba aje lifan din Habib.
Wayar Ammah Abdul Hakeem ya Kira ya fada Mata Mahmud yace a turo a gano gidan an
Gama gyaran, dakin Mama Ammah ta shiga ta fada Mata sannan Kira Aunty Hasana ta
fada Mata kafin ta wuce gurin Alhajin ta fada Masa tunda shiya dawo daga gidan
gonar sai su Abdul Hakeem ya baro suna yiwa shanu Allura da Basu magunguna.
Wurin karfe biyar Aunty Hasana ta debesu a mota harda Sajida suka nufi Hayin bankin
cikin jagorancin Habib, lokacin Inna Bata Nan taje MIYA gurin wata aminiyar ta da
sukayi aikin Haji shekara daya.

Duk cikinsu ba wadda Bata kadu da ganin gidan ba domin ba karaya an narka
mahaukatan kudi a gidan bazaka tab'a cewa renovation akayi Masa ba, bedroom's ne
guda uku biyu suna kallon juna dayan Kuma daga gefe da alama yafi sauran girma
Kuma shi kadai ne a rufe, sun zagaya ko Ina sai santin gidan Sajida tace tana ta
daukar video, falon kadai abin kallo ne duk da ba komai a cikinsa sai fitilu da aka
kunna sai Kuma AC da aka ware.
Hajiya mama ce ta kasa hakuri ta leka ta Kira Habib Nan falon ya shigo Yana fadin
"gani Mama"
Yana Dan rankwafawa.
Aunty Hasana mama ta kalla "Hasana Dan Allah ki tayani tambayar yaron Nan tunda
shi namu ne na gida baze cucemu ba, Wai wannan yaron sana'ar me yake daya iya Kama
hayar wannan uban gidan"?"
Kara risinawa yayi Yana fadar "ba haya ya Kama ba Baba malam ne ya bashi kyauta,
sai Kuma kungiyar yake yiwa aiki suka kawo masu aiki suka yiwa gidan 'yan gyare -
gyare harda kayan daki ma suka zuba masa, Bismillah Bari na bude muku ku gani yanzu
ba dadewa zuka Gama hadawa da kitchen din suka tafi".
Dakin ya bude musu ba Hajiya mama da take ta kwana biyu ba, ko Aunty Hasana da
Sajida Saida suka Zama 'yan kauye Dan tunda suke Basu taba ganin irin wanna gadon a
zahiri ba, ita kanta aunty Hasana lamarin Yana neman ya gagari tunaninta fa ance
Almajirin Baba malam to Amma idan aka saka mizanin hankali abin yafi karfin yanda
aka fada to wane irin NGO's ne da suke irin wannan aikin akan daidaikun ma'aikatan
su haka?" Gaskiya abin akwai abin dubawa.
Lokacin da suka fito harabar gidan ne wata Hilux ta shigo da kaya a bayan motar
mutane uku ne a motar bakar fata biyu fari daya Kamar balarabe Kamar kwara.
Kameme Hajiya mama ta hanasu tafiya sai da aka sauke kayan ta gani abinda da suka
Gane irin katuwar plasima din Nan Mai cin Rabin bangon Nan ne kawai amman sauran
tarkacen Basu Gane komai ba, haka suka kada suka tafi mama nata mitar "A'a da sake
Alhaji ya titsiya yaron Nan saiya nuna Iyayen shi kafin a Kai Masa yarinyar Nan
haka kawai aje ayi kitso da kwarkawata mutanen yanzu ba abin yarda bane sai kaga
mutum har mutum Amman a Baki malam a ciki Kuma Fir'auna".
Maganar data Basu Aunty dariya kenan.

❤️
❤️
❤️
AUREN HUCE HAUSHI

❤️
❤️
❤️

STORY
AND
. WRITTEN
BY
MAMAN FATIMAH
PAGE EIGHT

Lokacin da suka shigo gidan ana ta kokarin daura alwalar sallar magariba.
Sai bayan sallar insha'i ne Mama ta shigo dakin Ammah suka hadu da Aunty
Hasana suna fadawa Ammah yanda suka gano gidan da Kuma yanda abin ya daure musu
kai.
Nisawa Ammar tayi tana fadar "Mama ki Sami Abban kiyi Masa bayani yanda ze
fahimta kinsan yanda suke da malam bana tunanin wannan abun ze saka ya canza
ra'ayinsa duba da yanda ya yanke hukuncinsa Bai nemi shawarar kowa ba".
"Aiko dai ya kamata ayi wani Abu gaskiya Nima lamarin ya tsaya mini a cikin
zuciya".
Aunty Hasana ta fada.
Sun jima suna tattaunawar kafin Mama ta koma daki tabar Autty Hasanar da Ammah.
Zama Aunty Hasanar ta kyara ta fuskanci Ammar ta Kira sunanta "Anya wannan
Mahmud din ba abinda yake boyewa kuwa Ammah Kinga gidan kuwa ga wannan uwar wayar
daya canza Mata kinsan kudinta kuwa ? gaskiya I doubt much, ni dai kiyiwa Abban
magana da kanki Kamar zefi daukar abun serious akan na Mama".
Can Kuma sajida ce tasa Zahra a gaba tana ta faman zuba.
"Innalillahi! Kinga gidanki kuwa? Allah ya bamu ya taku wallahi Zahra ki godewa
Allah. Wallahi Allah ya Gama miki duk wata ni'ima ta ko Ina kinyi gaban da Nan
kurkusa dai kafin a fiki za'a Dade ana lalube. Zahra Naga mijinki har mun gaisa ada
Ina adawa da auren Amma tunda na ganshi Naga Yana yinsa nasan yanzu ne kikayi aure
da mijin daya Dace ke.Kawai dai matsalar za'ace ba Mai kudi bane,amma a yanda gidan
da zaya ajeki yake wallahi ko minister ne sai hakan, akwai abinda na gani a
gidanki wallahi ban taba gani a gidanki kowa ba duk yawona sai dai a film amma dai
a zahiri A'a ban taba gani ba Allah Bai kaini gurin ba".
Tunda ta Fara zuba Zahrar ke bin sajida da idon lokaci daya duk ta wani rude sai
zuba take Kamar 'ya 'yan kanya.
"Kin Gama?"
zahrar ta tambayi sajidar.
"Eh na Gama aini an ma yanka ta tashi na fasa tafiyar zanyi waya da Mom taje can
Rimin sumailar gurin Baffan kawai, tunda Daman zatazo nan din ba suna kwantagora".
"Ke Kika sani dai tunda Naga kina nema ki Zama wata daban ko dai an canza min ke da
wata ne ko Kuma wani abun ya fada Miki ya goge Miki hadda ne?".
"Eh da alama Kam Dan ya fiki iya lafazi gaskiya inaga na Zama 'yar team dinsa fa
tunda Naga ke Baki da wayo".

Ta fada tana dariya.

Washe gari tun safe Abba yasa aka Kai furniture's din Zahra gidan Daman Aunty
Hasana sunyi magana da Wanda zasu hada musu kayan, kayan kitchen da sauran
kayayyakin duk suna gidan Aunty Hasana daga can aka ringa daukowa, masu aikin su
suka hada komai na gidan hatta kitchen su suka gyara komai, gidan ba karamin kyau
yayi ba, ba karya duk Wanda yaga gidan yasan na 'yar gata ne.Dan wasu irin
mahaukatan Turkish furniture's ne wanda kakanninta ta gurin uwa sukayi Mata duk
wani abun more rayuwa akwai shi a gidan Nan, bangaren electronics ma sai a cikin
lockers aka zuba wasu, komai yayi.
Lokacin da aka Gama gyaran Aunty Hasana da sajida ne sukazo gani ba karamin burgesu
gidan yayi ba Dan sai yanzu ne ya fito a asalinsa na kyau da kayatar da Mai gani,
komai na gidan unique ne Masha Allah.

A waya sajida ta daukowa Ammah komai. Ita kanta Ammah Kai Kawai take jinjinawa Dan
ba karamin burgeta abin yayi ba, sai dai can kasan ranta rudani ne kala-kala domin
abin ne duk yazo a hagunce.
Tana tsoron lamarin sosai sai da har abada baza iya jayayya da Alhajin ba Dan da
gaske ubane tsayayye Wanda baya nuna banbanci tsakanin abinda ya Haifa da Wanda
yake bashi ya Haifa ba, amma harga Allah tana zulumin wannan AUREN HUCE HAUSHIN da
Alhajin yayiwa 'yar marainiyar Allah, mazan yanzu sunce suna sonka ma ya kukan kare
idan Zama yayi Zama ballantana matar cushe ta San komai Daren dadewa ranar da yaga
irin matar da yake so Sai dai zahra tayi hakurin zama Kawai, duk da tasan Bata da
haufi akan yarinyar Tata Dan macece har mace abin alfaharin kowa ne namiji ace ya
mallaki Kamar ta, to Amma shi lamarin so daban yake duk kyan mutum da asalinsa ba
lallai ne ace yana burge kowa ba domin shi dai so makaho ne.
Ajiyar zuciya ta sauke a hankali duk jikinta yayi Mata wani irin Sanya ta kalli
Aunty Hasana tace "Hasana Ina jin wani irin rauni a zuciya ta game da lamarin nan
Ina tausayin yarinyar nan rayuwa tana ta walagigi da ita sai nake ganin Kamar laifi
nane Dana kafe a barmin yarinyar Nan na hana kakanninta ita ni Kuma nayi sakacin da
aka maida rayuwar ta Kamar kwallo ana ta dokata daga Nan zuwa nan".
Ta karasa maganar hawaye na zubo mata.
Abinda tunda Allah ya kawo Aunty Hasana duniya Bata taba gani ba a zahiri gurin
Ammah Nan da Nan hankalinta ya tashi sajida ma kukan ta Fara duk da batasas
takamaimai man abinda ya saka Ammah kukan ba, tashi tayi ta fice daga dakin jin an
Fara Kiran sallar magariba.
Aunty Hasana ce tace "Haba Ammah duk yanda Kika jure bakin cikin baya na abubuwan
da suka faru Baki taba zubar da hawaye ba sai yanzu da Allah ya nufa akayi ai
godiya Zaki yiwa Allah daya kawo karshen wahalar ba kuka ba".
Gefen zani tasa tana goge hawayen.
"Hasana Ina hango abinda ke bakya hangowa ne,masu iya magana suna cewa matar shige
Bata daraja ba irin wannan rayuwar na sowa Zahra ba to sai dai kana naka Allah Yana
nasa Kuma nasan ne gaskiya. Ba komai haka Allah ya tsara komai mukaddari ne daga
gare shi, naji Alhaji Yana maganar zuwa juma'a za'a kaita".

*******Tun bayan kammala karatunsu na bayan insha'i da suke na littafin iziyya yake
zaune a kusa da Baba malam har kowa ya watse ya rage saura su biyu tunda malam yaga
haka yasan da magana a bakin Mahmud ne.
"Ya ya akayi ne Mahmuda?"
Malam ya jefo Masa tambayar, Kara dukar da Kai yayi kafin yace "Daman maganar kayan
lefe ne dazu Oga Sameer ya kirani yace ya hado tasa gudunmawar kenan, shine nace
Bari na fada maka Dan kasan da zuwansu".
"Ikon Allah shi wannan yaron baya gajiya ne Kamar baisan ciwon nema ba tunda yazo
ya riski maganar Nan yake Yi kan jiki kan karfi. Allah ya saka Masa da Alkhairi
yabar muku zumunci".
"Ameen" ya amsa.
Harya Mike ze tafi sai malam din ya dakatar dashi, dawowa yayi zauna.
Gyaran murya malam din yafa kafin ta jefo Masa tambayar.
"Sai zuwa yaushe ne kake ganin zamuje ga mahaifan naka kaga dole muje musu tunda
wannan lamarin ya faru".
Kai ya sadda kasa Yana fadin "zamuje in Sha Allah Amma Dan Allah a Kara min lokaci
da kaina zanyi maganar ayi hakuri".
"To ba laifi Allah ya iya Mana kaje ka Samu su Habibu kuje acan gidan ku kwana kaga
sun zuba dukiyar kasan yanzu mutum ake kiwo ba dabba ba".
"To in Sha Allah za'ayi hakan amma ni Ina Nan sai dai su Habib din suje".
"To ai hakan ma yayi Allah yayi Albarka".
Saida ya dudduba dakunan yaran ya tabbatar da komai lafiya lokacin sha biyu ta
wuce, dakinsu ya nufa wanka yayi ya saka kayan barci sannan ya hau gado ya bude
laptop dinsa. Email dinsa ya shiga Yana duba sakknnin daya samu sakon daya shigo ne
ya dauki hankalinsa.
"Ya Salam!".
Abinda ya iya ambata kenan sai Kuma sautin daddad'an ringtone dinsa ya karade
dakin.
"Sameer!" Ya fada a hankali yasan za'ayi haka, ya haga wayar Yana fadin "Ta Yaya
hakan ya faru?"

Daga can bangaren Sameer din yadan furzar huci Mai zafi Yana fadar "wallahi nayi
duk yanda zanyi Amma abun yaki yuwuwa dole ka daura ka kawar da komai muje gaskiya
Dan kasan tunda akaje Nan zuwan nake ne Kawai mafita".
"Amman ai kasan halin da ake ciki so kake ace na gudu nabar 'yar mutane Eyeh?".
"Cool down Mana my man abin Bai Kai nan ba aikin daine ya taso na gaggawa Kuma dole
sai da Kai za'ayi Dan haka suyi hakuri su aje maka ita zuwa sanda ka dawo ko Kuma
ka dauko abarka ku tafi, kaga ai tafiyar tafi yi maka armashi ko?"
Ya fada cikin zolaya.
"Dan Allah ka Zama serious mana, kayi duk abinda ya kamata a Nan goben ka hakura da
zuwan ka turo wannan friend din naka tunda yasan gurin ya kawo kayan kawai, Kai
Kuma ka Kira Baba malam ka fada Masa daga can sun nemi ganin wakilansu na kasa da
jahoshi da kananan hukumomi nasan dai kome ake ciki baze wuce kwana buying zuwa uku
ba kaga lokacin na tare a gidana nafi son na barta a Nan gidana akan na tafi Bata
tare ba".

"Ko dai.......?"
Sameer ya fada Yana dariya.
"Allah ya shiryeka ko dai me? kasan ni salihn ne ba ruwana da wannan sabgar sai
ku".
Kit ya kashe wayar sannan yayi switch off dinta.

Misalin karfe Sha biyun Rana wata tamfatsetsiyar mota Parker a kofar gidan malam.
Akwatuna Yara suka dunga saukewa suna shiga falon malam saida suka Gama sannan baki
nufi falon malam din bisa jagorancin Habib sun gaisa sosai da malam suka gabatar
Masa da kayan daga Sameer.
Malam yayi godiya ya saka Albarka ba adadi.
Falon malam ya bar musu sukaci abinci suka huta sannan Habib ya rakasu can gidan
suka gaisa da Mahmud din.
Sai bayan Azahar suka tafi malam yayi musu Sha Tara ta arziki.
Kayan malam yace suje su duba su gani saboda da an jima za'a Mika musu can gidan
Alhajin.
Kaya ne na gani na fada an zubasu Kamar ba gobe, an shigarwa da iya Abu ciki ta
gani malam yace ta turawa makotanta na kusa suzo su gani anjima za'a Mika musu.
Bayan fitowa daga sallar la'asar ne Malam Bukar ya fadawa Alhaji yanzu su malam
Mudi da Alaramma malam Haruna zasu kawo kayan Zahara'u.
Fada Alhajin yayi akan kayan da za'a kawo Yana fadar "Haba malam Dan me za'ayi min
haka ko wancen da aka fasa auren Kai sheda ne ban karbi lefe ba da suka matsa cewa
nayi suje da kayan idan tazo saiya ba matarsa".
Kai malam yanjinjina Yana fadin "Anyi hakan Kam amma wannan shima bamu muka hada ba
wannan yaron Sameeru ne ya turo dasu dazu yace gudunmawarsa ce aba Amarya"
"Ikon Allah shi baya gajiya da dawainya haka daga wannan sai wance Allah ya saka da
Alkhairi ya bar.zumunci na jima banga yaro mai karqmcinsa ba abin duniya Bai rufe
Masa ido ba".

Da yamma su sajida suna zaune suna Shira ita da Zahra da wata kawar Zahra Mujiba
Nan take makotansu suna dasawa da Zahra sosai sun Kuma yi sabo sosai da Sajida tun
lokacin da sake zuwa hutu da Sajidar lokacin suna makaranta.
Ba zato ba tsammani Yara suka shigo da manyan jakunkuna dasu cylinder din gas, ai
Zahra na ganin haka ta tashi da sauri ta nufi hanyar shigowa gidan da gudu ta
karasa Kamar karamar yarinya suka rungume juna da Hameeda Kamar zasu fadi. Suna
rike da hannun suka shigo ciki su Mujiba suna ta faman yi Mata sannu da zuwa, sai
daga baya Salma ta shigo tana wani shankanshi Bata kula su Zahra ba Suma ba Wanda
ya kula ta, directly dakin Mama ta nufa.
Kamar jira ake Salma ta wuce saiga su Magaji da manyan Akwatunan lefe suna shigowa
da sauri Zilai Mai aiki ta warto Babbar tabarma ta baza tana rabsa guda tana fadin
"Masha Allah! Alherin Allah ya sauka. Fara Mai farar aniya sukari bakai farin banza
Fatima Zahara'u 'yar Muhammadu sani, jikar hardon fulanin Mubi, Amarya gidan Mahmud
Kuma uwar gidansa Alherin Allah ya Kai Miki, Mama!Ammah ku fito ga abin arziki ya
sauka". Har rige-rigen fitowa a key tsakanin Mama da Salma yayin daga dakin Ammah
Inna maimuna ta fito.
❤️
❤️
AUREN HUCE HAUSHIN
❤️
❤️

WRITTEN
BY
MAMAN FATIMAH

PAGE NINE🔷(9)

____Akwatuna ne na garari masu tsadedden kyau har set biyu aka shigo dasu, sai wasu
irin manyan jakunkuna guda uku, guda Zilai ta dinga gud tana fadin "wani kaya sai
amale wane jaki. Allah ya Kara daukaki Fatima ya Dora ki akan makiyanki lallai
girma sai dan girma kaga wadda ta gaji arziki gaba da baya"
Inna maimuna ce ta jimko kudi ta dankawa zilai tana fadin "na fanshi jikata tunda
kin koma roko".
Dariya tayi tana fadin "wallahi Inna Dana iya kirarin da yafi wannan da nayi Mata.
Uwar dakina murucin kan dutse ce Bata fito ba Saida ta shirya, yakuwar akan
kabarice bakin cikin 'yan taushe, bikin cikinka sauro yau ga xanzaro a bene" .
Ta Kara kwarara wata gudar.
Da sauri Mama ma tazo ta dankawa zilai kudi tana fadin yau ai ranar farin ciki ce
maza bude Mana muga karamar Arziki"
Tunda aka Fara shigo da kayan Zahra tayi dakinsu tabar su Sajidar anan.Hameeda da
zilai ne suke fama bude kayan suna santinsu komai na ciki Mai kyau ne ba karya duk
wadda ta hado kayan 'yar gayu ce ta gani kasheni komai na ciki classic ne.
Saida suka bude kowa ne akwatin duka Sha biyun.
Ba abinda Inna maimuna ke maimatawa sai Masha Allah,Allah ya kade fitina yasa gurin
zamane Allah ya hada arzikinsau.
Duk bidirin da ake Salma na tsaye Bata taba ko tsinke a ciki ba sai cika take tana
batsewa Kamar anyi Mata dole sai ta zaune a gurin.
Su Sajida da Mujiba da Hameeda ne suka shigar da kayan falon Ammah.
Sai da suka jerasu sannan Hameeda ta nufi dakin Mama su Kuma su Mujiba suka nufi
gurin Zahra.
Wata uwar harara Salma da dokawa Hameeda tafin tayi dogon tsaki tana fadin "Allah
wadaran naka ya lalace yanzu ke ko kishin Kai Baki dashi Kika bige gurin jidar
kayan kanwar bayanki kina wani washe Baki ke game kirki". Baki Hameedar ta murguda
Mata tayi gaba tana cewa "Ina ruwanki Aunty Salma danke bakya ra'ayinta dole Nima
sai nabi naki ra'ayi kowa yayi ta kansa kawai ni bana ara na yafa abinda Babu
ruwana ba.
Mama ce ta fito daga bed room dinta fuskarta a hade da waya a hannunta kallon
Hameedar tayi "to rasa kunya b'eran tanka Dan ta fada Miki gaskiya Zaki kare Mata
tana din rashin mutunci cewa nake koni Dana tsuguna na haifeki ban Isa kizo inda
nake ba Saida Kika dangana da gurin kanwar uwarki".
Baki Hameedar ta zumbura tayi gaba tana magana kasa -kasa.
"Ai Daman za'a rina tunda Naga kin biyo Mama daki, wallahi mutum ya kiyayi gulma da
munafurci in dai yansla son yaga ci gaba a rayuwarsa"
Tana Gama fada ta shige uwar daki.
A waya Ammqh ta Kira Aunty Hasana ta fada Mata an kawo lefen Zahra.
Lokacin da tazo taga kayan ta kadu da gasken gaske, Amma dai Bata furta komai ba
kada Ammah taga Kamar Bata son auren ne ko wani Abu.
Sai bayan sallar magariba Mujiba tayiwa su Ammah sallama Sajida ta rakata ita
Haidar din Aunty Hasana.
Tun Zahra na tsammanin ganin Hameeda har ta hakura saboda dare ya fara so sai Dan
Sajida har tayi barci, sai tayi Kamar ta kirata a waya saita fasa, da taga zaman
yayi yawa sai ta dauko alqur'ani ta Fara karatu har Saida daya ta gota sannan tayi
addu'a ta shafa.
Kwantawa tayi rigingine tana tariyo rayuwartan ta baya komai ya ringa dawo Mata
Kamar lokacin yake faruwa
************_
_
TUSHEN LABARIN

AZARE KATAGUM L.G.A


BAUCHI STATE
UNGUWAR FAMFON SHANU.
Yarinya ce 'yar kimanin sheKara goma Sha biyu haka, kyakykyawar gaske fara irin
farin Nan Mai hade da Kamar golden yellow , idanunta dara-dara farare tas sai
gashin kanta bakirkirin har gadon bayanta hancinta irin dogon Nan ne har baka
bakinta Dan karami Mai dauke da 'yan jaja-jaja pink-pink din lebe, bazaka kirata
doguwa sosai ba irin tsaka tsakiyar nan, jikin lublub Kamar Mai rayuwa a kasanshen
sanyi komai nata Mai kyau ne Wanda idan ka kalleta saika Kara kallonta Dan Allah
s.w.a yayi Mata sura Mai kyau na a gani a Kara kalla. Da sallama ta shigo cikin
gida tana fadar "wash Allah Ammah wallahi na gaji wadannan littatafan sunyi nauyi
da yawa inaga sai dai na kwafo time table kullum na ringa zuwa da Wanda zamuyi
amfani dasu kawai". Ta fada tana kokarin Ciro jikar daga bayanta, dariya Ammah tayi
tana fadin "ke dai anyi raguwa wallahi zahra ke Sam bakya da juriya jakar da Zaki
Goya zuwa mota ma neman gagararki tajeyi".
Kwantawa tayi saman kujera tana fadin "Allah da nauyi dauki fa kiji".
Sulaiman ne ya shigo shima da tasa jakar a kafada Yana dariya.
"Kai Kuma dariyar me kake?"
Ammah ta tambaye shi.
Zahra ya nuna Yana cigaba da dariya. Baki ta zumbura tana dira kafa tana fadar
"Allaha Ammah ki rabani da Ya sulaiman Kinga tundazu yake min dariya Kuma nace ya
tayani daukar jikar ya Kiya".
"Wai Kai meye haka kazo kana ta dariya Kamar wani sabon kamu".
Jakarsa ya jefa kusa data Zahra kafin ya zauna Yana ba Ammah labari.
"Wato Ammah muna hanyar dawowa ne man motar ya Kare tunanin Malam Bala harya kawo
mu gida man Bai Kare ba saboda yace ya biya gidan man yaga da layi idan yace zebi
layin zamu Dade muna jiransa shine kawai ya taho, to muna zuwa wurin gidan sarki
kawai man motar Nan ya Kare shine fa muka tako a kafa, ita Kuma gwanar iya son jiki
ta wani shagwabe mini Wai na daukar Mata jaka na hada da tawa Kamar wani jaki,
shine Dan tsabar rainin hankali Wai to na dauka zata karbi kudin gurin Abba ta
biyani Kamar wani Dan dako".
Tsaki Ammah tayi tana hararar Sulaiman din "wannan shine abin dariyar Kuma wallahi
kayi girman kwabo da meye amfanin hada babba da yaron ba saboda taimakon ba".
"A'a Ammah duka da wata biyar fa na girme mata, to Ina wani girma sa'anni muke ba
gashi ajinmu daya ba da dai su Ya Sadiq ne su Aunty Janah, kuma fa duk su Hameeda
kowa fa ya dauko tasa sai itace tafi kowa son jika za'a daukar Mata wa zata yiwa
karatun ba kanta ba".
Ya fada Yana cire safarsa.
Fita Ammah tayi, ita Kuma Zahra ta shige bedroom din Ammah ba Wanda ya Kara bi
takan sulaiman.wanka ta shiga tayi kafin taci abinci saboda Bata son ta makara a
islamiyya Sam Bata son abinda ze taba lafiyar jikinta tunda a makarantar bokon suke
sallar Azahar.
Lokacin data fito tana sanye da uniform din islamiyya da Jakarta tana kokarin shiga
dakin Mama ta biya Hameeda ne taga Hameedar da wani Kaya a wata leda babba ta fito
tana zumburar Baki.
"Ya Naga Baki shirya ba ko bazaki makarantar ba? Kinga fa yau zamu bada hadda".
Mama ce ta fito daga dakin tana hararar Zahra "to uwar kinibibi bazatan ba ki Kama
hanya ki wuce, ko zata ai bazaku tafi tare ba ana gqninki waye ze kalleta na nuna
Miki bana son kina shige Mata amman kin kasa ganewa, Haba yarinya sai kwawa"
Duk wanna maganar da Mama takeyi a hankali take fada Banda Zahrar da Hameedar ba
Mai jin abinda take fada duk da Ammah na kofar kitchen dinsu Wanda yake kusa da
bangaren na Mama.
Daki Mama ta nunawa Hameeda ta koma yayin da Zahra ta nufi Ammah tana fadin "Ammah
na tafi"
"To Allah ya bada sa'a a maida hankali ki biyawa Mujiba ki tafi".
"To" ta amsa ta nufi waje da sauri.
Saida dama Ammah tana ankare da Mama Sam Bata son Zahra na mu'amala da Hameeda
kwata-kwata sai Kuma Allah ya hada wata irin kauna tsakanin yaran salma ce Sam basa
jituwa da Zahra da ita wata sakarai ce da zahra ko ruwa Mai dadi Salma bazata Bari
Tasha a gidan ba, motsi ba motsi ba sai ta Fara fadin ai dai Nan ba gidanki bane ke
'yar riko ce.
Lokacin da Ammah taji maganar a bakin yarinyar tayi mamaki sosai Dan a lokacin
wayonta Bai Kai ta iya banbance tsakanin Dan gida na ruko.
Da Ammah ta tsareta ta fada Mata wayace Zahra ba 'yar gidan bace sai tace " Mama ce
ta fada tace min na duba Mana Naga ko kalar jiki mu ba iri daya bace mu daina
tafiya ma da ita, Wai ta fimu kyau idan muna binta idan muka girma baza'a sure mu
ba".
Kan Salma Ammah ta dafa tana fadin "itama 'yar uwarku ce kuyi zumunci da ita kinji"
kai ta gyada alamar to.
Abin ya jima Yana baiwa Ammah mamaki Bata zaci haka a gurin mamar ba, tunda a
zahiri ba komai a tsakaninsu sai mutunta juna duk da tasan sha'anin kishi ta ciki
na ciki ne ta baka na baka.
Sai kusan magariba su zahra suka shigo hannunsu na sarkafe da juna ita da Hameedar,
daga gurin Aiken ta wuce makarantar Amma Tasha bulalar makara.
Bayan sun Gama cin abincin dare ne suna hira a dakin Ammah Hameeda ta shigo ta
gaishe da Ammah ta zauna sukaci gaba da hira lokacin Ammar tana dakin Abbansu ta
Kai Masa abinci.
Lokacin data shigo dakin ya kacame sunata musu akan wani aiki da akayi musu yau a
makaranta su matan suna ga yanda za'ayi shi Kuma Sulaiman Yana fadar ga yanda
za'ayi, Ammar ce ta zauna tana fadin su kawo ta gani maths ne, Kuma duk hanyar da
akabi za'a kaiga samun amsar Dan haka tace kowa yayi nasa yanda ya fashimta.
Har ta shiga bedroom dinta ta fito tana fadin "Na manta Abbanku yace na fada muku
ranar Saturday zakiyi jarabawar share fagen shiga karamar secondary school ta
kwamnatin tarayya, yace kuyi karatu duk Wanda baici ba baze saimasa ba Saida yaci
gaba a makarantar da yake".
Murna suka farayi da gudu Hameeda ta nufi dakinsu Dan ta fadawa Mama.

******Alhaji Jafar Mai yadi haifaffan garin Azare ne ta jihar Bauch a unguwar
fanfon shanu, su hudu ne iyayensu suka Haifa uku maza sai autarsu daya mace amman
su biyu suka rayu biyu tun suna Yara suka rasu, sun taso shi da kanwarsa Amina a
hannun Babarsu Hajiya Fatima wadda ake kiranta da Nanna, kasancewar Babansu Malam
Ibrahim Wanda ake Masa laqabi khalilu Allah yayi masa rasuwa tun Yana aji day na
babbar sakandire Amina Kuma tana aji shida na primary.
Sun Sha wahala kasancewar mahaifan su ba Mai karfi bane Bai bar musu wani Abu Mai
yawa ba daga gidan da suke cikin sai konaki biyu, tunda Jafar ya Gama babbar
sakandire yake zaune a gida saidai dinkin hula da aikin hannu na riguna kusan dashi
yake rike Nanna da Amina said Kuma 'yan kulle-kullen kayan Miya daaya kafawa Nanna
jarinsu.
A hankali Jafar yana Tara kudinsa lokacin daya da yaga kudin sun danyi auki ya nemi
Shawarar Nanna akan yana son ya Fara sayar da Yadiddika na maza, tayi murna sosai
ta dinga saka Masa albarka.
Cikin ikon Allah ya Fara kasuwar da kafar dama Nan da Nan abun ya Fara bunkasa da
taimakon wani uban gida da Allah ya hada jininsu yake bashi Kaya akan farashi Mai
sauki har takai ga Fara tura shi aba Yana sawo Masa Kaya a hankali ya bashi aron
kudi masu Dan yawa yace shima ya hada da nasa jarin ya sawo nasa kayan zeyi Masa
kokarin shago kafin ya dawo.
Nan da Nan al'amura suka kankama ba'a rufe shekara ba arzikinsau ya Fara habaka da
taimakon Ubangidansa ya samu Yara masu amana ya zuba a shagon shi Kuma ya shiga
cuku- cukun nema admission Nan University ta Bauchi cikin ikon Allah ya samu course
din da ya nema Agricultural science.
Cikin ikon Allah karatu ya kankama, yayin da a gefe ga kasuwanci Yana ta habaka.
Lokacin Yana shiga level 300 lokaci Amina ta kammala secondary dinta manema sukayi
Mata chaaaa, Amma an kada an raya ta fitar da gwani ta Kiya Wai duk Bata sonsu.
Haha aka tattara aka kyaleta Jafar yaso ya nemar Mata gurbin karatun N.C.E Amma
Nanna tayi tsalle ta dire ba za'a wannan aiki da ita ba, haka suka zauna har kusan
shekara Amina ita ba karatun ba ba auren ba.
Wata ranar juma'a lokacin su Jafar sunzo hutun karshen first semester na level 400,
Nanna ta aiki Amina kasuwa gurin Jafar ta karbo Mata wasu kudi uzurinsu ya taso
Mata na gaggawa.
Lokacin da taje baya shogon nasa Yana shagon Ubangidansa Alhaji Dauda, can ta nufa
tunda tasan shagon nasa.
Suna ciki Hira da bakon Alhaji Dauda kawai ya hango Amina ta nufo shagon tana
gaishe da Alhajin daya fita a lokacin, kafin ta karaso har taso ya nufo ta Yana
fadin"lafiya Amina? Daga Ina kike?"
Dariya tayi kyawawan hakoranta jerarru farare tas suka bayyana tana fadin "kai Yaya
ba komai fa Nanna ce ta Aiko ni".
Fita sukayi ta fada Masa sakon sukaje shago ya Bata ai Bari ta hau abin Hawa ba ya
dauketa a mashin dinsa suka tafi gida.
Da dare Yana zaune a inda suke Hira yaga motar Alhaji Dauda ta tsaya a kofar
gidansu da sauri ya tashi ya nufi inda yayi parking sai yaga harda bakon Alhajin
Zakariyya suke tare, sun gaisa sosai kafin Alhaji Daudan ya fada Masa Amininsa Kuma
Dan uwansa ne yaga Amina Yana so shine nace yazo muji da zafi -zafi akan bugi
karfe.
Jafar yaji Dadi sosai zaifi kowa murna idan hakan ta kasance Dan ya yaba sosai da
hankalinsa sosai.
Cikin gidan Jafar ya shiga ba jimawa ya fito Yana musu iso ciki sun gaisa da Nanna
Alhaji Dauda ne yayiwa Nanna bayanin koma itama irin amsar Jafar ta fada idan tana
so ba matsala ba inda aure baya Kai mace Nasarawa batayi nisa ba.
Cikin ikon Allah kuwa Amina taji Alhaji Zakariyya ya kwanta mata a rai Kuma zata
iya aurensa duk da fada Mata Yana da Mata harda Yara biyu.
A cikin wata biyu akayi bikin Amina da Alhaji zakariyyan, Jafar yayi Mata komai da
uba yake aka kaita can Nasarawa state cikin garin Akwanga.
Wannan kenan.
Haka Jafar yaci gaba da karatunsa har ya Gama ya dawo gida Yana jiran shiga camp.
Lokacin da saki post na tafiya service sunan Jafar ya Fado a cikin masu zuwa Jos
yayi murna sosai ko banza Yana jiyo kamshin gida tunda suna makotan jahohi.
Bayan gama zaman camp wata makarantar 'yan Mata jeka ka dawo aka Kai Jafar, Baiyi
wata biyu ba Allah ya hada shi da wata yarinya Rabi'a yaji yarinyar ta kwanta Masa
tana Kuma da irin Qualities din da yake fatan Samu a gurin matarsa.
Zuwa lokacin gama service dinsu har magana tayi karfi inda iyaye suka shiga.
Wani gida Jafar ya saya kusa da gidansu ya gyara' ba'a dauki lokaci ba akayi
bikinsa da Rabi'a suka tare a gidansu. Duk wata kulawarsa da soyayya ya tattara ya
baiwa Rabi'a ba abinda ta nema ta rasa sai abinda baza'a rasa ba. Rabi'a irin matan
Nan ne masu kissa kafin wani lokaci ta kanainaye zuciyar Nanna.
Kwanci tashi ba wahala a gurin Allah aurensu ya shekara Amma kalubaken da suka Fara
fuskanta na Rashn zaman ciki a jikin Rabi'a kusan barinta uku. Ana haka Jafar ya
samu aiki da ma'aikatar gona ta jihar Bauchi BARDA.
Cikin kankanin lokaci kofofin wadata suka budewa Jafar kafin shekara biyu ya gina
gida Mai kyau sunje makka shida Nanna.
Nan da Nan likafa tayi gaba Amma dai matsalar su na Nan ta rashin haihuwa.
Yayin da abin ma ya Fara damun Nanna har ta gaji tayi Masa magana akan ko maganin
hausa za'a fata nemawa Rabi'a ne.
Amma sai ya nuna Mata ayi hakuri tunda tana ganin consultant na Gynicology a gani
idan ba wani cigaba sai ayi na hausan.
A Kuma ciki shekarar ne Alhaji Jafar ya koma Abuja da aiki inda arzikinsa ya Kara
bunkasa gashi Allah yayi shi Mai sakakken hannu bashi da rowa ko kadan, in dai Yana
gari to kofar gidansa Cike take da jama'a, sai Suma mutane suna tausaya Masa akan
rashin haihuwa ga dukiyar dai Kama hankadota ake Amma ba magaji.
Ana haka Allah ya kawo ibtila'in ambaliyar ruwa a Adamawa state yankin MUBI.
Lokacin da gwamnati tarayya zata tura masu zuwa jaje sai sunan Alhaji Jafar ya
shigo cikin tawagar vice president.
Sun jajje guraren da b'arnar ta afku anyi rubuce rubuce sosai da Alkawarin ka na
gwamnatin tarayya sanan an bada kayan agaji ga wadanda iftila'in ya shafa a
hanyarsu ta komawa ne Alhaji Jafar suna tattaunawa da Ardon filanin Yana Karayi
Masa bayanin abinda ya faru.
Suka jiyo maganar mace daga bayansu lokacin ayarin sun danyi nisa dasu, da sauri
Ardon ya juya Yama fadin "ho! 'yar nema Saida Kika biyoni Nan ko ma'u?"
Dariya tayi tana kare fuskarta da wani littafin Mai Dan fadi dake hannunta cikin
shiga take ta Kamala Riga da siket na lace brown sai takalman ta da jaka da
mayafinta farare.
Har kasa ta tsuguna tana gaishe da Baffan nata kafin ta Dan kalli gurin da Alhaji
Jafar yake ta gaishe shi.
Baffan nata ta mikawa littafin hannunta tana fadar "Baffa ga project din nawa komai
ya kammala".
Baki sake Alhaji Jafar ke kallonsu wannan 'yar yarinyar har ta Gama karatu ake nufi
ko me"

❤️
❤️
AUREN HUCE HAUSHIN
❤️
❤️

WRITTEN
BY
MAMAN FATIMAH

PAGE NINE🔷(9)

____Akwatuna ne na garari masu tsadedden kyau har set biyu aka shigo dasu, sai wasu
irin manyan jakunkuna guda uku, guda Zilai ta dinga gud tana fadin "wani kaya sai
amale wane jaki. Allah ya Kara daukaki Fatima ya Dora ki akan makiyanki lallai
girma sai dan girma kaga wadda ta gaji arziki gaba da baya"
Inna maimuna ce ta jimko kudi ta dankawa zilai tana fadin "na fanshi jikata tunda
kin koma roko".
Dariya tayi tana fadin "wallahi Inna Dana iya kirarin da yafi wannan da nayi Mata.
Uwar dakina murucin kan dutse ce Bata fito ba Saida ta shirya, yakuwar akan
kabarice bakin cikin 'yan taushe, bikin cikinka sauro yau ga xanzaro a bene" .
Ta Kara kwarara wata gudar.
Da sauri Mama ma tazo ta dankawa zilai kudi tana fadin yau ai ranar farin ciki ce
maza bude Mana muga karamar Arziki"
Tunda aka Fara shigo da kayan Zahra tayi dakinsu tabar su Sajidar anan.Hameeda da
zilai ne suke fama bude kayan suna santinsu komai na ciki Mai kyau ne ba karya duk
wadda ta hado kayan 'yar gayu ce ta gani kasheni komai na ciki classic ne.
Saida suka bude kowa ne akwatin duka Sha biyun.
Ba abinda Inna maimuna ke maimatawa sai Masha Allah,Allah ya kade fitina yasa gurin
zamane Allah ya hada arzikinsau.
Duk bidirin da ake Salma na tsaye Bata taba ko tsinke a ciki ba sai cika take tana
batsewa Kamar anyi Mata dole sai ta zaune a gurin.
Su Sajida da Mujiba da Hameeda ne suka shigar da kayan falon Ammah.
Sai da suka jerasu sannan Hameeda ta nufi dakin Mama su Kuma su Mujiba suka nufi
gurin Zahra.
Wata uwar harara Salma da dokawa Hameeda tafin tayi dogon tsaki tana fadin "Allah
wadaran naka ya lalace yanzu ke ko kishin Kai Baki dashi Kika bige gurin jidar
kayan kanwar bayanki kina wani washe Baki ke game kirki". Baki Hameedar ta murguda
Mata tayi gaba tana cewa "Ina ruwanki Aunty Salma danke bakya ra'ayinta dole Nima
sai nabi naki ra'ayi kowa yayi ta kansa kawai ni bana ara na yafa abinda Babu
ruwana ba.
Mama ce ta fito daga bed room dinta fuskarta a hade da waya a hannunta kallon
Hameedar tayi "to rasa kunya b'eran tanka Dan ta fada Miki gaskiya Zaki kare Mata
tana din rashin mutunci cewa nake koni Dana tsuguna na haifeki ban Isa kizo inda
nake ba Saida Kika dangana da gurin kanwar uwarki".
Baki Hameedar ta zumbura tayi gaba tana magana kasa -kasa.
"Ai Daman za'a rina tunda Naga kin biyo Mama daki, wallahi mutum ya kiyayi gulma da
munafurci in dai yansla son yaga ci gaba a rayuwarsa"
Tana Gama fada ta shige uwar daki.
A waya Ammqh ta Kira Aunty Hasana ta fada Mata an kawo lefen Zahra.
Lokacin da tazo taga kayan ta kadu da gasken gaske, Amma dai Bata furta komai ba
kada Ammah taga Kamar Bata son auren ne ko wani Abu.
Sai bayan sallar magariba Mujiba tayiwa su Ammah sallama Sajida ta rakata ita
Haidar din Aunty Hasana.
Tun Zahra na tsammanin ganin Hameeda har ta hakura saboda dare ya fara so sai Dan
Sajida har tayi barci, sai tayi Kamar ta kirata a waya saita fasa, da taga zaman
yayi yawa sai ta dauko alqur'ani ta Fara karatu har Saida daya ta gota sannan tayi
addu'a ta shafa.
Kwantawa tayi rigingine tana tariyo rayuwartan ta baya komai ya ringa dawo Mata
Kamar lokacin yake faruwa
************_
_
TUSHEN LABARIN

AZARE KATAGUM L.G.A


BAUCHI STATE
UNGUWAR FAMFON SHANU.
Yarinya ce 'yar kimanin sheKara goma Sha biyu haka, kyakykyawar gaske fara irin
farin Nan Mai hade da Kamar golden yellow , idanunta dara-dara farare tas sai
gashin kanta bakirkirin har gadon bayanta hancinta irin dogon Nan ne har baka
bakinta Dan karami Mai dauke da 'yan jaja-jaja pink-pink din lebe, bazaka kirata
doguwa sosai ba irin tsaka tsakiyar nan, jikin lublub Kamar Mai rayuwa a kasanshen
sanyi komai nata Mai kyau ne Wanda idan ka kalleta saika Kara kallonta Dan Allah
s.w.a yayi Mata sura Mai kyau na a gani a Kara kalla. Da sallama ta shigo cikin
gida tana fadar "wash Allah Ammah wallahi na gaji wadannan littatafan sunyi nauyi
da yawa inaga sai dai na kwafo time table kullum na ringa zuwa da Wanda zamuyi
amfani dasu kawai". Ta fada tana kokarin Ciro jikar daga bayanta, dariya Ammah tayi
tana fadin "ke dai anyi raguwa wallahi zahra ke Sam bakya da juriya jakar da Zaki
Goya zuwa mota ma neman gagararki tajeyi".
Kwantawa tayi saman kujera tana fadin "Allah da nauyi dauki fa kiji".
Sulaiman ne ya shigo shima da tasa jakar a kafada Yana dariya.
"Kai Kuma dariyar me kake?"
Ammah ta tambaye shi.
Zahra ya nuna Yana cigaba da dariya. Baki ta zumbura tana dira kafa tana fadar
"Allaha Ammah ki rabani da Ya sulaiman Kinga tundazu yake min dariya Kuma nace ya
tayani daukar jikar ya Kiya".
"Wai Kai meye haka kazo kana ta dariya Kamar wani sabon kamu".
Jakarsa ya jefa kusa data Zahra kafin ya zauna Yana ba Ammah labari.
"Wato Ammah muna hanyar dawowa ne man motar ya Kare tunanin Malam Bala harya kawo
mu gida man Bai Kare ba saboda yace ya biya gidan man yaga da layi idan yace zebi
layin zamu Dade muna jiransa shine kawai ya taho, to muna zuwa wurin gidan sarki
kawai man motar Nan ya Kare shine fa muka tako a kafa, ita Kuma gwanar iya son jiki
ta wani shagwabe mini Wai na daukar Mata jaka na hada da tawa Kamar wani jaki,
shine Dan tsabar rainin hankali Wai to na dauka zata karbi kudin gurin Abba ta
biyani Kamar wani Dan dako".
Tsaki Ammah tayi tana hararar Sulaiman din "wannan shine abin dariyar Kuma wallahi
kayi girman kwabo da meye amfanin hada babba da yaron ba saboda taimakon ba".
"A'a Ammah duka da wata biyar fa na girme mata, to Ina wani girma sa'anni muke ba
gashi ajinmu daya ba da dai su Ya Sadiq ne su Aunty Janah, kuma fa duk su Hameeda
kowa fa ya dauko tasa sai itace tafi kowa son jika za'a daukar Mata wa zata yiwa
karatun ba kanta ba".
Ya fada Yana cire safarsa.
Fita Ammah tayi, ita Kuma Zahra ta shige bedroom din Ammah ba Wanda ya Kara bi
takan sulaiman.wanka ta shiga tayi kafin taci abinci saboda Bata son ta makara a
islamiyya Sam Bata son abinda ze taba lafiyar jikinta tunda a makarantar bokon suke
sallar Azahar.
Lokacin data fito tana sanye da uniform din islamiyya da Jakarta tana kokarin shiga
dakin Mama ta biya Hameeda ne taga Hameedar da wani Kaya a wata leda babba ta fito
tana zumburar Baki.
"Ya Naga Baki shirya ba ko bazaki makarantar ba? Kinga fa yau zamu bada hadda".
Mama ce ta fito daga dakin tana hararar Zahra "to uwar kinibibi bazatan ba ki Kama
hanya ki wuce, ko zata ai bazaku tafi tare ba ana gqninki waye ze kalleta na nuna
Miki bana son kina shige Mata amman kin kasa ganewa, Haba yarinya sai kwawa"
Duk wanna maganar da Mama takeyi a hankali take fada Banda Zahrar da Hameedar ba
Mai jin abinda take fada duk da Ammah na kofar kitchen dinsu Wanda yake kusa da
bangaren na Mama.
Daki Mama ta nunawa Hameeda ta koma yayin da Zahra ta nufi Ammah tana fadin "Ammah
na tafi"
"To Allah ya bada sa'a a maida hankali ki biyawa Mujiba ki tafi".
"To" ta amsa ta nufi waje da sauri.
Saida dama Ammah tana ankare da Mama Sam Bata son Zahra na mu'amala da Hameeda
kwata-kwata sai Kuma Allah ya hada wata irin kauna tsakanin yaran salma ce Sam basa
jituwa da Zahra da ita wata sakarai ce da zahra ko ruwa Mai dadi Salma bazata Bari
Tasha a gidan ba, motsi ba motsi ba sai ta Fara fadin ai dai Nan ba gidanki bane ke
'yar riko ce.
Lokacin da Ammah taji maganar a bakin yarinyar tayi mamaki sosai Dan a lokacin
wayonta Bai Kai ta iya banbance tsakanin Dan gida na ruko.
Da Ammah ta tsareta ta fada Mata wayace Zahra ba 'yar gidan bace sai tace " Mama ce
ta fada tace min na duba Mana Naga ko kalar jiki mu ba iri daya bace mu daina
tafiya ma da ita, Wai ta fimu kyau idan muna binta idan muka girma baza'a sure mu
ba".
Kan Salma Ammah ta dafa tana fadin "itama 'yar uwarku ce kuyi zumunci da ita kinji"
kai ta gyada alamar to.
Abin ya jima Yana baiwa Ammah mamaki Bata zaci haka a gurin mamar ba, tunda a
zahiri ba komai a tsakaninsu sai mutunta juna duk da tasan sha'anin kishi ta ciki
na ciki ne ta baka na baka.
Sai kusan magariba su zahra suka shigo hannunsu na sarkafe da juna ita da Hameedar,
daga gurin Aiken ta wuce makarantar Amma Tasha bulalar makara.
Bayan sun Gama cin abincin dare ne suna hira a dakin Ammah Hameeda ta shigo ta
gaishe da Ammah ta zauna sukaci gaba da hira lokacin Ammar tana dakin Abbansu ta
Kai Masa abinci.
Lokacin data shigo dakin ya kacame sunata musu akan wani aiki da akayi musu yau a
makaranta su matan suna ga yanda za'ayi shi Kuma Sulaiman Yana fadar ga yanda
za'ayi, Ammar ce ta zauna tana fadin su kawo ta gani maths ne, Kuma duk hanyar da
akabi za'a kaiga samun amsar Dan haka tace kowa yayi nasa yanda ya fashimta.
Har ta shiga bedroom dinta ta fito tana fadin "Na manta Abbanku yace na fada muku
ranar Saturday zakiyi jarabawar share fagen shiga karamar secondary school ta
kwamnatin tarayya, yace kuyi karatu duk Wanda baici ba baze saimasa ba Saida yaci
gaba a makarantar da yake".
Murna suka farayi da gudu Hameeda ta nufi dakinsu Dan ta fadawa Mama.

******Alhaji Jafar Mai yadi haifaffan garin Azare ne ta jihar Bauch a unguwar
fanfon shanu, su hudu ne iyayensu suka Haifa uku maza sai autarsu daya mace amman
su biyu suka rayu biyu tun suna Yara suka rasu, sun taso shi da kanwarsa Amina a
hannun Babarsu Hajiya Fatima wadda ake kiranta da Nanna, kasancewar Babansu Malam
Ibrahim Wanda ake Masa laqabi khalilu Allah yayi masa rasuwa tun Yana aji day na
babbar sakandire Amina Kuma tana aji shida na primary.
Sun Sha wahala kasancewar mahaifan su ba Mai karfi bane Bai bar musu wani Abu Mai
yawa ba daga gidan da suke cikin sai konaki biyu, tunda Jafar ya Gama babbar
sakandire yake zaune a gida saidai dinkin hula da aikin hannu na riguna kusan dashi
yake rike Nanna da Amina said Kuma 'yan kulle-kullen kayan Miya daaya kafawa Nanna
jarinsu.
A hankali Jafar yana Tara kudinsa lokacin daya da yaga kudin sun danyi auki ya nemi
Shawarar Nanna akan yana son ya Fara sayar da Yadiddika na maza, tayi murna sosai
ta dinga saka Masa albarka.
Cikin ikon Allah ya Fara kasuwar da kafar dama Nan da Nan abun ya Fara bunkasa da
taimakon wani uban gida da Allah ya hada jininsu yake bashi Kaya akan farashi Mai
sauki har takai ga Fara tura shi aba Yana sawo Masa Kaya a hankali ya bashi aron
kudi masu Dan yawa yace shima ya hada da nasa jarin ya sawo nasa kayan zeyi Masa
kokarin shago kafin ya dawo.
Nan da Nan al'amura suka kankama ba'a rufe shekara ba arzikinsau ya Fara habaka da
taimakon Ubangidansa ya samu Yara masu amana ya zuba a shagon shi Kuma ya shiga
cuku- cukun nema admission Nan University ta Bauchi cikin ikon Allah ya samu course
din da ya nema Agricultural science.
Cikin ikon Allah karatu ya kankama, yayin da a gefe ga kasuwanci Yana ta habaka.
Lokacin Yana shiga level 300 lokaci Amina ta kammala secondary dinta manema sukayi
Mata chaaaa, Amma an kada an raya ta fitar da gwani ta Kiya Wai duk Bata sonsu.
Haha aka tattara aka kyaleta Jafar yaso ya nemar Mata gurbin karatun N.C.E Amma
Nanna tayi tsalle ta dire ba za'a wannan aiki da ita ba, haka suka zauna har kusan
shekara Amina ita ba karatun ba ba auren ba.
Wata ranar juma'a lokacin su Jafar sunzo hutun karshen first semester na level 400,
Nanna ta aiki Amina kasuwa gurin Jafar ta karbo Mata wasu kudi uzurinsu ya taso
Mata na gaggawa.
Lokacin da taje baya shogon nasa Yana shagon Ubangidansa Alhaji Dauda, can ta nufa
tunda tasan shagon nasa.
Suna ciki Hira da bakon Alhaji Dauda kawai ya hango Amina ta nufo shagon tana
gaishe da Alhajin daya fita a lokacin, kafin ta karaso har taso ya nufo ta Yana
fadin"lafiya Amina? Daga Ina kike?"
Dariya tayi kyawawan hakoranta jerarru farare tas suka bayyana tana fadin "kai Yaya
ba komai fa Nanna ce ta Aiko ni".
Fita sukayi ta fada Masa sakon sukaje shago ya Bata ai Bari ta hau abin Hawa ba ya
dauketa a mashin dinsa suka tafi gida.
Da dare Yana zaune a inda suke Hira yaga motar Alhaji Dauda ta tsaya a kofar
gidansu da sauri ya tashi ya nufi inda yayi parking sai yaga harda bakon Alhajin
Zakariyya suke tare, sun gaisa sosai kafin Alhaji Daudan ya fada Masa Amininsa Kuma
Dan uwansa ne yaga Amina Yana so shine nace yazo muji da zafi -zafi akan bugi
karfe.
Jafar yaji Dadi sosai zaifi kowa murna idan hakan ta kasance Dan ya yaba sosai da
hankalinsa sosai.
Cikin gidan Jafar ya shiga ba jimawa ya fito Yana musu iso ciki sun gaisa da Nanna
Alhaji Dauda ne yayiwa Nanna bayanin koma itama irin amsar Jafar ta fada idan tana
so ba matsala ba inda aure baya Kai mace Nasarawa batayi nisa ba.
Cikin ikon Allah kuwa Amina taji Alhaji Zakariyya ya kwanta mata a rai Kuma zata
iya aurensa duk da fada Mata Yana da Mata harda Yara biyu.
A cikin wata biyu akayi bikin Amina da Alhaji zakariyyan, Jafar yayi Mata komai da
uba yake aka kaita can Nasarawa state cikin garin Akwanga.
Wannan kenan.
Haka Jafar yaci gaba da karatunsa har ya Gama ya dawo gida Yana jiran shiga camp.
Lokacin da saki post na tafiya service sunan Jafar ya Fado a cikin masu zuwa Jos
yayi murna sosai ko banza Yana jiyo kamshin gida tunda suna makotan jahohi.
Bayan gama zaman camp wata makarantar 'yan Mata jeka ka dawo aka Kai Jafar, Baiyi
wata biyu ba Allah ya hada shi da wata yarinya Rabi'a yaji yarinyar ta kwanta Masa
tana Kuma da irin Qualities din da yake fatan Samu a gurin matarsa.
Zuwa lokacin gama service dinsu har magana tayi karfi inda iyaye suka shiga.
Wani gida Jafar ya saya kusa da gidansu ya gyara' ba'a dauki lokaci ba akayi
bikinsa da Rabi'a suka tare a gidansu. Duk wata kulawarsa da soyayya ya tattara ya
baiwa Rabi'a ba abinda ta nema ta rasa sai abinda baza'a rasa ba. Rabi'a irin matan
Nan ne masu kissa kafin wani lokaci ta kanainaye zuciyar Nanna.
Kwanci tashi ba wahala a gurin Allah aurensu ya shekara Amma kalubaken da suka Fara
fuskanta na Rashn zaman ciki a jikin Rabi'a kusan barinta uku. Ana haka Jafar ya
samu aiki da ma'aikatar gona ta jihar Bauchi BARDA.
Cikin kankanin lokaci kofofin wadata suka budewa Jafar kafin shekara biyu ya gina
gida Mai kyau sunje makka shida Nanna.
Nan da Nan likafa tayi gaba Amma dai matsalar su na Nan ta rashin haihuwa.
Yayin da abin ma ya Fara damun Nanna har ta gaji tayi Masa magana akan ko maganin
hausa za'a fata nemawa Rabi'a ne.
Amma sai ya nuna Mata ayi hakuri tunda tana ganin consultant na Gynicology a gani
idan ba wani cigaba sai ayi na hausan.
A Kuma ciki shekarar ne Alhaji Jafar ya koma Abuja da aiki inda arzikinsa ya Kara
bunkasa gashi Allah yayi shi Mai sakakken hannu bashi da rowa ko kadan, in dai Yana
gari to kofar gidansa Cike take da jama'a, sai Suma mutane suna tausaya Masa akan
rashin haihuwa ga dukiyar dai Kama hankadota ake Amma ba magaji.
Ana haka Allah ya kawo ibtila'in ambaliyar ruwa a Adamawa state yankin MUBI.
Lokacin da gwamnati tarayya zata tura masu zuwa jaje sai sunan Alhaji Jafar ya
shigo cikin tawagar vice president.
Sun jajje guraren da b'arnar ta afku anyi rubuce rubuce sosai da Alkawarin ka na
gwamnatin tarayya sanan an bada kayan agaji ga wadanda iftila'in ya shafa a
hanyarsu ta komawa ne Alhaji Jafar suna tattaunawa da Ardon filanin Yana Karayi
Masa bayanin abinda ya faru.
Suka jiyo maganar mace daga bayansu lokacin ayarin sun danyi nisa dasu, da sauri
Ardon ya juya Yama fadin "ho! 'yar nema Saida Kika biyoni Nan ko ma'u?"
Dariya tayi tana kare fuskarta da wani littafin Mai Dan fadi dake hannunta cikin
shiga take ta Kamala Riga da siket na lace brown sai takalman ta da jaka da
mayafinta farare.
Har kasa ta tsuguna tana gaishe da Baffan nata kafin ta Dan kalli gurin da Alhaji
Jafar yake ta gaishe shi.
Baffan nata ta mikawa littafin hannunta tana fadar "Baffa ga project din nawa komai
ya kammala".
Baki sake Alhaji Jafar ke kallonsu wannan 'yar yarinyar har ta Gama karatu ake nufi
ko me"

❤️️
AUREN HUCE HAUSHIN
❤️
❤️

🔷PEGE TEN🔷
Story
&
Written
By
MAMAN FATIMAH

******Jujjuya littafin project din Ardo yayi, sai Kuma ya mikawa Alhaji Jafar Yana
fadin "Duba ka gani Yallabai ni tunda ba ganewa zanyi ba,naji Dadi da Allah yasa
aka Gama wannan karatun ba domin na saka auduga na toshe kunnuwa naba da ba'ayi
karatun Nan ba, tunda Wanda yaso auren nata yace in dai zatayi karatun Nan shi ya
fasa, shi Kuma Dan uwanta na wajen kanena yace karatu Babu gashi tunda tana ganewa
Kuma tana so, kaga yanzu duk gurin nan namu ita me yiwa mutane Allura".
Kallonta Alhaji Jafar ya karayi,sannan ya kalli Ardon Yana fadin.
"Yaushe ta Fara karatun ne na ganta karama amma har ta hada diploma?"
Gyara tsayuwa Ardon yayi Yana fadin "wallahi am tun tana aji hudu na furamare Dan
uwanta ta kaita aji daya na sakandire tunda yayi wani zuwa suka zauna da kannen
nasa yaga tana da kokari shine yace Mata idan ta Gama makarantar tana son taci gaba
da karatu, shine tace Masa tana son ta Zama malamar asibiti, to tunda sukayi haka
ya kudurci aniyar tsayawa akan karatunta shi yasa da akayi Mata chaaaa akan maganar
aure yace Bai Hana ayi maganar aure ba. Amma ya Dora sharadin saidai idan mijin ze
barta tayi karatu abinda ya gagara kenan aka fasa Amma duk yan uwanta anyi musu".
"Masha Allah. Allah ya Sanya Albarka, haka ake so a rinka barin Yara Mata suna
karatu barin ma na bangaren lafiyar da malaman makaranta, yanzu ba cewa kayi ita ke
yiwa mutane allura ba da sauran abubuwa? To da batayi karatun ba da basai an tafi
wai gurin an nema ba? Ba komai in Sha Allah zatayi auren ta Kamar kowa".
Ardo ya amsa da "Allahumma Amin".
Ma'un Alhajin ya kalla "Asma'u kin amince na tafi da project din naki na duba a
hankali in yasa said dawo Miki dashi".
Kai ta gyada alamar Eh.
Sunyi sallama da Ardo tawagarsu suka wuce zuwa Yola inda zasu bi jirgi zuwa Abuja.
Wannan shine silar haduwar Alhaji Jafar da Ammah, ya koma maida project da Kuma
kafa gwanatinsa cikin ikon Allah suka yarjewa juna.
Lokacin da magana tayi karfi Rabi'a taso tada hankalinta saida Nanna ta taushe ta
da kalamai masu kwantar da hankali.
Cikin kankanin lokaci akayi bikinsu. Amarya ta tare cikin ikon Allah zaman Rabi'a
da Asma'u ya kasance Zama Mai tsabta.
Wata uku da auren Asma'u ciki ya bullo duk masoyin Alhaji Jafar ya Taya shi murna
sosai a lokacin ne Alhaji Jafar ya biyawa Rabi'a makka kusan abinda ya kwantar Mata
da hankali kenan Dan ya fada Mata idan take tayi addu'a sosai akan matsalar ta.
A haka rayuwa ta dunga gurguwa har cikin ya Isa haihuwa Ardo dasu Inna maimuna sun
so Ma'un to koma gida zaman haihuwa Amma Nanna ta Hana tace meye amfanin ta ita in
dai sai Asma'u ta koma gida.
Cikin ikon Allah a wani dare nakuda ta tasowa Asma'u lokacin Alhajin Yana nan, Nan
da Nan suka nufi asibiti wurin karfe biyu da rabi Amma kafin hudu Allah ya dauketa
lafiya ta haifi takwaye mace da namiji.
Murna gurin wannan iyalin ba magana ranar suna yaran aka bar musu sunan su sai dai
su Hassan da Hasana aka daka musu.
Kullum yaran suna tsakanin Rabi'a da Asma'u suka rainon 'ya'yansu. Lokacin da aka
yayesu a lokacin Allah ya baiwa Rabi'a ciki itama ba'ayi wata biyu ba Asma'u ma ta
Fara laulayi, cikin ikon Allah cikin Rabi'a ya zauna kusan lokaci daya suka haihu
Rabi'a haifi Hamza yayin da Asma'u ta haifi Abdul Hakeem.
Bayan haihwar Hamza Rabi'a Bata Kara haihuwa ba Saida Asma'u tayi maza biyu sanan
Rabi'a ta haifi mace Murjanatu, bayan Murjanatu Rabi'a ta Kara haihuwar Salma sai
auta Hameeda ita Kuma Asma'u ta haifi Sulaiman sai auta Musaddiq, zuwa lokacin
sunansu ya bace yayin da ake gadawa Hajiya Rabi'a Mama wasu na waje suce Hajiya
Mama, Hajiya Asma'u Kuma Ammah.

WACECE FATIMAH ZAHRA?


'ya daya tilo ga kanin Ammah shaqiqi Muhammad Sani. Mahaifiyar Zahra Najwa
Balarabiyar Jordan ce sun hadu da Muhammad Sani ne lokacin da yaje karatu kasar da
farko mutunci suke da Najwa sai daga baya ya juye ya Zama soyayya har Allah ya
nufesu da aure da taimakon wani malaminsu Dan kano Dan kusan ta bagarensa su Ardo
wanda suke Kira Baffa ya Sani ya Kuma amince da Malam Muhammad Kabir ya Zama
waliyyin Muhammad Sani a can.
Lokacin da Muhammad Sani ya Gama karatu ya zauna a can yayi aiki kusan shekara biyu
daga baya ya tattaro nasu ya nasu suka dawo Nigeria, lokacin Najwa nada cikin
Zahra wata bakwai a lokacin Kuma Ammah na goyon Sulaiman Mama na goyon Hameeda.
A Jimeta Muhammad Sani ya sayi gida saidai suje Mubi kawai suga iyayensa,ba dadewa
Najwa ta haifi 'yarta Zahra wadda taci sunan mutum biyu mahaifiyar Najwa da
Mahaifiyar su Ammah.
Haihuwar Zahra ba dadewa Muhammad sani ya Sami aiki a Abuja karkashi minstary of
internal affairs da taimakon Alhaji Jafar.
Zahra nada wata biyar wani cikin ya bullo a jikin Najwa Mai wata irin masifar
laulayi, Wanda ya tilasta Ammah ta dauke Zahra daga bakin nono.
Lokacin da komai da dai dai ta a gurin aikin nasa ya dauki Najwa suka koma Abuja.
Saida watan haihuwarta ya Kama ya kaita Mubi shi Kuma ya koma Abuja.
Lokacin data haihuwa iyayenta sunzo Nigeria da kanwarta Nawwara a Karon na biyu
Mahaifiyar ta taso tafiya da Zahra Ammah ta dunga magiyar abar Mata ita harda
kukanta.
Lokacin da suka Gama wanka Muhammad sani yazo ya tafi dasu tafiyar da har abada
Basu dawo ba a hanya sukayi hadari sun bar Jos Basu karasa Abuja ba.
Yan uwa da iyaye sun shiga cikin tashin hankali marar misaltuwa Ammah tayi Kika
Kamar ba gobe,ta rasa Dan uwanta shakiki, ba karamin Kai ruwa Rana akayi ba kafin
Ummee kakar Zahra ta hakura ta barwa Ammah Zahrar.
Tunda daga lokacin Ammah ke baiwa Zahra wata irin kulawa ta musamman sai Kuma shima
Mai gidan ya kwallafa ransa akan soyayyar yarinyar abinda ya haddasa tsana Mai
tsanani tsakanin Mama da zahra inda ita mamar ke ganin Kamar nema ne yasa Alhaji ke
kaunar Zahra, tana ganin idan Dan tana 'ya mace ne karama ai itama tana da nata
kananan 'ya'yan mata Amma baya nuna kulawa akasu Kamar Zahra ko Dan tafisu kyaune
tunda Babu inda ta baro uwarta.
Wannan kenan.

Ranar da za'ayi jarabawar share fagen shiga karamar secondary ta gwamnatin tarayya
tun sassafe zu Zahra suka shirya ita da Sulaiman da Hameeda da Salma duk da Salma
ta girmesu Amma yawan yi Mata repeating yasa suka taddo ta.
Har sun shiga mota Bala direba na niyyar shiga Zahra ta bude ta fito da sauri ta
nufi cikin gida Sulaiman Yana kiranta tayi banza dashi ta shige da gudu ta karasa
dakin Ammah tana fadin "Ammah na manta kayana da Ya Hassan ya kawo min har zamu
tafi na tuna".
Daga toilet Ammar ta fito ta nufi bedside locker ta janyo ta mikowa Zahra ledar
tare da fadar "Maza kada ku makara mana".
Kai Zahra ta gyada kafin tace "Ammah ki kara yi Mana addu'a Dan Allah Ina son naci
jarabawar saboda Abbana yace idan naci makarantar zemin kyautar wani Abu"
"To naji maza Allah ya bada sa'a"
A kofa suka hadu da Sulaiman ya biyo ta tana fadin "Na rantsa da Allah zamu tafi mu
barki ba Dan Abba ya fito ba da wallahi sai dai ki fito kiga bama gidan".
Kafin ya saki labulen ya juya Zahra ta Kai kofar da zata kaika compound din gidan.
Masha Allah anyi jarabawa an Gama sai jiran sakamako.
A haka sukaci Baga da zuwa makaranta har suka Zama common enterence a matakin jaha.
Lokacin da suka dawo zaman gida lokacin ne Alhaji Jafar da kansa ya yiwa Zahra
passport da visa Saida ya Gama komai sannan ya fadawa su Ammah da Mama. Godiya
Ammah ta shiga jerawa Mai gidan nasu,yayin da Mama tayi shiru Kamar bazatayi magana
ba sai Kuma tace "yanzu Yallabai da kanka zaka rakata ai da Koda Hasana ko Hassan
ka hadasu zasu kaita ko Kuma a fadawa cen kakanninta su turo a tafi da ita ai cacar
kudin Kamar yayi yawa".
Daga Ammah har Alhaji Jafar din kallon Mamar suke ita dai Ammah shiru tayi yayin da
Alhajin yace.
Saboda ban San darajar 'ya'ya ba zan hada Yara a tafiyar uwa duniya daga Nan har
Jordan na kwanta a gida hanakli kwance ko?"
Kai ta gaigice tare da fadin "gani makudan kudi za'a kashe".
Wani kallo yayi Mata "kada ki kawo b'araka Rabi'a duk yaran dake gabana daya na
daukesu yada zan yiwa abinda na Haifa haka zan yiwa marainiyar Allah. Da Kuma kike
maganar cacar kudi idan zan jera shekara Ina Kai zahra Jordan kullum ba abinda ze
girgaiza a cikin abinda na mallaka".
Ku tashi kuje.
Lokacin da zasu tafi anyi Mata tsara sosai Dan Nanna ma kilishi tasa aka yi Mai
yawa na tsaraba.
Har kano su Ammah da yara sukayi musu rakiya.
Lokacin da sukaje Jordan din ba karamar murna kakanninta zukayi ba Dan Babu zato
suka gansu, sun Kuma Kara yabawa da cika Alkawarin Alhaji Jafar Dan da kansa yayi
musu Alkawarin ze kawo musu Zahra Dan ko a waya Bai fada musu zuwansu ba,sai
address dai daya taba tambaya can wani lokaci.
A ranar Zahra taga zallar soyayya a gurin dangin Najwa Dan gidan cika yayi da 'yan
uwa aka dasa sabon kukan rashin Najwar da kyar Abbie da Abbanta suka dinga Basu
hakuri Dan ma Alhaji Jafar ba larabcin yakeji sosai ba saidai Wanda suke Jin
turanci suka ringa magana dasu.
Lokacin da Alhaji Jafar din ze tafi masukin daya Kama a hotel Abbie hanawa yayi duk
yanda yaso zillewa kin yarda yayi dole ya amince aka sauke shi a wani part dake
kusa da nasa Ummee din, Dan ba karya dukiya dai Kam akwaita Dan shi kanshi Alhajin
yayi mamakin yanda ya riskesu Bai taba kawo haka suke ba lallai yasan hadin Allah
ne kawai da suka bawa Muhammad sani auren 'yarsu Dan tazarar Mai nisa ce a tsakanin
su.
Kwanan Alhaji Jafar bakwai ya wuce Umara yayin da Ummee tayi Masa Alkawarin zasu
hadu a Saudiyyar tunda zata kawo Zahrar Nan gurin iyayenta da 'yan uwa su ganta a
cikin garin Madinatul Munawwara.
Satinsa daya da zuwa Suma su Zahrar sukazo Saudiyyar ita da Ummeen da Aunty
Nawwara.
A Nan ma Saudiyyar Zahra taga gata iya gata Dan kowa Nan Nan yake da ita, Dan
kanwar Ummee Hanifa sosai ta kafe sai dai a bar Mata Zahra ta tafi da ita Istanbul
inda take aure Wai Bata yarda da zaman Nigeria ba.
Ankai ruwa Rana da ita kafin ta hakura Dan da gaske Alhaji Jafar ya bude Mata aiki
Dan cewa yayi idan irin haka za'a ringa yi bazai Kara bawo musu ita ba saidai duk
Mai son ganinta taje ya ganota Kamar yanda Ummee keyi, hakuri aka ringa bashi.
Saida aka Kai Zahra makka suyi kayi umara sannan suka fara Shirin baro kasar.l
Sayyaya dai Zahra ta shata Dan wasu kayan sai a awon cargo akayo musu su.
Sarkar gwal da warwaro zobe kuwa kirar Saudiyya da Dubai zuwa kirar Bahrain sun Kai
kala goma duk dai dai size din ta sai na Ammah biyu na Hasana ma biyu shi kanshi
Alhajin anyone mass goma Sha Tara ta Arziki.
Ranar da zasu dawo Zahra Tasha kuka haka kakarta Ummee,har jidda sukayo musu rakiya
Basu suka tafi ba sai da jirgin su Zahra ya tashi a sararin subahanahu wata'ala.
Saukar safe sukayi anan suka samu Bala direban Alhaji Dan Bai fadawa kowa sun taho
ba sai Balan kawai, sau da yawa idan ya fada gashi Nan a hanya hankalin Nanna baya
kwanciya har sai ya iso.
Lokacin da suka shigo harabar gidan suna tsayawa Zahra to garzaya cikin gida tana
fadin "Ammah!!! mun dawo".
Da gudu Hameeda ta fito daga part dinsu, rungume juna sukayi suna ta tsallen murna
Sai jikin zahra Hameedar ke shafawa gani take kamar canza Mata Zahrar akayi.
Da sauri Ammah ta fito tana "fadin wa nake gani ne haka Kamar bakin saudiyya zuwa
ba notice?"
Alhajin ne ya Bata amsa.
"Surprised din ki mukayi ko Zahra na?.
Kai ta gyada masa.
Kayansu ne su Bala da Mai gadi suka Fara shigowa dasu kafin Alhajin ya nufi part
dinsa na cikin gidan yayin da Ammah ta rufa Masa baya.

Har yayi wanka ya shirya Mama Bata shigo ba, har ya tambayar Ammah yayi Ina
Rabi'a ? Tace Masa tana ciki watakila ko barci take.
Kusan kwana su Zahra sukayi tana baiwa Hameeda labarin abinda ta gani da inda
sukaje a Jordan da saudiyya, wurin karfe biyu Ammah ta tashi zatayi nafila ta jiyo
su suna Hira a dayan bed room dinta lokacin wuri biyu da rabi na dare, leko tace
su kwanta basu san dare yayi sosai ba.

Washe gari an baje tsarabar Zahra an baiwa kowa dai dai gwargwado.
Amman tsarabar Hameeda daban take Dan har sarka Saida ta baiwa Hameedar.
Basifi sati biyu da dawowa ba jarabarsu ta fito ta Federal inda Zahra ta samu
F.G.G.C KAZAURE yayin da Sulaiman ya samu F.G.C DAURA, Hameeda F.G.C AZARE. Salma
ce kawai bata samu ba a cikinsu.
Sunyi murna Kuma sunyi bakin cikin rashin samun makaranta daya duk an watsa su
Abban Kuma da ya Hassan sunce kowa ya tafi inda ya samu, ita Hameeda Bata da
damuwa tana gida, su Kuma duka 'ya'yan Ammah duk sun fita waje danma hanyarsu daya
sai an aje Zahra a karasa da Sulaiman.
Ranar da zasu tafi sun Sha kuka haka suka dauko hanya malam Bala da Ya Hassan ne
suka kaisu.
Lokacin da aka Kai Zahra an tashi daga aji, wasu Yara House master dinsu ya kira da
wata prefect yasa su Kai Zahra room din 'yan j.s one.
A cikin yaran da suka Taya Zahra daukar kayane wata yarinya tace Mata "sister kizo
ki zauna a kwana ta tunda ni daya ce saman gadona ba kowa".
Kai kawai zahra ta gyada Mata tana ta sauke ajiyar zuciya.
Ita ta taimkawa Zahra ta shirya komai a locker dinta, Saida ta Bari zahra ta HUCE
daga kukan da tsaha sannan tace Mata "ni sunana Sajida Musa ni 'yar kano ce unguwar
Gwammaja kefa ya sunanki?".
Nan Zahra ta fada Mata komai nata tun daga Nan suke tare har suka Zama aminai komai
nasu ya Zama daya banbanci su kawai Sajida na A Zahra na C.
Haka sukaci gaba da rayuwa a makarantar gasu Kuma Yara masu kwazo barin zahra ga
kyau ga ilimi Nan da Nan tayi suna a makarantar kafin hutu tayi popular sosai a
makarantar, idan kace 'yar larabawa kowa ya santa ba Kuma Dan Babu irin jiinsin
nata ba A'a farin jini ne daga Allah.
Lokacin da akayi hutu Zahra ba karamar murna tayi ba Kuma cikin ikon Allah da wuri
malam Bala yazo lokacin har ya dauko Sulaiman.
Bayan Azahar kadan suka shiga Azare sunyi murna sosai da ganin mutanen gida Dan
Sulaiman har da kuka, Nan su Hameeda suka saka gaba suna tsokana.
Haka suka cigaba da karatunsu cikin amincin Allah, lokacin da sukazo hutun third
term ne akayi auren Aunty Hasana aka kaita Jos, Ya Hassan Kuma Daman Yana karatunsa
a Rasha.
Kowa inda yake yacigaba da karatunsa Salmace Allah ya taikata ta samu shiga FGC
AZAREN itama a ss1.
A haka aka dunga juyawa har suka Gama secondary School dinsu suka dawo gida.
Dawowarsu ba dadewa Allah ya yiwa Nanna rasuwa rashin daya taba Abbansu sosai.
Dan ya Dade Yana fama da damuwa tunda a rayuwa da ita ya tashi baisan dadin uba
namiji ba itace komai nasa.
Ganin abin nasa Yana neman yayi yawa yasa Abokinsa bakon malamin daya sauka Nan
daura gidan Nanna da almajiransa dududu Bai zaifi sa'an Alhajin ba malam Bubar ya
dukufa yi Masa addu'a tare da saka Yara kanana suna Masa addu'a, cikin ikon Allah
sai komai ya daidaita.

Ranar wata laraba zahra ta shirya zata raka Hameeda duba Qawarta meenal gidan Dan
majalissarsu Mai wakiltar su majalissar Jaha, wani material ta saka Mai ruwan
sararin samaniya yayi matukar karbar jikinta haka dinki ma ya Dace da material din,
simple makeup tayi ta saka turarenta Amber oud new edition na kamfanin Al
haramaini.
Tunda ta fito Mama ke Mata wani irin kallo Wanda har saida ta rinqa Jin ta takura
kafin Hameedar ta fito.
A kasa suka taka suna Hira har sulaje gidan,sun Dan jima suna Hira da marara
lafiyar kasancewar breast lump ne aka cire Mata ba wani serious case bane.
Lokacin da zasu tafi suka Kara komawa gurin mamanta sukayi Mata sallama suna zaune
ne da a falonta kafin meenal din tayi Mata magana ta fito. Wani handsome guy ne ya
shigo falon da sallama ya Dan jefa car key dinsa sama, kana ganinsa kasan hutu ya
Kama jikinsa.
Ciki ya shigo lokacin da Suke amsa masa sallamarsa kujera two seaters ya zauna a
Kai wadda ke facing dinsu Hameedar.
Gaishe shi sukayi su Duke ya amsa Yana cewa "Hameeda daman kina Nan na Dade ban
ganki ba gaskiya Ina ga tun kafin na tafi Colombia fa".
Dan rausayar da Kai tayi tana fadar "wallahi Kam Ya Sahal an jima Kam kune dai
bakwa ganuwa Kuna uwa duniya kunyi shiru Kum barmu da zafin Kasarmu".
Ta fada tana dariya.
Dai dai lokacin mommyn su meenal din ta fito kallon Sahal tayi tana fadar Kai Kuma
haka mukayi da Kai?"
Kaisa ya Dan Sosa da key din hannunsa Yana fadi "Iam so sorry Mom kada ki damu
yanzu zanje na kawo Miki in Sha Allah."
Ya fada Yana mikewa da nufin tafiya Meenal tayi tsagal tana fadin "Dan Allah Ya
Sahal ka tafi dasu tunda cikin garin kayi.
Suka yiwa mommy sallama da godiya suka fito da leda Mai Dan girma a hannun Meenal
wadda mommyn ta Basu.
Har kofar gida ya kawosu suna tsayawa ya kalli Hameeda Yana fadar "Dan Allah ki
bani aron sister din take Mana Kona ten minutes ne Mana".
Dan murmushi tayi tana fadar.
"Ka Fara yiwa Abban mu magana dai haka Naga anayi"
Ita dai Zahra ciki ta wuce Dan Kamar a kan.kaya take duk ya takura Mata da wani
irin kallo har a cikin mota ma saita mirror yayi sitinta tunda Hameeda ce ta zauna
a seat din gaba tana Masa Hira Amman gaba daya hankalinsa yana kan Zahra.
Ita dai zahra Bata San yanda suka Kare ba taga dai Lokacin da Hameedar ta shigo ta
wuce dakin su.

Bayan kwana biyu da zuwa gidansu Meenal da yamma su zahra sun tafi islamiyya ne
baki sukazo gurin Alhaji Jafar, ya sansu farin sani daya kanin Dan majalissar su ne
dayan Kuma kanin Babansu.
Yayi mamakin ganinsu Saida suka gaisa ne suka bijiro da abinda ya kawo su na yiwa
yaron gurin Dan uwansu Sahal kidiba yaga yarinyar gurinsa Yana so. Shine mahaifansa
ya turosu ya gabatar da maganar Yana neman izininsa na Fara zuwa gurinta Shira.
Alhajin yaji Dadi sosai na yanda suka zo suka memi izininsa duk da Daman sharadinsa
kenan, ya Kuma nemi Jin wacece daga cikin yaran suka gada Masa zahra ce, nan ya
amince musu da addu'ar Allah ya hada kawunan su.
Tun daga lokacin Sahal ya Fara zuwa gurin Zahra cikin ikon Allah tayi na'am dashi
Basu Dade sosai ba sukayi wata irin shakuwa ta ban mamaki duk Wanda ya kwana ya
tashi a unguwar yasan irin soyayyar da sahal yakewa zahra kusan Kullum da yamma
Yana nan makale da ita, a haka har manya suka shiga maganar aka tsaida lokaci wata
shida inda zasu tafi Colombia inda yake hada masters dinsa ita kuma zata Fara nata
degree din.
Anyi lefe na garari Wanda ya dauki Baki fiye da tunanin Mai tunani, an kashe kudi
Kamar ba'a San zafinsu ba.
Lokacin da bikin ya rage baifi saura wata biyu ba sai lamarin ya Fara canzawa kwata
-kwata Sahal ya rage zuwa gurin Zahra haka ma sai a kwana a wuni Bai kirata ba,
duk wani zazzari da yake na bikin su events din da yake ta faman damun zahra da
maganar duk ya daina Kai tafi-tafi sai ayi kwana uku hudu har sati Bai kirata ba,
da farkon abin tana kiransa taji ko lafiya a yanayin yanda yake amsa Mata wayar
saita hakura da Kiran nasa, tun Ammah na zuba ido har ta samu Zahra a wani dare ta
tsareta da tambayar ko wani Abu ya hadata da Sahal ne? Ta Bata tabbacin ba abinda
ya hadasu sai dai ta fada Mata yanda suka ringa yi dashi a kwanaki idan ta Kira
shi.
Addu'a Ammah ta Bata tace ta ringa yi itama zataci gaba da yi, Mata sannan ta
umarceta da kada ta Kara kiransa a wayar ta zuba ido kawai.
Duk abinda Ammah take na shirye-shiryen Baki Bata fasa ba, tayi waya mutanan Jordan
ma sunce suna Nan tafe Amma a daure a turo Zahra Kamar saura wata data bikin.
Ba'afi sati daya da waya da kakanninta na uwa ba sakon kayan dakinta ya sauka
Nigeria daga Istanbul kayan da suka gigita Mama Dan ba kayan Wasa bane set din
gado har hudu kujeru set uku bayan electronics kuwa wasu har ba'a San amfaninsu ba
sai dai idan an duba manual din.
Alhaji Jafar yayi fada Kamar ya Ari Baki lokacin daya Kira Abbie akan danme zasuyi
Masa haka toshi meye amfaninsa da bazasu Bari yayi Mata kayan dakin ba.
Hakuri Abbien ya shiga bashi akan su basuyi Dan su Bata Masa raiba, sunga abinda ya
kamata suyiwa diyar Najwa kenan.
Ammah da Mama Alhaji Jafar ya Kira ya fada musu tunda an Riga an yiwa zahra kayan
dakin da duk abinda ya kamata to ga fifty million Nan ya baiwa Zahra idan komai ya
nutsa saita Fara business na abinda take son sayarwa sannan ya Bata shanu biyar.
Kuka Ammah ta saka saboda Dadi ta rasa bakin da zatayi Masa godiya, yanda take
dawainya da wannan marainiyar Allah Bai taba gajiyawa ba.
Mama ce ta Ari bakinta tana ta yiwa Abban godiya da saka Albarka sai faman dariya
tace bakinta yaki rufuwa, tun Ammah na ganin dariyar farin ciki ce har ta Fara wani
tunani na daban, Nan da Nan ta Kori shaidan akan abinda zuciya ke sawwala Mata.

Lokaci na Kara tafiya daukewar ma'amala na Kara yawaita a tsakanin Sahal da zahra,
yanzu ta Kai kwata-kwata sun daina waya dashi, ana saura kwana talatin da hudu a
Fara biki Wanda yayi daidai da saura kwana uku zahra da Hameeda da Abdul Hakeem su
tafi Istanbul. Dan direct gurin kanwar Ummeen Hanifa zasu tafi daga baya su Ummeen
sun samesu a can, idan an Gama komai su rankato Nigeria Dan da gaske Ummee ta
shiryawa bikin sosai.

Washe gari, tunda gari ya waje Mama ke Kai kawo tsakar gida duk da ba aikinta bane
ba Kuma halayyarta bane hakan. Yayin da a bangaren Ammah ta rasa me yake Mata Dadi
duk kasala ta baibayeta jinta take Kamar ma zazzabi na neman rufata...


❤️️
AUREN HUCE HAUSHIN
❤️
❤️

🔷PEGE TEN🔷
Story
&
Written
By
MAMAN FATIMAH

******Jujjuya littafin project din Ardo yayi, sai Kuma ya mikawa Alhaji Jafar Yana
fadin "Duba ka gani Yallabai ni tunda ba ganewa zanyi ba,naji Dadi da Allah yasa
aka Gama wannan karatun ba domin na saka auduga na toshe kunnuwa naba da ba'ayi
karatun Nan ba, tunda Wanda yaso auren nata yace in dai zatayi karatun Nan shi ya
fasa, shi Kuma Dan uwanta na wajen kanena yace karatu Babu gashi tunda tana ganewa
Kuma tana so, kaga yanzu duk gurin nan namu ita me yiwa mutane Allura".
Kallonta Alhaji Jafar ya karayi,sannan ya kalli Ardon Yana fadin.
"Yaushe ta Fara karatun ne na ganta karama amma har ta hada diploma?"
Gyara tsayuwa Ardon yayi Yana fadin "wallahi am tun tana aji hudu na furamare Dan
uwanta ta kaita aji daya na sakandire tunda yayi wani zuwa suka zauna da kannen
nasa yaga tana da kokari shine yace Mata idan ta Gama makarantar tana son taci gaba
da karatu, shine tace Masa tana son ta Zama malamar asibiti, to tunda sukayi haka
ya kudurci aniyar tsayawa akan karatunta shi yasa da akayi Mata chaaaa akan maganar
aure yace Bai Hana ayi maganar aure ba. Amma ya Dora sharadin saidai idan mijin ze
barta tayi karatu abinda ya gagara kenan aka fasa Amma duk yan uwanta anyi musu".
"Masha Allah. Allah ya Sanya Albarka, haka ake so a rinka barin Yara Mata suna
karatu barin ma na bangaren lafiyar da malaman makaranta, yanzu ba cewa kayi ita ke
yiwa mutane allura ba da sauran abubuwa? To da batayi karatun ba da basai an tafi
wai gurin an nema ba? Ba komai in Sha Allah zatayi auren ta Kamar kowa".
Ardo ya amsa da "Allahumma Amin".
Ma'un Alhajin ya kalla "Asma'u kin amince na tafi da project din naki na duba a
hankali in yasa said dawo Miki dashi".
Kai ta gyada alamar Eh.
Sunyi sallama da Ardo tawagarsu suka wuce zuwa Yola inda zasu bi jirgi zuwa Abuja.
Wannan shine silar haduwar Alhaji Jafar da Ammah, ya koma maida project da Kuma
kafa gwanatinsa cikin ikon Allah suka yarjewa juna.
Lokacin da magana tayi karfi Rabi'a taso tada hankalinta saida Nanna ta taushe ta
da kalamai masu kwantar da hankali.
Cikin kankanin lokaci akayi bikinsu. Amarya ta tare cikin ikon Allah zaman Rabi'a
da Asma'u ya kasance Zama Mai tsabta.
Wata uku da auren Asma'u ciki ya bullo duk masoyin Alhaji Jafar ya Taya shi murna
sosai a lokacin ne Alhaji Jafar ya biyawa Rabi'a makka kusan abinda ya kwantar Mata
da hankali kenan Dan ya fada Mata idan take tayi addu'a sosai akan matsalar ta.
A haka rayuwa ta dunga gurguwa har cikin ya Isa haihuwa Ardo dasu Inna maimuna sun
so Ma'un to koma gida zaman haihuwa Amma Nanna ta Hana tace meye amfanin ta ita in
dai sai Asma'u ta koma gida.
Cikin ikon Allah a wani dare nakuda ta tasowa Asma'u lokacin Alhajin Yana nan, Nan
da Nan suka nufi asibiti wurin karfe biyu da rabi Amma kafin hudu Allah ya dauketa
lafiya ta haifi takwaye mace da namiji.
Murna gurin wannan iyalin ba magana ranar suna yaran aka bar musu sunan su sai dai
su Hassan da Hasana aka daka musu.
Kullum yaran suna tsakanin Rabi'a da Asma'u suka rainon 'ya'yansu. Lokacin da aka
yayesu a lokacin Allah ya baiwa Rabi'a ciki itama ba'ayi wata biyu ba Asma'u ma ta
Fara laulayi, cikin ikon Allah cikin Rabi'a ya zauna kusan lokaci daya suka haihu
Rabi'a haifi Hamza yayin da Asma'u ta haifi Abdul Hakeem.
Bayan haihwar Hamza Rabi'a Bata Kara haihuwa ba Saida Asma'u tayi maza biyu sanan
Rabi'a ta haifi mace Murjanatu, bayan Murjanatu Rabi'a ta Kara haihuwar Salma sai
auta Hameeda ita Kuma Asma'u ta haifi Sulaiman sai auta Musaddiq, zuwa lokacin
sunansu ya bace yayin da ake gadawa Hajiya Rabi'a Mama wasu na waje suce Hajiya
Mama, Hajiya Asma'u Kuma Ammah.

WACECE FATIMAH ZAHRA?


'ya daya tilo ga kanin Ammah shaqiqi Muhammad Sani. Mahaifiyar Zahra Najwa
Balarabiyar Jordan ce sun hadu da Muhammad Sani ne lokacin da yaje karatu kasar da
farko mutunci suke da Najwa sai daga baya ya juye ya Zama soyayya har Allah ya
nufesu da aure da taimakon wani malaminsu Dan kano Dan kusan ta bagarensa su Ardo
wanda suke Kira Baffa ya Sani ya Kuma amince da Malam Muhammad Kabir ya Zama
waliyyin Muhammad Sani a can.
Lokacin da Muhammad Sani ya Gama karatu ya zauna a can yayi aiki kusan shekara biyu
daga baya ya tattaro nasu ya nasu suka dawo Nigeria, lokacin Najwa nada cikin
Zahra wata bakwai a lokacin Kuma Ammah na goyon Sulaiman Mama na goyon Hameeda.
A Jimeta Muhammad Sani ya sayi gida saidai suje Mubi kawai suga iyayensa,ba dadewa
Najwa ta haifi 'yarta Zahra wadda taci sunan mutum biyu mahaifiyar Najwa da
Mahaifiyar su Ammah.
Haihuwar Zahra ba dadewa Muhammad sani ya Sami aiki a Abuja karkashi minstary of
internal affairs da taimakon Alhaji Jafar.
Zahra nada wata biyar wani cikin ya bullo a jikin Najwa Mai wata irin masifar
laulayi, Wanda ya tilasta Ammah ta dauke Zahra daga bakin nono.
Lokacin da komai da dai dai ta a gurin aikin nasa ya dauki Najwa suka koma Abuja.
Saida watan haihuwarta ya Kama ya kaita Mubi shi Kuma ya koma Abuja.
Lokacin data haihuwa iyayenta sunzo Nigeria da kanwarta Nawwara a Karon na biyu
Mahaifiyar ta taso tafiya da Zahra Ammah ta dunga magiyar abar Mata ita harda
kukanta.
Lokacin da suka Gama wanka Muhammad sani yazo ya tafi dasu tafiyar da har abada
Basu dawo ba a hanya sukayi hadari sun bar Jos Basu karasa Abuja ba.
Yan uwa da iyaye sun shiga cikin tashin hankali marar misaltuwa Ammah tayi Kika
Kamar ba gobe,ta rasa Dan uwanta shakiki, ba karamin Kai ruwa Rana akayi ba kafin
Ummee kakar Zahra ta hakura ta barwa Ammah Zahrar.
Tunda daga lokacin Ammah ke baiwa Zahra wata irin kulawa ta musamman sai Kuma shima
Mai gidan ya kwallafa ransa akan soyayyar yarinyar abinda ya haddasa tsana Mai
tsanani tsakanin Mama da zahra inda ita mamar ke ganin Kamar nema ne yasa Alhaji ke
kaunar Zahra, tana ganin idan Dan tana 'ya mace ne karama ai itama tana da nata
kananan 'ya'yan mata Amma baya nuna kulawa akasu Kamar Zahra ko Dan tafisu kyaune
tunda Babu inda ta baro uwarta.
Wannan kenan.

Ranar da za'ayi jarabawar share fagen shiga karamar secondary ta gwamnatin tarayya
tun sassafe zu Zahra suka shirya ita da Sulaiman da Hameeda da Salma duk da Salma
ta girmesu Amma yawan yi Mata repeating yasa suka taddo ta.
Har sun shiga mota Bala direba na niyyar shiga Zahra ta bude ta fito da sauri ta
nufi cikin gida Sulaiman Yana kiranta tayi banza dashi ta shige da gudu ta karasa
dakin Ammah tana fadin "Ammah na manta kayana da Ya Hassan ya kawo min har zamu
tafi na tuna".
Daga toilet Ammar ta fito ta nufi bedside locker ta janyo ta mikowa Zahra ledar
tare da fadar "Maza kada ku makara mana".
Kai Zahra ta gyada kafin tace "Ammah ki kara yi Mana addu'a Dan Allah Ina son naci
jarabawar saboda Abbana yace idan naci makarantar zemin kyautar wani Abu"
"To naji maza Allah ya bada sa'a"
A kofa suka hadu da Sulaiman ya biyo ta tana fadin "Na rantsa da Allah zamu tafi mu
barki ba Dan Abba ya fito ba da wallahi sai dai ki fito kiga bama gidan".
Kafin ya saki labulen ya juya Zahra ta Kai kofar da zata kaika compound din gidan.
Masha Allah anyi jarabawa an Gama sai jiran sakamako.
A haka sukaci Baga da zuwa makaranta har suka Zama common enterence a matakin jaha.
Lokacin da suka dawo zaman gida lokacin ne Alhaji Jafar da kansa ya yiwa Zahra
passport da visa Saida ya Gama komai sannan ya fadawa su Ammah da Mama. Godiya
Ammah ta shiga jerawa Mai gidan nasu,yayin da Mama tayi shiru Kamar bazatayi magana
ba sai Kuma tace "yanzu Yallabai da kanka zaka rakata ai da Koda Hasana ko Hassan
ka hadasu zasu kaita ko Kuma a fadawa cen kakanninta su turo a tafi da ita ai cacar
kudin Kamar yayi yawa".
Daga Ammah har Alhaji Jafar din kallon Mamar suke ita dai Ammah shiru tayi yayin da
Alhajin yace.
Saboda ban San darajar 'ya'ya ba zan hada Yara a tafiyar uwa duniya daga Nan har
Jordan na kwanta a gida hanakli kwance ko?"
Kai ta gaigice tare da fadin "gani makudan kudi za'a kashe".
Wani kallo yayi Mata "kada ki kawo b'araka Rabi'a duk yaran dake gabana daya na
daukesu yada zan yiwa abinda na Haifa haka zan yiwa marainiyar Allah. Da Kuma kike
maganar cacar kudi idan zan jera shekara Ina Kai zahra Jordan kullum ba abinda ze
girgaiza a cikin abinda na mallaka".
Ku tashi kuje.
Lokacin da zasu tafi anyi Mata tsara sosai Dan Nanna ma kilishi tasa aka yi Mai
yawa na tsaraba.
Har kano su Ammah da yara sukayi musu rakiya.
Lokacin da sukaje Jordan din ba karamar murna kakanninta zukayi ba Dan Babu zato
suka gansu, sun Kuma Kara yabawa da cika Alkawarin Alhaji Jafar Dan da kansa yayi
musu Alkawarin ze kawo musu Zahra Dan ko a waya Bai fada musu zuwansu ba,sai
address dai daya taba tambaya can wani lokaci.
A ranar Zahra taga zallar soyayya a gurin dangin Najwa Dan gidan cika yayi da 'yan
uwa aka dasa sabon kukan rashin Najwar da kyar Abbie da Abbanta suka dinga Basu
hakuri Dan ma Alhaji Jafar ba larabcin yakeji sosai ba saidai Wanda suke Jin
turanci suka ringa magana dasu.
Lokacin da Alhaji Jafar din ze tafi masukin daya Kama a hotel Abbie hanawa yayi duk
yanda yaso zillewa kin yarda yayi dole ya amince aka sauke shi a wani part dake
kusa da nasa Ummee din, Dan ba karya dukiya dai Kam akwaita Dan shi kanshi Alhajin
yayi mamakin yanda ya riskesu Bai taba kawo haka suke ba lallai yasan hadin Allah
ne kawai da suka bawa Muhammad sani auren 'yarsu Dan tazarar Mai nisa ce a tsakanin
su.
Kwanan Alhaji Jafar bakwai ya wuce Umara yayin da Ummee tayi Masa Alkawarin zasu
hadu a Saudiyyar tunda zata kawo Zahrar Nan gurin iyayenta da 'yan uwa su ganta a
cikin garin Madinatul Munawwara.
Satinsa daya da zuwa Suma su Zahrar sukazo Saudiyyar ita da Ummeen da Aunty
Nawwara.
A Nan ma Saudiyyar Zahra taga gata iya gata Dan kowa Nan Nan yake da ita, Dan
kanwar Ummee Hanifa sosai ta kafe sai dai a bar Mata Zahra ta tafi da ita Istanbul
inda take aure Wai Bata yarda da zaman Nigeria ba.
Ankai ruwa Rana da ita kafin ta hakura Dan da gaske Alhaji Jafar ya bude Mata aiki
Dan cewa yayi idan irin haka za'a ringa yi bazai Kara bawo musu ita ba saidai duk
Mai son ganinta taje ya ganota Kamar yanda Ummee keyi, hakuri aka ringa bashi.
Saida aka Kai Zahra makka suyi kayi umara sannan suka fara Shirin baro kasar.l
Sayyaya dai Zahra ta shata Dan wasu kayan sai a awon cargo akayo musu su.
Sarkar gwal da warwaro zobe kuwa kirar Saudiyya da Dubai zuwa kirar Bahrain sun Kai
kala goma duk dai dai size din ta sai na Ammah biyu na Hasana ma biyu shi kanshi
Alhajin anyone mass goma Sha Tara ta Arziki.
Ranar da zasu dawo Zahra Tasha kuka haka kakarta Ummee,har jidda sukayo musu rakiya
Basu suka tafi ba sai da jirgin su Zahra ya tashi a sararin subahanahu wata'ala.
Saukar safe sukayi anan suka samu Bala direban Alhaji Dan Bai fadawa kowa sun taho
ba sai Balan kawai, sau da yawa idan ya fada gashi Nan a hanya hankalin Nanna baya
kwanciya har sai ya iso.
Lokacin da suka shigo harabar gidan suna tsayawa Zahra to garzaya cikin gida tana
fadin "Ammah!!! mun dawo".
Da gudu Hameeda ta fito daga part dinsu, rungume juna sukayi suna ta tsallen murna
Sai jikin zahra Hameedar ke shafawa gani take kamar canza Mata Zahrar akayi.
Da sauri Ammah ta fito tana "fadin wa nake gani ne haka Kamar bakin saudiyya zuwa
ba notice?"
Alhajin ne ya Bata amsa.
"Surprised din ki mukayi ko Zahra na?.
Kai ta gyada masa.
Kayansu ne su Bala da Mai gadi suka Fara shigowa dasu kafin Alhajin ya nufi part
dinsa na cikin gidan yayin da Ammah ta rufa Masa baya.

Har yayi wanka ya shirya Mama Bata shigo ba, har ya tambayar Ammah yayi Ina
Rabi'a ? Tace Masa tana ciki watakila ko barci take.
Kusan kwana su Zahra sukayi tana baiwa Hameeda labarin abinda ta gani da inda
sukaje a Jordan da saudiyya, wurin karfe biyu Ammah ta tashi zatayi nafila ta jiyo
su suna Hira a dayan bed room dinta lokacin wuri biyu da rabi na dare, leko tace
su kwanta basu san dare yayi sosai ba.

Washe gari an baje tsarabar Zahra an baiwa kowa dai dai gwargwado.
Amman tsarabar Hameeda daban take Dan har sarka Saida ta baiwa Hameedar.
Basifi sati biyu da dawowa ba jarabarsu ta fito ta Federal inda Zahra ta samu
F.G.G.C KAZAURE yayin da Sulaiman ya samu F.G.C DAURA, Hameeda F.G.C AZARE. Salma
ce kawai bata samu ba a cikinsu.
Sunyi murna Kuma sunyi bakin cikin rashin samun makaranta daya duk an watsa su
Abban Kuma da ya Hassan sunce kowa ya tafi inda ya samu, ita Hameeda Bata da
damuwa tana gida, su Kuma duka 'ya'yan Ammah duk sun fita waje danma hanyarsu daya
sai an aje Zahra a karasa da Sulaiman.
Ranar da zasu tafi sun Sha kuka haka suka dauko hanya malam Bala da Ya Hassan ne
suka kaisu.
Lokacin da aka Kai Zahra an tashi daga aji, wasu Yara House master dinsu ya kira da
wata prefect yasa su Kai Zahra room din 'yan j.s one.
A cikin yaran da suka Taya Zahra daukar kayane wata yarinya tace Mata "sister kizo
ki zauna a kwana ta tunda ni daya ce saman gadona ba kowa".
Kai kawai zahra ta gyada Mata tana ta sauke ajiyar zuciya.
Ita ta taimkawa Zahra ta shirya komai a locker dinta, Saida ta Bari zahra ta HUCE
daga kukan da tsaha sannan tace Mata "ni sunana Sajida Musa ni 'yar kano ce unguwar
Gwammaja kefa ya sunanki?".
Nan Zahra ta fada Mata komai nata tun daga Nan suke tare har suka Zama aminai komai
nasu ya Zama daya banbanci su kawai Sajida na A Zahra na C.
Haka sukaci gaba da rayuwa a makarantar gasu Kuma Yara masu kwazo barin zahra ga
kyau ga ilimi Nan da Nan tayi suna a makarantar kafin hutu tayi popular sosai a
makarantar, idan kace 'yar larabawa kowa ya santa ba Kuma Dan Babu irin jiinsin
nata ba A'a farin jini ne daga Allah.
Lokacin da akayi hutu Zahra ba karamar murna tayi ba Kuma cikin ikon Allah da wuri
malam Bala yazo lokacin har ya dauko Sulaiman.
Bayan Azahar kadan suka shiga Azare sunyi murna sosai da ganin mutanen gida Dan
Sulaiman har da kuka, Nan su Hameeda suka saka gaba suna tsokana.
Haka suka cigaba da karatunsu cikin amincin Allah, lokacin da sukazo hutun third
term ne akayi auren Aunty Hasana aka kaita Jos, Ya Hassan Kuma Daman Yana karatunsa
a Rasha.
Kowa inda yake yacigaba da karatunsa Salmace Allah ya taikata ta samu shiga FGC
AZAREN itama a ss1.
A haka aka dunga juyawa har suka Gama secondary School dinsu suka dawo gida.
Dawowarsu ba dadewa Allah ya yiwa Nanna rasuwa rashin daya taba Abbansu sosai.
Dan ya Dade Yana fama da damuwa tunda a rayuwa da ita ya tashi baisan dadin uba
namiji ba itace komai nasa.
Ganin abin nasa Yana neman yayi yawa yasa Abokinsa bakon malamin daya sauka Nan
daura gidan Nanna da almajiransa dududu Bai zaifi sa'an Alhajin ba malam Bubar ya
dukufa yi Masa addu'a tare da saka Yara kanana suna Masa addu'a, cikin ikon Allah
sai komai ya daidaita.

Ranar wata laraba zahra ta shirya zata raka Hameeda duba Qawarta meenal gidan Dan
majalissarsu Mai wakiltar su majalissar Jaha, wani material ta saka Mai ruwan
sararin samaniya yayi matukar karbar jikinta haka dinki ma ya Dace da material din,
simple makeup tayi ta saka turarenta Amber oud new edition na kamfanin Al
haramaini.
Tunda ta fito Mama ke Mata wani irin kallo Wanda har saida ta rinqa Jin ta takura
kafin Hameedar ta fito.
A kasa suka taka suna Hira har sulaje gidan,sun Dan jima suna Hira da marara
lafiyar kasancewar breast lump ne aka cire Mata ba wani serious case bane.
Lokacin da zasu tafi suka Kara komawa gurin mamanta sukayi Mata sallama suna zaune
ne da a falonta kafin meenal din tayi Mata magana ta fito. Wani handsome guy ne ya
shigo falon da sallama ya Dan jefa car key dinsa sama, kana ganinsa kasan hutu ya
Kama jikinsa.
Ciki ya shigo lokacin da Suke amsa masa sallamarsa kujera two seaters ya zauna a
Kai wadda ke facing dinsu Hameedar.
Gaishe shi sukayi su Duke ya amsa Yana cewa "Hameeda daman kina Nan na Dade ban
ganki ba gaskiya Ina ga tun kafin na tafi Colombia fa".
Dan rausayar da Kai tayi tana fadar "wallahi Kam Ya Sahal an jima Kam kune dai
bakwa ganuwa Kuna uwa duniya kunyi shiru Kum barmu da zafin Kasarmu".
Ta fada tana dariya.
Dai dai lokacin mommyn su meenal din ta fito kallon Sahal tayi tana fadar Kai Kuma
haka mukayi da Kai?"
Kaisa ya Dan Sosa da key din hannunsa Yana fadi "Iam so sorry Mom kada ki damu
yanzu zanje na kawo Miki in Sha Allah."
Ya fada Yana mikewa da nufin tafiya Meenal tayi tsagal tana fadin "Dan Allah Ya
Sahal ka tafi dasu tunda cikin garin kayi.
Suka yiwa mommy sallama da godiya suka fito da leda Mai Dan girma a hannun Meenal
wadda mommyn ta Basu.
Har kofar gida ya kawosu suna tsayawa ya kalli Hameeda Yana fadar "Dan Allah ki
bani aron sister din take Mana Kona ten minutes ne Mana".
Dan murmushi tayi tana fadar.
"Ka Fara yiwa Abban mu magana dai haka Naga anayi"
Ita dai Zahra ciki ta wuce Dan Kamar a kan.kaya take duk ya takura Mata da wani
irin kallo har a cikin mota ma saita mirror yayi sitinta tunda Hameeda ce ta zauna
a seat din gaba tana Masa Hira Amman gaba daya hankalinsa yana kan Zahra.
Ita dai zahra Bata San yanda suka Kare ba taga dai Lokacin da Hameedar ta shigo ta
wuce dakin su.

Bayan kwana biyu da zuwa gidansu Meenal da yamma su zahra sun tafi islamiyya ne
baki sukazo gurin Alhaji Jafar, ya sansu farin sani daya kanin Dan majalissar su ne
dayan Kuma kanin Babansu.
Yayi mamakin ganinsu Saida suka gaisa ne suka bijiro da abinda ya kawo su na yiwa
yaron gurin Dan uwansu Sahal kidiba yaga yarinyar gurinsa Yana so. Shine mahaifansa
ya turosu ya gabatar da maganar Yana neman izininsa na Fara zuwa gurinta Shira.
Alhajin yaji Dadi sosai na yanda suka zo suka memi izininsa duk da Daman sharadinsa
kenan, ya Kuma nemi Jin wacece daga cikin yaran suka gada Masa zahra ce, nan ya
amince musu da addu'ar Allah ya hada kawunan su.
Tun daga lokacin Sahal ya Fara zuwa gurin Zahra cikin ikon Allah tayi na'am dashi
Basu Dade sosai ba sukayi wata irin shakuwa ta ban mamaki duk Wanda ya kwana ya
tashi a unguwar yasan irin soyayyar da sahal yakewa zahra kusan Kullum da yamma
Yana nan makale da ita, a haka har manya suka shiga maganar aka tsaida lokaci wata
shida inda zasu tafi Colombia inda yake hada masters dinsa ita kuma zata Fara nata
degree din.
Anyi lefe na garari Wanda ya dauki Baki fiye da tunanin Mai tunani, an kashe kudi
Kamar ba'a San zafinsu ba.
Lokacin da bikin ya rage baifi saura wata biyu ba sai lamarin ya Fara canzawa kwata
-kwata Sahal ya rage zuwa gurin Zahra haka ma sai a kwana a wuni Bai kirata ba,
duk wani zazzari da yake na bikin su events din da yake ta faman damun zahra da
maganar duk ya daina Kai tafi-tafi sai ayi kwana uku hudu har sati Bai kirata ba,
da farkon abin tana kiransa taji ko lafiya a yanayin yanda yake amsa Mata wayar
saita hakura da Kiran nasa, tun Ammah na zuba ido har ta samu Zahra a wani dare ta
tsareta da tambayar ko wani Abu ya hadata da Sahal ne? Ta Bata tabbacin ba abinda
ya hadasu sai dai ta fada Mata yanda suka ringa yi dashi a kwanaki idan ta Kira
shi.
Addu'a Ammah ta Bata tace ta ringa yi itama zataci gaba da yi, Mata sannan ta
umarceta da kada ta Kara kiransa a wayar ta zuba ido kawai.
Duk abinda Ammah take na shirye-shiryen Baki Bata fasa ba, tayi waya mutanan Jordan
ma sunce suna Nan tafe Amma a daure a turo Zahra Kamar saura wata data bikin.
Ba'afi sati daya da waya da kakanninta na uwa ba sakon kayan dakinta ya sauka
Nigeria daga Istanbul kayan da suka gigita Mama Dan ba kayan Wasa bane set din
gado har hudu kujeru set uku bayan electronics kuwa wasu har ba'a San amfaninsu ba
sai dai idan an duba manual din.
Alhaji Jafar yayi fada Kamar ya Ari Baki lokacin daya Kira Abbie akan danme zasuyi
Masa haka toshi meye amfaninsa da bazasu Bari yayi Mata kayan dakin ba.
Hakuri Abbien ya shiga bashi akan su basuyi Dan su Bata Masa raiba, sunga abinda ya
kamata suyiwa diyar Najwa kenan.
Ammah da Mama Alhaji Jafar ya Kira ya fada musu tunda an Riga an yiwa zahra kayan
dakin da duk abinda ya kamata to ga fifty million Nan ya baiwa Zahra idan komai ya
nutsa saita Fara business na abinda take son sayarwa sannan ya Bata shanu biyar.
Kuka Ammah ta saka saboda Dadi ta rasa bakin da zatayi Masa godiya, yanda take
dawainya da wannan marainiyar Allah Bai taba gajiyawa ba.
Mama ce ta Ari bakinta tana ta yiwa Abban godiya da saka Albarka sai faman dariya
tace bakinta yaki rufuwa, tun Ammah na ganin dariyar farin ciki ce har ta Fara wani
tunani na daban, Nan da Nan ta Kori shaidan akan abinda zuciya ke sawwala Mata.

Lokaci na Kara tafiya daukewar ma'amala na Kara yawaita a tsakanin Sahal da zahra,
yanzu ta Kai kwata-kwata sun daina waya dashi, ana saura kwana talatin da hudu a
Fara biki Wanda yayi daidai da saura kwana uku zahra da Hameeda da Abdul Hakeem su
tafi Istanbul. Dan direct gurin kanwar Ummeen Hanifa zasu tafi daga baya su Ummeen
sun samesu a can, idan an Gama komai su rankato Nigeria Dan da gaske Ummee ta
shiryawa bikin sosai.

Washe gari, tunda gari ya waje Mama ke Kai kawo tsakar gida duk da ba aikinta bane
ba Kuma halayyarta bane hakan. Yayin da a bangaren Ammah ta rasa me yake Mata Dadi
duk kasala ta baibayeta jinta take Kamar ma zazzabi na neman rufata...

❤️

✨️
AUREN HUCE HAUSHIN

❤️
❤️

STORY
&
WRITTEN
BY
MAMAN FATIMAH.

🔷✨PAGE ELEVEN✨🔷 (11)


________Misalin Sha biyu da rabi na Rana kawar Mama kuma Aminiyar Asabe tazo
gidan macece wayayya Mai kisisina Bata fiye zuwa gidan sosai ba sai lokaci lokaci,
ta Dan jima a dakin Ammah suna hira har tana tsokanar zahra da Amaryar gobe ana
dariya.
Part din Mama ta shiga suka kule a master bedroom dinta.
Batafi awa daya da zuwa ba, wasu Mata suka shigo gidan lokacin Ammah tana
bangaren Abba.
Zilai Mai aik cei ta leko tana fadin "uwar dakina anyi baki kuwa ko Ammah zaki
yiwa magana Naga bakin nata be"
Mayafi karami ta Dora a saman gashinta da tayi parking dinsa har wajen kugunta Yana
reto Baki sidik dashi jikin Nan nata Kamar ka taba jini fito.
Lekowa tayi tana musu sannu da zuwa tare da gaishe su tana fadar "ku shigo daga
ciki Bari na Kira Ammar".
Ta fada tana zura silifar a kafarta.
Daya daga cikin su ukun ne ta tabe Baki ta kauda Kai tana fadar "kirawo ta tazo ba
sai mun shiga ba tunda ba Zama mukazo ba"
Ita dai Zahra gaba tayi yayin da su Zilai masu aiki suka zuba musu idanu suna
kallon kallo ya junansu Dan daga Jin lafazinsu sun San ba abin Arziki ne ya
kawosu ba.
Kafin Ammah ta fito daga bangaren Abba sahura Daya Mai aikinta ta leka ta fadawa
Mama anyi baki. Da ita da Asaben suka fito Asaben na fadin "lale barhabin kushigo
Mana kun tsaya daga wajen"
Wata ce daga cikinsu Bata farkon da tayi maganar ba tace "A"a Hajiya ba Zama mukazo
ba munzo ne mu karbi kayan lefen da muka kawo na Sahal yace baya yi akai kasuwa".
Lafazin da Ya yiwa Ammah sallama kenan lokacin data fito Zahra na biye da ita.
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un"
Abinda Ammah ta fada kenan a zuciyar ta Nan da Nan wani jibi ya taso Mata.
Salatin Mama da Asabe ne ya fito da Alhajin daga part dinsa yayin da su Zilai
sukayi cirko-cirko duk wuta ta dauke musu Dan maganar tasu ba karamin razani tasa a
zukatansu ba.
A hankali ya karaso kusa da Ammah Yana tambayar meke faruwa ne kafin tayi magana
Mama tayi tsagal tana fadin "wane irin cin mutunci ne Alhaji ba laifi tsaye bana
zaune zasuzo suce a Basu lefensu Wai auren amfasa".
Ta karasa fada tana fashewa da kuka tana maganganu, ita kuwa Ammah ba abinda take
sai ambaton Allah yayin da Zahra ta nemi gefen inda aka shuka filawoyi ya zauna Dan
ji tayi Nan da Nan jiri Yana nema kayar da ita, itama bakinta ba abinda yake sai
ambaton Allah.
Kallo Daya Alhaji Jafar yayiwa Baki ya kawar da kansa Dan da alama da rashin
mutunci suka shigo gidan. Gyaran murya yayi kafin yace "Masha Allah munji sakonku
Amma Dan Allah ku koma kuce musu zuwa anjima inshallah Allahu za'a dawo da duk wani
Abu daya kasance nasu ne har sadakin da suka kawo Allah yasa hakan yafi Alkhairi".
Yana Gama fadar haka ya juya dakinsa ya barsu a Nan a teaye, Dan dukkansu ba
karamin kwarjini yayi musu ba.
Ammah part dinta ta nufa duk kwakwar mutum baze taba Gane Yanayin da take ciki
ba.Dan Allah yayi Mata wata irin zuciya Mai iya danne bacin Rai da wuya ka Gane
fushinta tana da hadiye fushi sosai, dakin suka bita suna Bata magana Mama sai
sharbe take tana Dan Allah wannan wane irin cin zarafi ne da tazarce ace saida
komai ya kankama sannan za'a bullo da wannan cin zatafin dan a wulakanta yarinya
har a ringa yi Mata wani gani -gani aga Kamar wani Abu tayi yasa aka fasa".
Sai lokacin Ammah tayi magana tana fadin "ba komai Mama Daman can haka Allah ya
nufa ba mijinta bane Kuma maganar mutane su ringa ganin Kamar wani Abu marar kyau
ne yasa aka fasa na barsu da Allah yayi Mani maganin komai, ba komai haka Allah ya
nufa rubutaccen Al'amarine baya goguwa".
Tana Gama fadar haka ta wuce bedroom dinta sun jima a falon suna tattaunawa kafin
su koma dakin mamar su Zilai kuma suka nufi in da Zahra tace zaune suka dinga Bata
magana duk da Bata want rude ba a nitsenta take.
Duk wannan kwamacalar da akayi su Hameeda da Salma basa Nan sunje Aiken Mama.
Tunda Alhaji Jafar ya koma daki ya kasa zaune ya kasa tsaye Bai taba zaton karamar
magana daga gida irin Honorable ba Amma ya hanasu kayan ne Dan ya tabbatar da daga
Ina maganar take shin da sanin uban yaron da waliyayansa ko Babu Dan yanda sukayi
komai cikin girma da mutunci ya kamata ko baza'ayi auren ba to a rabu cikin mutunta
juna.
Su malam Bukar da Yayan Alhajin Wanda suke 'yan maza Alhajin ya Samu da maganar
basuyi kasa a Gwiwa ba zuka nufi gurin waliyyan Sahal sai dai maganar haka take Dan
sun tsame ma hannunsu daga lamarin tunda iyayensa Basu da lissafi, Wai yaron ne
yace musu shi baze iya auren Zahrar ba yanzu ba wadda ya tsana kamarta duk duniya".
Lokacin da suka dawowa da Alhajin wannan labarin ransa yayi matukar baci, a ranar
aka maida duk wani Abu da yake mallakinsu ne.
Sai dare Abban ya Samu kebewa da Ammah in da ya ringa tausarta da kalamai masu Dadi
har ta Samu ta Samu nutsuwa Amma fa kasa kwana tayi a dakin nasa.
Lokacin data dawo daki Zahra Bata tafi nasu bangaren ba tana dakin Amma a kan gadon
tayi rigingine idanuta a rife hawaye na zurarowa daga gefen idon wani Abu yake Mata
yukuki a zuciyar ta.
Har Ammah ta bude kofa zahra Bata sani ba saida ta zauna a kiss da ita taji
shashhshekar kukanta kasa -kasa.
"Tashi zaune magana zamuyi".
Daga sama taji maganar Sam bata San Ammar ta shigo ba.
Ba musu ta tashi zaunen tana koge fuskarta da tayi wajir.
"Meye dalilin da Sahal ya fasa Aurenki ko ya sanki 'ya mace ne".
Cikin tashin hankali marar misaltuwa Zahra ta dago ta kalli Ammah kafin ta fasa
kukan da take dannewa tana na zuci. Kai ta shiga girgizawa tana wani irin numfashi
nKamar wadda zata shide.
Kafin Allah ya batan ikon bude bakinta ta magantu. "Wallahi Ammah ban taba abinda
kike tuhumata ba Koda wasa wallahi zan rantse Miki da Alur'an a bani zanyi Alwala
in ratse, idan na taba Zina Ammah Allah ya haramtamin shiga Aljannarsa ranar
Alkiyama"
Ta fada tana wani irin kuka Mai taba zuciyar Mai sauraro.
"Shitttt.....kada na Kara Jin wata magana makaranciyar wannan daga bakin ki. Ba
zarginki nakeyi ba na kasa samun nutusawa ne tun lokacin da sabbin halayensa suka
Fara fitowa, nake cikin zulumi da taraddadi saboda sanin yanda rayuwa ta Zama
abinda ta zama, ba komai kansa yayiwa ke kuma Allah yayi Miki Albarka ya bakin
Wanda yafi Sahal".
Bata iya amsawa a fill ba sai a zuciyar ta.
Tun bayan faruwar lamarin Zahra ke cikin damuwa Dan ma Haneeda tana tausarta da
kalamai na kwantar da hankali. Ammah ta Kira su Ummee ta fada musu komai sun so
kwarai zahrar taje Amma Alhaji Jafar yayi uwa yayi makarb'iya akan suzuzo idan
hankali ya kwanta, da haka suka bar zancen.
A Dan tsakanain ne Aunty Hasana tazo, sun Sha jajantawa sosai da Ammah itama sai da
ta tsare zahra da tambayoyi kala kala, daga karshe ta Kare da nasiha Mai tsoratarwa
sosai.
Lokacin da zata koma Jos ta nemi zata tafi da Zahra Abban bai Hana ba Yana ganin
idan tayi nisa da garin zatafi Samun kwanciyar hankali.
Zamanta a Jos Mai Dadi ne Dan daga baya ma fafutukar nemar Mata admission mijin
Aunty Hasanar ya Fara ba'a samu wadda ake so ba, sai diploma ya nemar Mata a wata
private school ta Fara computer science.
Hankalinta ya kwanta sosai ta cire soyayya daga zuciyar ta Sam taqi ba kowa fuska
akan soyayya duk da yanda ake kawo Mata Rida.
Ranar wata litinin sun Gama lectures dinsu na safe suna zaune da wata course mate
dinta 'yar kabilar Tiv suna wani Assignment jininsu ya hadu da jannifer sosai Dan
har gidan Aunty Hasana tana zuwa idan zasuyi wani aikin.
Bayan sun Gama ne suka nufe caf'e na cikin makarantar a cire musu hard copy din
aikin suka tarar da cinkoson mutane dole tasa suka fito waje ayi musu.
Har sun Gama sun fito suna niyyar tsallaka titi ne wata mota Mai azabar kyau ta
tsaya dai dai inda suke tsaye. A hankali na ciki ya sauke tinted glass din motar,
wani guy ne da gani hutu ya ratsa shi sosai, murmushi yayi musu idonsa na kan
zahra
Yana fadin "sannunki"
Jannifer ce to amsa masa Dan tana Jin hausa Kamar jakar kano.
"Yauwa sannunka" ta fada.
Kofar ya bude ya fito Yana sanye da kananun Kaya,fari tas dashi kamar irin ruwa
biyu din Nan half cast Dan sumarsa a nannade take kamar irin ta buzaye din Nan.
Cikin kwarewa da yadda da Kai kalli jannifer Yana fadar "Naga kawarki ne inso da
fatan zakiyi min campaign".
Dariya tayi tana kallon Zahra wadda tayi kicin kicin da fuska Kamar zatace wayyo
Allah.
"Gaskiya na tafi tunda Baki da aikin Yi ke saiki zauna".
Zahra ta fada tana nufar titi ganin an Sami space din tsallawa.
Jannifer da Dan jima dashi kafin ta shigo cikin makarantar, Koda ta shigo Bata yi
Mata maganar komai ba har suka Gama lacture dinsu suka tashi. Direban su Aunty
Hasana ya dauke su ya ajiye jannifer a hanya kasancewar su zahra sun gaba dasu Amma
hanyarsu daya sau da Daman sukan tafi tare ranar da jannifer Bata zuwa shagonsu.
Ranar Saturday misalin hudu da rabi haka su zahra da yaran Aunty suna compound din
gidan tana Dora Yara kan lilo marry go round suna Wasa kusan duk weekend a Nan
suke hutawa da yamma tunda islamiyyar safe suke zuwa a weekend.
Mai gadi ne ya nufo gurin da suke Yana fadin Zahara'u ki fadawa yallabai Yana da
bako a waje".
Auntyn ta fadawa Abban su Faruq Yana da bako inji Mai gadi.
Lokacin daya fito yayi mamakin da baiga bakon ba ya nufi gate Yana tambayar Mai
gadi, shine yace "ni ne na hana ya shigo tunda yace bakasan da zuwansa ba bilhasal
ma yace baka sanshi ba"
Kofar Mai gadin ya bude masa ya nufi gurin da motar take yayin da shi kuma na cikin
ya fito. Da gaske baisan yaron ba, hannu ya bashi sukayi musahiha sai Kuma sukayi
shiru Ya Aliyun ne mijin Aunty Hasanar yace Masa "ko kaine maisallama Dani?".
"Eh nine"sai Kuma ya danyi shiru.
Ya Aliyun ne yace "my friend pls talk feel free with me".
Nan yayi Masa bayanin yaga Zahra ne Yana sonta shine ya biyota gida, ya fada masa
sunansa MUNEEB mahaifansa Kuma Alhaji Salman Mai fata. Kallonsa ya Aliyu ya karayi
yayi mamakin yanda d'a Kamar na Alhaji Salman Mai fata yake da irin wannan tarbiyya
ganin yanda mahaifansa yake da mahaukanta kudi Kuma yasan 'ya'yansa sosai Amma da
yawansu gata yasa sun lalace basa ganin kan mutane da gashi.
Ya Aliyun yaji dadi sosai ya Kuma bashi damar zuwa gurin Zahrar sannan ya Dan fada
Masa wacece Zahrar a gurinsa.
Lokacin da ya Aliyun ya koma bayani ya yiwa Aunty Hasana na abinda ya faru itama ta
bada goyon baya tasan ko yanzu Zahra tayi gaba Allah ya Bata Wanda yafi Sahal Dan
ba karya ba hadi a tafiyar.
Da dare Aunty ta Samu zahra da maganar da farko tuburewa tayi akan ita Bata so
saida Aunty ta fito Mata ta bayan gida sannan ta fashimci abinda Auntyn take son ta
Gane.
Washe gari Aunty har da ita aka hadawa MUNEEB abin tarba, Zahra ta Dade tana
mamakin yanda akayi yasan gidan su Amma data Zama very curious sai ta gano duk
yanda akayi jannifer ce ta bashi address dinta. Yau ma da yamma yazo, falon Ya
Aliyu aka bude Masa yayin da Mai aikin Aunty shema'u ta Kai Masa abin tarba.
Wata straight gown ta saka ta atamfa glitter Mai ruwan peach colour sai madaidaici
gyale kalar lemon green irin touching din jikin atamfar sai takalmi shima lemon
green din plat Mai kyau. Bata daura dankwalin kayan ba. Ta fesa turenta Amber oud
gold, tun kafin ta karaso kamshin ta ya fada Masa zuwanta, kofar ya zubawa idanu ai
lokacin data shigo da sallama Saida ya Dan samu shock na wucin gadi Ashe ranar ba
inishin Zahrar ya gani ba yanzu ne yaga zahirinta, a kasa ta zauna kan carpet tana
gaishe shi kanta Yana kallon kasa. Nan ya gabatar Mata da kansa da abinda ya kawo
na son aurenta, bai matsa Mata na lallai sai yaji ra'ayinta a sannan ba shima bai
jima ba ya tafi, bayan ta shigo ne Mai gadi yayi knocking a kofar falon shema'u ta
bude manyan ledoji ne ya Mika Mata guda biyu yace a bawa Zahara'u inji bakonta.
Tun daga lokacin Koda yaushe Muneeb yana hanyar gurin Zahra,r tun tana dari dari
dashi har ta sake, shi mutum ne Mai saurin shiga Rai Yana da wasu Qualities da
zasusa asoshi.
Kafin su rufe wata biyu sunyi wata irin shakuwa ta ban mamaki duk Wanda ya kwana
ya tashi a family din Mubeen yasan da zaman Zahra haka itama nata sun San Muneeb
Dan har Azare yaje ya gaishe su da ashirin bama sha tarabta Arziki ba,har Saida
Abban su yayi Masa fada sosai akan kada ya Kara musu haka in dai Yana son su
Shirya.
Sun daf da Gama diploma dinsu Iyayen Muneeb sukayi maganar aure, ba Bata lokaci aka
saka Rana ba'a wani ja lokaci ba Mai tsawo ba, abu kama-kama shima Kamar na baya
abun ya shashence ba wani cikakken dalili haka Nan Rana tsaka Muneeb yace ya fasa
akayi juyin duniyar Nan yace shifa aure ba dai da Zahra ba komai za'ayi, dole aka
hakura Dan shi cewa yayi har kayan ya bar Mata saidai abinda iyayenta Basu amince
ba kenan.
Fadin halin da zahra da su Ammah suka shiga bazai misaltu ba, Dan hankalinsu yanzu
yafi tashi fiye da wancan lokacin.
Ammah taso kwarai zahrar ta koma Azare Amman Maman Ya Aliyu ta roki Alfarmar zata
Kai zahra gurin masu Islamic chemist a gani ko namijin Aljani ne ya aureta.
Ammah ba tayi musu ba sai godiya tayi sosai, sunje harda Aunty Hasana anyiwa Zahra
tambayoyi ba alamar Aljani a jikinta sai dai sun fada musu da alamar sihiri a tare
da ita Amma ba sosai ba, Nan suka bada magunguna Hajiyar ta biya suka dawo gida.
Jannifer ma tayi bakin cikin abinda ya faru taso Zahra ta Bata dama taje garinsu
ayi mata wani Abu akan idan ma wani ne yake lalata lamarin auren zega abinda ze
same shi. Nunawa tayi Bata so ita haka Allah ya tsara Mata wannan qaddarorin Kuma
ba makawa sai sun sameta.
A haka har suka Gama diploma dinsu kafin Aunty Hasana ta mayar da Zahra Azare.
Haha rayuwa taci gaba da gudana, duk wani buri akan aure Zahra ta cire shi Bata
kula kowa duk iya nacin mutum Bai isheta kallo ba, wani lokacin har fada suke da
Hameeda akan rashin kula samari sai dai sau da yawa tana Mata uzuri akan irin yanda
fasuwar aure take walagigi da ita.
Zama ya Mika lokacin har anyi wurin wata Tara da fasa aurenta da Muneeb. Wani
yammaci suna zaune a bayan part din Ammah ita da Hameeda da Mujiba data shigo musu
yawan yamma suna hira Kiran ya Abdul Hakeem ya shigo wayar Hameeda Yana tambayar
suna ina ne ya shigo Bai gansu ba.
Inda suke ta fada Masa suna niyyar tashi ya zagayo bayan, a tare suka gaishe dashi
ya amsa Yana gaisuwar tasu yana fadin "Congratulations"
"For what Yaya?" cewar Zahra.
Irin Brown din envelope din Nan babba ya Mika Mata Admissions letters ne guda biyu
a ciki na Salma da Hameeda duk sun Sami gurbin karata a federal University Dutse
jigawa state (F.U.D).
Cikin murna ta rungume Hameeda tana fadin "congratulations sister".
Kafin ta sake ta tana Mika Mata takardun, ai tana arba da wannan abin Arziki ta
Diba a guje tana fadin"thank you Yaya Allah ya saka maka da Alkhairi".
Bayan ta wuce ne zahra ma ta Kara Masa godiya sosai.
Kujerar da Hameeda ta tashi ya janyo ya zauna alamun dake nuna magana Mai
mahimmanci zeyi da ita.
Ganin haka yasa Mujiba tashi tana fadin "Yaya sai anjima".
"Dawo ki zauna ba Zama zanyi ba.magana zan fada Mata kawai"
A takure ta koma ta zauna.
Kan Zahra ya maida kallonsa "kina jina?" Kai ta gyada Masa alamar eh.
"Good" ya fada.
"Ina ga Nan da one month ko three weeks kema Zaki wuce Zuwa Turkey daga can Kuma
idan komai ya daidaita Zaki wuce syprus inda Zaki hada a degree dinki, idan kin
tuna Kamar two months da suka wuce ai na karbi komai naki to Mama Hanifa ce ta
bukata a tura Mata a she makarantar zata nemar Miki taso a Samu a Nan turkey din to
ba'a samu ba, ita kuma Bata son a Kara Bata lokaci, shine ta yiwa danta magana
tunda a can yake aiki da ofishin jakadancin turkiyya na kasar Kuma ma Nan ne kawai
Mama Hanifar ke ganin yafi kusa da istanbul din".
Ba Zahra kawai ba hatta Mujiba tayi murna kwarai da gaske gatan da za'a yiwa Zahra
kenan a irin wannan lokacin na a rabata da kasar gaba daya Kota Samu peace of mind.
Godiya ta ringa yiwa ya Abdul Hakeem din harda 'yan hawayenta na Dadi.
Gashi Ammah Bata Nan taje Jimeta gurin biki, taso tana Nan ta kwanta a jikinta suyi
sharing din farin cikin. Har ya Abdul Hakeem din ya kai kwanar da ze fita ya juyo
Yana fadin "don't talk to anyone, keep silent pls, nasan Mujiba Bata da problem shi
yasa na fada a gabanta".
Yasa Kai ya wuce.
Kallon junan su sukayi suna son banbance maganar Ya Abdul Hakeem.
❤️

AUREN HUCE HAUSHI


❤️

MAMAN FATIMAH

PAGE TWELVE (12)

__________A cikin qanqanin lokaci aka Gama yiwa su Hameeda shirye - shiryen tafiya
makaranta Dan sau biyu suna Zuwa jigawar akan registration din. Sai wannan ciccira
kai salma keyi tana sakin maganganu bare idan suna dakinsu su kadai ta dinga fadin
magana kenan, ko ci kanki zahra Bata ce Mata sai ma wani lokacin Hameeda ke kwabawa
Nan da Nan Kuma su hau sama da ita.
Ranar da zasu tafi harda ZAHRA a 'yan rakiyar, Mama ma taso zuwa Abba ne ya hanata
ya Kama fadan me zatayo.
Har hostel Zahra ta rakasu Lokacin da zasu taho ne Hameeda ta Fara share hawaye
itama zahra ta Kama, Saida ya Hamza yayi musu Jan Ido suka daina kukan, Yayin da
Ya Abdul Hakeem yake musu dariya Yana fadar "Banda tsabar shagwaba ta lalacewa har
wani kuka kuke Kamar wasu 'yan J's one".
Wani kallo ya ai kawa zahra na Baki Fara kuka ba.sai kin ganki a tsakiyar masu
jajayen kunne tukunna Dan ma dai kema samman kalne ya gada a zuciyar sa.
Sai bayan magariba suka dawo gidan.
Ba'a fi sati biyu da tafiyar su Hameeda ba visa din su Zahra ta fito ita da Abdul
Hakeem.
Sai ana ya gobe zasu tafi Ammah ta fadawa Mama. Ai Kuma tayi korafin abin Dan har
Alhajn ta fadawa yace shima jiya yake Jin labarin tunda Saida komai ya kankama
sannan suka Kira suka fada Masa Dan kada ya Hana.
Da safe Bala dureba ta dauke sai kano inda zasu tashi.
Satin Abdul Hakeem hudu a can Dan Bai taho ba Saida ya raka Zahra har syprus din a
gabansa komai ya kammala ranar da ze tafi Zahra tayi kuka Kamar idonta ze fita sai
a sannan taga ba karamar wauta tayi ba data yarda da wannan karatun, dadin ta daya
da uncle Haisam a kasar ko banza tana da gurin zuwa a debe Mata kewar gida.

Ta Fara karatu cikin nasara Bata da wata matsala ta zahiri saidai sau da yawa tana
shiga dogon tunani akan al'amuranta ta rasa Gane daga Ina ne ake samun irin wannan
akasin? matsalar dai iri daya ce, Kuma salon tafiyar iri daya ce sai Dan banbancin
da baza'a rasa ba.
Suna yawan waya dasu Ammah da mutanen Jordan, lokacin data Kira Hameeda mita ta
ringa yi Mata akan tana boye Mata wani Abu tunda gashi Saida ta bar kasar kana ta
Kira ta. Da kyar ta fashimtar da ita abun ne yazo da gaggawa itama Bata sani ba
Saida komai ya Zama ready, Kuma tayi ta try din ta sameta Bata Samu ba lokacin ana
fama da matsalar network a area dinsu.

Zahra najin dadin Zama a kasar duk karshen sati a gidan uncle Haisam take yin
weekend din ta, sai Monday da safe motar Embassy take dawo da ita.
Tsakanin syprus science University din wadda take kyrenia city a arewacin syrups
din da capital city din dake Nicosia tafiyar kilometers talatin ne, kawai daga Baya
ma da uncle din cewa yayi ta baro cikin makarantar ta dawo gidansa kawai da Zama
sai a ringa kaita kullum itace taqi tana ganin Kamar abun da wahala yau da gobe sai
Allah daga nesa nesa dai.
Yau ma Monday da wuri motar Embassy din ta kawo ta, tayi gaba da wasu daliban zuwa
mabanbantan makarantu inda suke karatunsu.Ganin da saura Kamar awa aya da rabi
kafin su shiga lectures yasa ta wuce hostel Dan ta aje kayan da tazo dasu.
Tana cikin tafiya tazo gota wani hostel Kamar a mafarki sai taji Kamar ana hausa a
dakin abin ya Bata mamaki tayi Kamar ta koma ta duba sai dai tayi gaba tunda bin
kwakwkwafi haramun ne.
Lokacin da suka Gama lectures din Bata koma hostel ba, karatu suka zauna sunayi da
wata course mate dinta 'yar kasar Lebanon Asseyeh tasu tazo daya sosai saboda itama
akwai nacin karatu ga Kuma kwanyar Allah ya hore itama, uwa uba ga rikon addini
tunda su dai kasar sai a hankali kawai culture din ta rinjayi addinin, Dan wasu Ma
sai kaga suna sallah zaka Gane musulmi ne.
Yamma likis su Zahra suka nufi hostel, haka nan Zahra taji tana son karabi ta wurin
inda taji ana magana da Hausar nan, can ta nufa bayan sun rabu da Aseeyeh.
Very lockly kuwa tayi Dace da wata daga ciki ta fito tana waya bahaushiya sosai.A
shape ce a jikinta ta atamfa sai karamin hijabi a jikinta da alama Kamar fita
zatayi.Dan tsayawa zahra tayi har ta karasa wayar, cikin nuna zallar farin ciki
zahra ta nufeta tayi Mata sallama.
Da sauri ta juyo Jin an Mata magana da Hausa cikakkiya.
"Wa'alaiki Salam" yarinyar ta amsa Mata tana kallon zahrar da murmushi itama a
fuskarta.
"Masha Allah wallahi naji dadin ganinki kema daga Nigeria kike".
Zahra ta tambaye ta.
"Eh daga Nigeria muke muna da Dan yawa zamu Kai goma".
Mamaki ne ya Kama zahra ganin Bata taba ganinsu ba Koda wasa.
"Ikon Allah! Amman dai baku Dade ba ko?"
Kai ta gyada "Mata gaskiya Kam ai ba school daya muke ba mu a Nan mu hudu ne,
sauran suna different Universities ne on transfer mukazo nan daga Sudan tunda can
rikici ya d'ai d'aita Qasar. Zo mu shiga ciki ki gaisa da sisters Dina kafin na
dawo zan fita na samo Ko fizza ne yau bamuyi girki ba".
Ta fada tana juyawa ciki, bayan ta zahra tabi suka nufi ciki.
"Khadijah ! Fatima,! Sajida! Kuna Ina ku fito gashi mun Samu qaruwa".
Kowacce barin abinda take tayi ta nufo kofar tana fadin "Anisa menene?".
Ai kafin tayi magana Zahra tayi Arba da sajida Musa, sajidar ta ta FGGC KAZAURE.
Cikin wani irin farin ciki suka rungume juna Zahra sai kuka Dan wani abune da Bata
taba zata ba robonta da sajidar tun suna cikin bala'in Sudan kafin wayar sajidar ta
salwanta shi kenan suka daina Jin juma Amma kullum zahra da fargaba take kwana har
zuwa lokacin da ta Samu labarin dawowar su sajidar a bakin Maryam Suraj wata
kawarsu.
Kallo saiya koma sama Wai shaho ya dauki giwa ita Mai kawo bakuwa sai duk suka Zama
'yan kallo.
Hannun zahra sajidar ta Kama ta nufi bed in ta da ita tana fadin "wannan wace irin
ranar farin ciki ce bestie wallahi ranar nan tana daga cikin ranekun da bazan taba
mantawa dasu ba cikin tarishin zamana a syprus, pls bestie talk ya akayi haka ta
faru Dan Allah kece ko gizo idona yake mini ne Dan Allah kiyi magana".
Ita dai zahra ba baka sai kunne, ai ita nata mamakin yafi na sajidar sau dari idan
da Wanda Allah ya yiwa gyadar dogo ai ita ce, ba zato ba tsammani Allah yayi Mata
irin wannan suturar bama 'yan Nigeria ba A'a aminiyar ta sukutun ya kawo Mata
kasar, ba abinda zata cewa mahalicci sai godiya take a Nan tayin sujudushshukur ga
Allah. Sai da ta goge hawayenta sannan ta Samu damar magana suka gaisa da sauran
yayin da Anisar ta cire hijabin tana fadin "Ai Kuma saidai kowa ya hakura da cin
fizzar Dan na fasa fitar kawai ayi abinci tunda Naga bakuwar tamu ce ko sister" ta
fada tana kallon sajida.
"Kwarai kuwa ai dukkanku kowa ya kwana da sanin Zahra Muhammad sani ko?".
Gaba daya suka zubawa Zahra idanu suna fadin sosai ma kuwa, niba har gaisawa munayi
ba some times idan Kuna vedio call lokacin muna Sudan" inji Khadijah.
"To ai ita ce gata a gabanki zahiri"
Khadijah ta Dade tana mamakin abun ita sai taga Kamar canza Zahra akayi tasan dai
yesss ba karya zahra Mai kyauce na a bugi kirji a fada, amma sai taga wannan Kamar
ma Bata taba hada dangantaka da 9ja tamu ba, komai nata classic ne.
Nan suka baje hajar hirar yaushe gamo, har kusan karfe goma na agogon kasar suna
tare anan su sajida suka fada Mata gwamnatin tarayya ce ta dawo dasu Nan tunda suna
under scholarship ne shine aka rarrabasu kasa kasa su Allah yasa suka shigo cikin
daliban da aka kawo Nan din.
Har daki suka raka Zahra a Nan ta Basu fizzar tunda Daman tazo da ita daga gidan
uncle Nan ma sun jima kafin su koma.
Ai tun daga ranar wata nutsuwa da kwanciyar hankali suka Samu kyakykyawan muhalli a
zuciyar Zahra, haka itama sajidar duk da Daman ita tana da masu dauke Mata kewar
gida, Suma su sajidar sau da yawa suna bin Zahra a wasu weekend din zuwa gidan
uncle Haisam din Amma su basa kwana duk da irin nacin da zahrar ke musu.
A haka karatunsu ya Mika har sukayi exams, Mama Hanifa taso Zahra taje Mata tayi
hutu Amma Haisam yace tayi hakuri sai hutun karshe session.
A haka suka Kare hutunsu suka Dora da karatu, ba Sajida ba hatta su Khadijah suna
Jin dadin Zama da zahra gashi Sam abin duniya Bai rufe Mata ido ba, Dan ta ko'ina
kudi ne ke sauka a Account din ta ba daga 9ja din ba, ba daga Jordan ba, ba daga
turkey ba, kowa kokarin farantawa zahra yake zuwa lokacin tayi wani irin mahaukacin
kyau na ban mamaki ga wayewa da wayon zaman duniya ta Kara Zama 'yar gayu Kamar me
Dan ba karya matar Uncle Haisam Yar gayu ce sosai kamar Auntyn ta Hasana tasan
yanda ake tattalin jiki matuka.
Har zuwa lokacin ba ruwan Zahra da saurayi bil hasal ko aboki namiji Bata dashi,
akwai wani Dan Syria Omer yaso Zahra Kamar kaddara Amma ta shafawa idanunta toka
tace ba wannan maganar yace to su Zama friends Nan ma tace lah lah.
Dole ya hakura saindai duk inda zasu hadu sai yayi Mata magana idan abu ta saya duk
yawan kudin shi ze biya.

Lokacin hutun karshen shekara Zahra taso zuwa Nigeria tunda taga su sajida nata
Shirin tafiya, ta kwallafa Rai sosai akan zuwan Amman sai Ammah ta hanata zuwan
tace taje Jordan idan hutun ya kusa karewa ta dawo Nan gurin Mama Hanifa ta karasa
Abdul Hakeem zezo ya ganta. Ba haka taso ba da har tayi niyyar Kiran Abban ta fada
Masa sai Kuma tayi tunanin kada Ammah tace ta Kai Kara dole ta hakura tunda Bata
San nufin Ammah din ba data hanata zuwan.
Taji dadin zuwa Jordan din sosai, dan Ummee na Shirin zuwa Saudi Arabia ne ma zuwan
Zahrar ne ya kawo Mata tsaiko, tare suka tafi bayan ta huta, a can suka tarar da
Aunty Nawwara wadda taje zuwa na musamman tunda lokacin ana daf da bikin aurenta
inda za'a kaita Bagdad (Iraq).
Sunyi sati daya zuwa suka nufi makka sukayi Umara, sosai Zahra ta mayar da hankali
gurin addu'a akan matsalolinta na yanda rayuwa ke walankekuwa da ita Bata rasa
komai ba Amma aure Yana neman yafi karfinta dah kudi ko kyau ke sawa mace ta auru
tasan da yanzu ba wannan zancen ake ba, sai dai tasan duk Dan Adam baya wuce tasa
kaddarar sai dai neman sauki gurin Allah s.w.a.
Madina suka koma da suka Gama umarar,basu Dade ba suka koma Jordan.
Lokacin da hutunsu ya taho garewa zahra ta koma syprus. Gidan uncle ta Fara Zama
kafin daliban su dawo tunda ana saura one week ayi resuming ta dawo. Karatu suke
ka'in da na'in ba Kama hannun yaro, amincin ta da Sajida ya Kara karfi tamkar uwa
daya uba daya suke, Dan lokacin da sukaje hutu sajidar har Azare taje ta gaishe da
Ammah ta karbowa Zahra sako.
Duk lokacin da za'a yaye dalibai makarantar tana hada gagarimin taro tana baiwa
best student na kowane department award.
A karshe semester din ne aka hada taron Wanda ya Tara al'umma daban daban daga
kasashen duniya masu Taya 'ya'yan su da 'yan uwa murnar gama karatu, celebration ne
ake na gasken gaske, su zahra dai suna kallon abubuwan tunda wannan shine na farko
da akayi suna Nan lokacin da akazo bada award ne ba zato ba tsammani aka Kira zahra
Muhammad sani daga Nigeria aka Bata award na overall a department dinsu akan kowane
subject.
Wayyo murna gurinsu ba'a magana Dan Zahra kuwa har mukan Dadi tayi data duba taga
yawan daliban da suke a department din nasu Amma ace ita ta karbi best ai abin
murna ne Kam. Sun Sha hotuna da mutanen mu na africa more especially 'yan Nigeria.
A ranar Zahra tayi takaicin karatun nesa da ace a gida ne da Abbanta ko Ammah ko
wani daga cikin yayinta zata danqawa kyautar su sharing happiness din tare Amma Nan
kuwa fa sai da friends da wasu tsirarun mutane Wanda ma ba saninsu tayi ba sukayi
farin cikin, ga Uncle Haisam ma a matarsa da yaran duka sun tafi turkey.
Sai ta waya sukayi murnarsu da jama'ar gida ta tura musu hoton award din ta waya
hotunan da suka dauka.

-----------------

AZAREN KATAGUM

Alhaji Jafar ne da Malam Bukar sai Habibu dan kanwar malam Bukar dake aure a suleja
malam din yake rikonsa tun yana karami mahaifinsa ya rabu da mahaifiyar sa acan
gida Yobe da tayi auren a suleja din ne baban Habibun yace baza'a tafi Masa da yaro
gidan wani ba yayi agolanci, rigima sosai aka kwasa da shi saboda itama tace bazata
bar danta a inda za'a kashe Mata shi ba. Shine mafarin malam din ya dauko shi tunda
ba wasu 'ya'ya yake dasu da yawa ba, a hannun malam ya girma shi yayi karatun boko
har matakin HND.
Jikamshi malumfashj zasuje Daurin Auren 'yar abokin Alhaji Jafar din sannan zasu
shiga Jikamshi dubiyar malamin malam Bukar din daya kwanta kwanakin baya a Asibitin
Ibadan nisa yasa shi majiyyacin ya Hana masu zuwa dubiya sai yanzu daya dawo gida
ne malam zeyi amfani da wannan damar yaje dubiyar.
Tafiya ce mikakkiya Dan tsakanin Azare da malumfashi tafiya ce ba kadan ba Dan haka
sukayi sakko Habibun ne ze tukasu malam Bala anyi Masa Rashi acen garinsu Itas
gadau Yana can.
Cikin ikon Allah Basu rasa Daurin auren ba Dan Sha buying Mai kyau suna cikin garin
malumfashin.
Basu Bata lokaci ba suka dauko hanya sun biya jikamshin sun duba malamin Alhaji
yayi masa kyau ta girma.
Suka dauki hanya sosai Alhaji Jafar ya yaba da tukin Habib Dan baiyi zaton ya kware
irin haka ba.
Sunzo kachako lokacin sallar la'asar yayi guri suka Sami inda akayi wani Dan
masallaci dan matafiya.
Suka firfito Dan gabatar da sallar, malam ne ya Fara gewayawa yayi dahara sannan
Shima Alhajin yayo sukayi alwala suka shiga sallah Saida suka Gama suka fito sannan
Habib Shima ya nufi gurin you daharar Amma shi saiya nufi wani bangaren daban, Bai
jima da tafiya ba sai gashi da sauri Yana Kiran" Baba malam! Kuzo ku gani". Da
sauri suka nufi inda yake harma da wani mutum da suka Sami a gurin Kamar Mai kula
da gurin ne Dan daga gefe da 'yar tiredar shi suka rankaya Habib na gaba suna bin
shi tun kafin su karasa suka hango mutum a kwance Kamar marar Rai.
"Subhanallahi "abinda suka gada kenan suna karasawa kusa dashi sai da suka matsa
sosai suka Gane da ransa Amma Yana cikin wani yanayi, dako dako sukayi aka rasa ya
za'ayi dashi matashi ne ba zefi sana'an Habibun ba saidai a yanayin yanda jikinsa
yake ba alamar wahala a tare dashi. Habib ne ya matsa kusa dashi sosai ya tsuguna
Yana dudduba jikinsa ko akwai alamun duka ko makamancinsa amma babu komai, shawara
sukayi su daukeshi kodan ceton Rai su tafi dashi idan yaso sai su dauki hotonsa a
Dora a social media wata kila a Dace.
Lokacin da suka shigo Azare ana sallar insha'i directly asibiti suka nufa dashi
ma'aikatan nan da Nan suka duqufa a kansa, sai gurin Sha daya Allah ya taimaka ya
kawa kwakwkwaran numfashi.
Sai lokacin suka nufi gida malam ya turo dalibansa guda biyu ya fada musu dakin da
aka kwantar da Wanda suka tsinta din, ya basu kudi saboda abun bukata.
Haka su Abubakar suka kwana da shi sai gurin hudu da rabi na Asuba ya bude idanunsa
Yana kallon bakon gurin da yake ciki ga bakin mutane a gurinsa, yukurawa yayi ze
tashi yqji ya kasa kansa Kamar an Dora Masa dutse, bakinsa ya bude zeyi magana yaji
kwata kwata ya kasa yayi yayi Amma Sam maganar taki yuwuwa sai hakuri yayi ya zuwa
bawa sarautar Allah ido.

,❤️
❤️

AUREN HUCE HAUSHIN

❤️
❤️

✨ MAMAN FATIMAH ✨

✨PAGE THIRTEEN ✨(13)

__________Washe gari daga gidan Alhaji Jafar Abdul Hakeem da magaji suka kawowa su
Abubakar abinci Asibiti, sun tausaya bawan Allah nan sosai Dan zuwa lokacin sun
fuskanci baya magana Kuma jikin ma baya motsuwa yanda ya kamata, toilet ma sai da
sukayi Kama Kama suka kaishi, a haka su malam suka shigo Asibitin tare dasu Malam
Mudi, Basu Dade da zuwa ba likitoci suka shigo round sun tambayi menene Asalin
ciwon to su dai sun fada musu Yan suka hadu dashi Dan Basu da masaniyar komai
akai.
Gwaje -gwaje suka rubuta ayi Masa Dan binciken lafiyarsa.
Basu Dade ba suka koma gida saboda a ranar Alhaji Jafar ze shiga Bauchi suna da
meeting da gwamna Amma ya bar kudade a hannun Abubakar saboda magani da sauran
hidimar Asibitin.
Da yamma Habib ma ya shigo ya duba marar lafiyar nasu, Wanda har lokacin baya
magana.
Likitoci sunyi iya nasu binciken basuga komai ba a tare dashi, sai dai rashin
maganar kawai Amma Kuma Yana Jin komai da ake fada.
Bayan sun Gama bashi taimakon daya kamata suyi Masa suka sallame shi, Magaji ne ya
dawo dasu gidan malam, Nan dakin malam na waje aka ajeshi tunda aka dawo dashi gida
malam ya dukufa da Yi Masa addu'a Dan yayi bincike akan lamarin ya fashimci inda
matsalar take, har Taraba ya tafi gurin malaminsa da yayi karatu a gurinsa ya fada
Masa matsalar yaron, kwanansa biyu ya dawo Azare aka dukufa da rokon Allah da
maganin hausa, haka zalika Alhaji Jafar ma Yana taho Masa dashi daga wani Islamic
chemist da yayi musu bayanin matsalar yaron a can Abuja.
Cikin ikon Allah ba'a rufe wata hudu ba ya Fara magana sai dai idan yayi sau daya
sai a wuni bai sake wata ba.
A haka aka dunga bashi taimakon har Allah yasa ya dawo normal Yana magana. A
lokacin ne malam ya zauna dashi da Habib suka fada Masa inda suka same shi da halin
da yake ciki a lokacin shiru yayi kafin yace musu shi dai yasan wata Rana Yana gida
ciwon Kai ya takura masa har ya kasa fita, jzuwa dare yasha magani ya kwanta, to
tun daga lokacin bazece ga yanda akayi ba shi dai ya farka ne ya ganshi a Asibiti
tare dasu a hankali Kuma ya Gane a wani garin ma yake daban ba garinsu ba. Lokacin
da Alhaji Jafar yazo garin malam ya fada Masa komai yanda sukayi da Mahmud din,
Alhajin yasa aka Kira shi ya Kara jajanta Masa sannan ya nemi ya fadi garin nasu a
mayar dashi Dan da gani Dan manyan mutanene.
Nan fa ake yinta Dan kekashe kasa yayi yace shifa ya manta sunan garin nasu akayi
juyin duniya yace sai dai ko Nan gaba idan Allah ya nufa ya tuna, abinda ya tuna ma
daga baya tunanin yazo Masa, haka suka hakura badan sun amince ba bayan ya tafi sun
tattauna da Malam din akan lamarin inda Suke hasashen ko bacin Raine ya baro shi da
gidan ya gwwmmace yayi zaman sa a Nan kafin ya huce ya nemi komawa gidan.
Nan yaci bada da Zama da Malam Yana kwasar ilimi kala kala.
Nan da Nan ya Zama Dan gida suka dinke da Habib duk da ze iya girmar Habib din da
Kamar shekara biyu dan yayi Kamar sa'an Abdul Hakeem.
Bai cika wata shida ba Allah ya kawo aikin NGOs din Nan Wanda aka sakewa makarantar
fasali da tsari suka sayi wani katon fili na makudan da sunan makarantar akayi gine
ginen hostel din Yara suka dauki ma'aikata suka gyara tsarin karatun saboda kwazon
Mahmud har co-ordinator din Shirin Muhammad Sameer ya dauke shi aika a shiyyar
Katagum local government din ya Zama shine idon su a Nan, tunda ya iya rubutu da
karatu. Habib ma Yana bada gudunmawa sosai a aikin duk da Shima nasa aikin da
ma'aikatar ruwa ta Nan local government din tasu.
Wannan kenan.

____
Syprus.

Zuwa lokacin su zahra karatu ya Mika, tun tana saka Rai da zuwa Nigeria har ta
hakura Kuma abinda ya Kara Bata mamaki sau biyu Abba da Abdul Hakeem suna zuwa
ganinta idan harkar kasuwanci ya kawo sun Istanbul.Amma Koda wasa Basu taba ce
Mata ga lokacin da zataje gida hutu ba.
A haka har suka hada shekara biyu a kasar, da gaske gida take son zuwa shi yasa
lokacin da hutunsu ya gabato batayi shawara da kowa ba ta kama shirin barin qasar,
online tayi komai Kamar su Sajida sai da komai ya Zama daidai sannan ta fadawa
Uncle Haisam Shima bai hanata ba yasan tayi hakuri, Mama Hanifa ma ta waya ta fada
Mata Nigeria zata wuce kawai, haka Ummee ma ta wayar itama ta fada Mata taso ta
hanata Amma sai tayi wani tunani kawai tayi shiru kudade dai to tura Mata masu yawa
Wanda har saida Zahrar ta Kara kiranta tana tambayar kudin ma meye haka da yawa?
Tace ta turo Mata ne kawai ko idan take zatayi wani abun, godiya tayi Mata sosai
hakan Kuma dabi'ar Zahrar ne komai kankantar Abu idan akayi Mata alherinsa zatayi
godiya Kuma ko waye ta Bata Bata duba ai iyayene.
Kwana biyu suka Kara da akayi hutun shima visa din su Khadijah ne Bata Zama ready
ba.
Lokacin da jirginsu ya dauka a Aminu Kano international airport taji ta sauko ta
shaqi iskar Nigeria ji taji Kamar a Aljanna take lallai kowa yabar gida gida ya bar
shi, saukar safe sukayi wurin karfe Sha daya ba yanda su zahra da Khadijah Basu da
zahra ba akan ta zauna ta Dan huta kona awa daya ne a gurin sajida Amma tace A'a
Azare tayi Kira su Anisa ne da Fatima suka bi Sajida Su dan huta kafin driver dinsu
ya karaso tunda ba nisa tsakanin kazaure da kano, Kuma Gwammaja kan hanya ne.
Shatar taxi Zahra ta dauka ta kaita Kano line Dan direban taxi din ta tambaya Ina
zata samu motar zuwa Azare ya fada Mata akwai gurare Amma ita Kano line yafi Mata
kusa.
Har cikin Tasha Mai taxi din ya shiga da ita gurin motocin arear Bauchi, tayi Masa
godiya sosai ta kuma Kara Masa kudi akan yanda ya bukata.
Away biyu da rabi Mai kyau matarsu zahra ta shiga Azare tun shigowa su ta Fara
ganin 'yan canje canje a garin Kamar sabbin titina street light na solar sai gine
gine masu kyau. Masha Allah ya dunga fada a zuciyar ta, Mai adai daita ta Sami ta
fada Masa inda ze kaita, tunda suka tinkaro unguwar naji want irin nishadi ya
mamaye ilahirin zuciyar ta, unguwar tasu ma an Sami cigqba sosai ga wasu gine gine
sabbi masu kamar makarantar kwana har da gate a gurin gidan malam Baba gidansu ma
gaba daya ya canza anyi Masa mahaukacin gyara tamkar sake sabo akayi.
Lokacin da Mai adaidatan ya sauke ta dai dai lokacin ya Hamza ya fito da alama wani
gurinzeje Nan kusa.
Da madaukakin mamaki yake kallon zahrar shi dai Koda Wasa baiji ance zatazo ba Kuma
yasan da ansan da zuwanta ai Bala driver ko su suje su daukota a kanon. Da sauri ya
karasa Yana Mata sannu da hanya ita Kuma tana gaishe shi, shi ya biya Mai Dan sahun
yace ta shiga ciki za'a shigo mata da kayan.
Tunda ta shigo gate din tasan eh lallai gidan ya lashe makudan kudin Dan gaba daya
an canza fasalin gidan, tunda ta shigo gidan Mai gadin ke kallon zahra Dan shi dai
sabo ne Bai Dade ba ta dai gaishe shi tayi gaba Nan ma wani mamakin ya rufe shi Jin
tayi hausa radau Dan shi dai ze iya rantsuwa da abinda ze kashe shi wannan ko zo
Bata sani ba da Hausa.
Ai mamakinta Bai karu ba Saida ta shiga cikin Nan dai ko rantsuwa tayi ba kaffara
sabbin gine gine ne dam kwata kwata inda parts din su na da yake gurin ba komai sai
filing da shuke shuken flowers.
Lokacin data shigo gidan ba motsin kowa kamar ba mutane a gidan kowa ne kofar part
Yana rufe Ido ta lumshe tana shakar iska Mai Dadi ta gidan. Idonta na nufen Nan
tana tsaye Dan ita batasan wane dakin zata nufa ba tunda da gaske ta Zama bakuwa a
gidan, maganar Ibrahim taji Mai bin magaji Yana fadar "kai!" Da karfi ya juya a
guje Yana fadin Ammah! Ammah! Kizo ga Aunty Zahra a tsaye a kofar part din Mama".
Magaji ne dake zaune a falon yana kallon wani series na 'yan Lebanon ya dago Kai
da sauri daga kallon T.V Yana tsaki Yana fadin Amma Kai ba karamin soko bane dallah
Banda tsabar hauka zaka wani ware murya Kama kwala Mata akan shashancin Kawai Wai
zahra A'a wat......"
Maganar ce ta makale Masa lokacin da zahrar ta kunno Kai ciki da sallama a
bakinta, dan a bude yabar kofar saboda zumudin ya kawo labari.
Ammah ce ta fito da sauri tana fadin Wai Kai har abada Ibrahim bazaka giirm..."
Idonta ya sauka akan Zahra wadda tayi tsaye ta langabar da Kai tana kallonsu,kafin
Ammah ta dawo daga duniyar mamaki sai Jin zahrar tayi ta rugumeta ta saki
shashhshekar Kuka.
"Ikon Allah!" "Ikon Allah!"
Abinda bakin Ammah ke fada kenan, ita Kuma zahra ta riketa kamar zata bace Mata.
Mamace ta shigo dakin da sauri tana fadin "Ina zahrar yanzu sahura ta shiga ta fada
min taga Zahra ta shigo yanzu".
Ta fada tana kokarin Zama idanunta suna kan Zahrar.
"Wallahi kuwa Mama kin ganta Nan yanzu Ina daki Ibrahim ya shigo a guje Yana fadin
gata Nan a waje nayi zaton shashancinsa ne Saida na fito na ganta kwatsam ba zato
ba tsammani ba wani bayani".
Ammar ta saki da Dago kanta tana goge hawayenta tana fadin. "Haba Ammah an kaini
wata uwa duniya an manta Dani idan nace zanzo ace A'a ni Kuma wallahi na gaji gida
nake so shi yasa naki fadawa kowa na tasho kawai na gaji da ganinku a waya ni
zahiri nakeso". Ta fada tana maida kanta jikin kafadar Ammar.
Tunda ta Fara magana Mama ta kureta da ido dan wani irin mahaukacin kyau taga
Zahrar ta kara, ga wata irin gogewa da wayewa tamkar ba Zahrar data sani ba komai
nata ya canza har ma salon yanda take magana.
"Ai kodai ki daina irin wannan kasadar ta tahowa daga uwa duniya irin wannan ke
kadai sai ki fada ko addu'a ayi Miki sannan aje a daukoki daga Kano, Amma fa Ina
tunanin a motar haya kikazo garin Nan ko?" Mama ta fada.
Kai Zahra ta gyada alamar eh, dai dai lokacin Yara suka shigo da jakunkuna ta guda
biyu.
zaunawa tayi tana gaishe dasu Ammah, sannan magaji yayi Mata sannu da hanya Yana
fadin "irin wannan surprised haka uktiy? kin ganki kuwa kin juye Balarabiyar ki sak
kodan kina cikin 'yan uwa dangi farare irinki"
Dariya Zahra tayi Masa kawai.
Ibrahim ne ya shigarwa da Zahra jakunkunan ta dayan bed room din Ammah, ya fito ya
nufi kitchen ya kawo Mata ruwa da lemo, ya koma ya dauko warmmers din abinci sai
Ina yaka saka yake da zahra har Mama na Masa Dan biki.
Saida tayi wanka taci abinci sannan suka zauna da Ammah bayan sallar insha'i, hira
sosai Suke Amma duk yawanci korafin Zahra ne na hanata zuwa.da Ammah tayi, a haka
Abdul Hakeem ya samesu Shima yayi mamakin ganin.zahra kamar a mafarki Dan lokacin
da ta dawo baya nan yaje Darazo ganin ganin wasu gonaki da Ya Hassan ya saya a
can.
Sun raba dare suna Hira da 'yan uwanta a falon Mama sunyi waya ma da Abban tunda
lokacin Yana aAbuja, Shima yayi fada sosai lokacin da Ammah ta Kira shi ta fada
Masa ga zahra tazo.
Sai da ta kwana biyu tana huce gajiyarta, tana jikin Ammah kullum kamar kamar wata
'yar yaye, duk 'yan uwan kowa nan nan yake da ita, kowa kokarin kyautata Mata yake
yi.
Sunyi waya da Aunty Hasana tace Mata tana nan tafe Jos zatayi Mata sati Amma sai
Abba ya dawo, haka kusan Kullum sai sunyi waya da Hameeda.
Ranar data kwana biyar ne Ammah ta takura Mata akan ta leka makwabta ta gaishe wasu
da yawansu sun shigo, wasu Kuma sun turo yaransu suyi Mata sannu da zuwa harda abin
hassafinsu.
A waya Zahra ta Kira mujiba akan ta Shirya ta rakata Nan gidajen su shishhiga a
gaisa.
Doguwar Riga ta saka kirar Dubai blue black Mai duwatsu tun daga sama har kasa ta
saka plat she dinta fari tas ba wani makeup da tayi powder kawai ta saka sai
lipsglow turarenta na Alkawari ta fesa Mai sanyi kamshi, Kota sa ko Bata Saba komai
na sutarata kamshin yake.
Ta fito Kamar wani dawisu Dan da gaske zahra mai kyauce komai nata Kamar ita ta
zabarma kanta. Tunda ta shiga bedroom din Ammah ke kallonta data ita sai halicinta
suka San abinda zuciyar ta ke ayyana Mata a fili Kuma sai tace "Masha Allah! Har
kin shirya?"
Kai ta gyada Mata tare da fadin "Eh Allah Dan dai kin matsabe Ammah Allah da Babu
inda zani sai nayi sati biyu ko gate ba leka ba".
Wata leda Ammah ta Miko Mata tasa hannu ta karba tana tambayar "na waye?"
" Idan kunje gaida Baba malam saiki bashi tasa tsarabar turarika ne".
Murmushi Zahra tayi har fararen hakoranta suka bayyana tana fadar "wace irin
tsaraba Kuma Ammah nida ba Hajji naje ko Umara ba daga makaranta fa na dawo hutu".
"To Miko min kije hannu sake ki gaisa ki taso tunda Zama da turawa ze saka ki koyi
rowa" ta Mika Mata hannu alamum ta Bata ledar.
Dariya tayi Zahrar tana fadin "Allah ya Baki hakuri Ammah Ina ni Ina koyo rowa a
garin wasu alhalin na gaji kyauta gaba da baya Allah qara lfy". Ta nufi kofa tana
fadin "saina dawo"
"Allah ya tsare Kya gaishe da Malam din.
Gidan su mujibar Zahra ta Fara shiga suka gaisa da Mamanta sannan suka shishhiga
gidajen suka gaisa, gidan Malam ne na karshe, a hanya Zahra ke tambayar Mujiba
ginin da taga anyiwa Almajiran Baba Malam? nan ta fada Mata iya abinda ta sani
akai.
A cikin rumfar canopy din da Malam yake bada karatu Zahra suka tarar da Malam din
suna magana da wani matashi sukayi sallama a bakin rumfar a tare malam da Wanda
Suke magana suka amsa sallamar, Yana fadin Bari naje na karbo yanzu in Sha Allah.
Juyowar da zeyi sukayi ido hudu da Zahra wallahi ita dai batasan lokacin data rufe
idanunta ba Dan wallahi wani Abu ta gani a idonsa Wanda Bata taba gani a idon kowa
ba take zuciyarta ta wani harba a cikin girjinta. Ga wani mayen kamshi daya cika
Mata hanci ita dai Bata San ya wuce ba Saida Mujiba ta tabata tana fadin ki bude
idonki "Zahra menene?".
Ajiyar zuciya tayi a hankali tace "ba komai muje"
Cikin rumfar suka shiga suka zauna daga gefe suna gaida malam din.
Amsawa yayi Yana fadin Masha Allah da bakin turai ne Fatimah yaushe Kika shigo ban
sani ba kodon Alhaji Yana Abuje shi yasa bani da labari".
Sunkuyar da Kai zahra tayi tana fadin.
"Ban Dade ba Baba Malam yau kwanana biyar da dawowa, Saida na huta nace Bari nazo
na gaisheka"
"To Masha Allah! Allah yayi Albarka ya bada sa'ar abinda akaje nema, ai ba'a Gama
karatun ba ko?".
"Eh da sauran shekara daya karatun ne da banbanci da namu na nan tunda su basa
yajin aiki".
"Wannan haka yake, Allah yayi jagora ya bada sa'a"
"Amin" suka amsa tashi zahrar tayi ta karasa gaban malam din ta aje Masa ledar
turarikan dake hannunta tana fadin "gashi Baba ba yawa"

Godiya yayi sosai kafin yace "ku shiga ku gaisa da zainabu batajin Dadi tana fama
da masassara tun jiya".
"Allah ya sauwake"suka fada suna fita faga cikin rumfar.
Tunda suka shigo gidan suka sallama Amman gidan shiru a falon ma ba kowa uwar dakin
Zahrar ta nufa tunda gidan ba bakonta bane, can tsakiyar gado ta hango Iya Abun
jikinta yana ta kadawa tana ta rawar sanyi da sauri Zahra ta karasa kusa da ita
tana Mata sannu Amman Sam ta kasa amsawa hannunta Zahrar ta Mika ta taba jikinta
sai taji Kamar wuta.
"Ya Salam".
Ta fada tana nufar falon inda tabar mujiba tana fadar "Bari na fadawa Baba Malam
jikin Kamar ya matsa gaskiya". Tayi waje ba tare data jira taji abinda mujibar
zatace ba.
Tafiya take cikin sauri burinta ta Isa gurin malam ta fada Masa abinda kenan.
Ita dai Batasan yanda akayi ba sai ji tayi ta bugi kirjin mutum da kanta abinda
yayi sanadiyyar ta tafi taga -taga zata Fadi taji an fusgota da Dan qarfi kafin ta
Kai kasa sai ganin ta tayi rungume kane kane a jikin koma wannene an saka hannu
biyu an zagaye bayanta.
Kici kicin kwace jikinta ta shiga yi data Samu ta Sami kanta coming fishing ta daga
ido taga wane Mai tarar aradu da fadin Kaine ya kwakumeta haka da yammcin Allah
wata'ala ta sauke Masa zallar rashin mutunci duk da ba halinta bane, tana daga Kai
sukayi arba dashi ya kafeta da idanunsa masu wani irin kaifi da mugun kwarjini a
cikin nata idanuwan Wanda a ganinta dashi na farko ya yamutsa duniyar ta

.AUREN HUCE HAUSHI


MAMAN FATIMAH

Page Fourteen 14.


-----------kusa da ita ya matso sosai Kamar ze Kara rungumo ta, da sauri tayi baya
tare da rufe idanunta ruf zuciyarta na Kara speed, a hankali yayi magana saitin
kunnanta "ki rinqa duba gabanki idan kina tafiya Mana kada kiyi Mana asara pls".
Ya fuske yayi wucewarsa ciki Bai Kara bi ta kanta ba. Nan inda ya barta Bata iya
motsawa ba, wani Abu ilahirin jikinta keyi itafa ji take kamar kafarta bazata iya
daukar ta ba wallahi,.shi Kuma wanene wannan a tare da malam haka? A Ina ya Samo
shi Dan a gaskiya baiyi Kama da kolo ba Sam to waye shi?". Tambayoyin dake Mata Kai
kawo kenan a kwakwalwarta daga ganin mutum haka kawai ze nemi yayi Mata shiga hanci
da qudundune,ga wani irin kwarjini a cikin idanunsa da Bata taba gani a gurin wani
namiji ba. Bata ankara ba taji maganar malam Baba Yana fadin " A'a Fatimah ya Kika
tsaya a Nan ko wani Abu kike jira?"
Da sauri ta bude idanun tana kallon malam da wani yana binsa a bayan.
"A'a ba komai Daman gurinka zani jikin Iya Abun ne Naga kamar ya Dan matsa tana ta
rawar sanyi".
Ta fadan kanta na kallon kasa kamar marar gaskiya, dan ji take kamar malam din Yana
Jin mayen kamshin turarensa da ilahirin jikinta keyi.
"To Babu laifi muje ciki, yanzu Mahmud yaje ya dauko abokinsa don ya kara dubata
tunda jiya sunje Asibiti da Halima matar malam Mudi ance zazzabin typoid ne yake
damunta, to da jikin yaki Dadi ne za'a Kara bincike ko na cizon sauro ne
zazzabin".. suka wuce ciki sannan zahrar tabi bayansu zuwa falon Iya Abun Kamar
kazar da kwai ya fashewa a ciki. Yana tsaye daga bakin kofar ta waje ya harde
hannuwansa a kirji kamar Mai tunanin.
Ganin malam din da salahuddeen sun shigo ya daga kansa Yana amsa sallamar su.
Mujiba ce ta leko tana fadin" ta tashi din gata Nan fitowa".
Bai shiga falon ba Saida malam ya Fara shiga sannan suka biyo bayansa.
Sannu salahuddeen din yayi Mata ya dauki jinita take a Nan yayi Mata gwajin
maleria ai kuwa ita ke damunta har ta Kai || +.
Allura ya dauko Yana fadin " malam allura za'a yi Mata emal, idan Allah yasa an
dace shi kenan idan Kuma Bai sauka ba sai ayi Mata Attusunate, amma muna fatan
Allah yasa a dace ma".

"Allaumma amin ya Rabb". suka fada su duka. Magunguna ya rubuta Mata na ulcer da
tayi masa complain na ciwon girji da gefen kafadar ta, sannan yayi Mata Allah ya
sawaqe suka fita.
Har magariba su zahra suna gidan Baba malam, tun bayan fitar su malam ba dadewa Iya
Abu ta koma daki ta kwanta Zahra ta rufeta da wani qaton blanket barci Mai nauyi ya
dauketa.
Nan falon suka zauna suna Dan tattaunawa da junansu, da tafiya zasuyi Majiba tace
su zauna zuwa wani lokacin tunda ansan suna Nan Dan lokacin da zasu shigo mujibar
taga kaninta Mubarak tace ya fadawa Mama suna gidan Baba malam.
Duk hirar da Mujiba ke yiwa Zahra Sam hankalinta baya tare da ita ta tafi duniyar
tunanin abinda ya faru dazu da Wanda aka Kira da Mahmud wai ita Zahra ce kwance a
kirjin wani namijin daba muharraminta ba, Kuma ba wani mataki data dauka Koda kuwa
na kad'a Masa warning ne yanda gobe baze Kara marmarin rungumar wata ba, Amma Wai
sai gata ta b'ige da shakkar idanunsa abinda kaf tarihin rayuwar ta hakan Bai taba
faruwa da ita ba, ga wata faduwar gaba ta ba gaira ba dalili data sameta yanzu,
ganin nan biyu da tayi Masa duk Abu daya takeji a kansa.
Wani wawan tsakin Zahrar tayi Wanda ya tabbatarwa Mujiba Bata tare da ita duk zubar
da takeyi kamar 'ya'yan kanya.
"Keda waye kike tsaki haka kuma?".
Majiba ta fada.
"Kedai kawai bari kawai ba komai. Ta fadar tare da you kwafa ta tashi tsaye tana
fadin
"Tashi mu wuce gida tunda Naga wannan barcin na Iya Abu bana Kare bane, inaga har
da allaurar barci yayi Mata gaskiya".
A kofar gida suka yiwa malam sallama Yana ta Sanya musu Albarka.
Tun daga ranar Zahra Bata sake fita ba tana gida saidai lokaci-lokaci Mujiba na
shigowa, a ranar data cika sati daya Abbansu ya dawo murna ba'a maganarta gurin
Zahra, duk da tana ganin shi a can syprus din idan yaje Amma hakan bai Hana sun Kai
wani lokaci ba suna tattaunawa irin ta d'a da mahaifi.
Saida Zahra tayi sati biyu sannan ta nufi Jos gurin Aunty Hasana.
Taji matukar dadin zuwanta Jos din. Dan har gidan Aunty Jana sukaje da Yara tunda
lokacin da akayi bikin Bata Nan. Duk inda ya kamata taje taje har gidansu Mama taje
haka ta kaiwa jannifer ziyara lokacin sunyi hutu tana karatu a Nan University ta
Jos.
Maganar samari da gaske ta sakata side idan ka ganta tana magana Mai tsawo da
namiji to ka tabbatar dan uwanta ne ko wani Mai qirma a idanunta.
Satinta daya a Jos suka taho tare da aunty Hasanar da Yara Wanda a satin sukayi
hutu, bayan dawowar ta daga Jos ne su Hameeda sukazo hutun semester.
A lokacin ne Salma ta fito mata a mutum sak, ta nuna da gaske Bata yin zahra abinda
yaso ya kawo b'araka Mai girma kenan tsakanin Mama da Ammah Dan da gaske an Kai
hakurin Ammar karshe, maganganu Salmar ta ringa saki kamar lokutan baya, sai dai a
wannan karon Zahrar ta nuna Mata jiya fa ba yau bace, idan da tayi tolerating na
nonsense din ta a yanzu Kam dai dai take da ita tunda Bata Jan girmanta a gurinta,
abinda ya Kara harzika Salmar lokacin da Zahra ta kalleta tayi tsaki tace "Wai
wannan ce mace,kina duba mirror Kuma kina ganin kanki kuwa?gara ni da har kike min
gorin ana saka aurena ana fasawa, Ina laifi tunda har ana ganina ana sona, kaddarar
Babu mijina a cikin su ce take rabani dasu, kefa ko Kare Bai taba zuwa yace Yana
sonki ba, baga kanwarki Nan ba Ina cewa har anzo tambayar aurenta? kije kiji da
abinda ya dameki Zaki zauna kina fada da kanwar bayanki".
Tana Gama fada Mata maganar ta nufi hanyar ficewa daga dakin. Cikin fushi salmar
tayo kan Zahrar ta fardota baya saura kadan ta Fadi dai dai lokacin Kuma sahura ta
shigo zatayi musu sharar yamma ta tarar da wannan badakalar, da sauri ta shiga
tsakanin tana Basu hakuri ta Kama salmar ta fita da ita daga dakin tana faman zagin
Zahrar abinda ya janyo hankalin Amma dake main kitchen din gidan tana yiwa Abba gas
meat saboda Yana sonsa sosai yawanci idan Yana gida kusan duk dare sai anyi Masa
shi.
Da sauri ta fito tana tambayar "me yake faruwa ne?"
Sahura ce ta fada Mata abinda ta shiga ta gani tsakanin Zahra da salmar, juyawa
kawai Ammah tayi ta koma taci gaba da aikinta Bata Kara lekowa ba tanaji Mama ta
fito tana fadan daman ai ba tun yau ba ta fuskanci Zahra ta Raina Salma, Kuma komai
runtsi dai Salma ai gidan ubanta ne Nan ba Mai hanata sakewa.
Zahra ce ta fito zata wuce zuwa part din Ammah,har ta gota Mamar batace komai ba,
Mamar tace.
"To fiqe kafi qaya tsini da Kika Samu guri kina yanda kikeso a gidan wallahi duk
rintsi bazaki Kai matsayin 'ya'yan gida ba, tunda har abada ba'a canzawa tuwo suna"
Har zahra tayi kamar ta maida Mata martani sai taji bazata iya ba babba babba ne,
kawai ta shige part dinsu.
Har Mama ta juya taji maganar Ammah daga bayanta, dan harga Allah batasan Ammah ta
fito main kitchen din ba, Sam duk da tana jiyo kamshi ta dauka a can part dinta
take aikin.
Bata juyo ba Amman ta tsaya.
Ammar tace
"Haba Mama ban zaci haka daga gareki ba wallahi, cewa nake da Zahra da su Hameeda
dauka daya ne a gurinki, ai saiki tambayi meya hada fadan?kiyi musu fadan gaba daya
ba wai ki nuna Salma itace taki ba, kina fadin maganganu irin haka ai na dauka ni
duk binda lauje ya yayo a gidan Nan ya kamata ki dauke shi ciyawa ne na gode amman
ki sani Banda komai nufin Allah ne Zahra tafi karfin ace Mata 'yar karere tunda Mai
gidan ne da kansa ya karbo rikon lokacin da aka nemi tafiya da ita kema Kuma sheda
ce kinsan su waye kakanninta ba bakinki bane, dukiya idan ana gadonta kinsa Zahra
'yar mun gada ce, ko shi Wanda kike takama da dukiyar tasa yasan tazarar da nisa a
tsakaninsu da kakanninta idan kina tunanin karya ne idan yazo ki tambaye shi ze
Baki cikakken bayani".
Bata jira taji abinda mamar ke kokarin fada Mata ba tayi gaba abunta ta nufi part
dinta.
Tun daga ranar Ammah ta daukewa Mama wuta gaisuwa kawai ke hada su, a kwana na biyu
da Mama ta karbi girki ta kasa hakuri ita abin yafi damunta ta fadawa Abban Ammah
Bata Mata magana, yayi mamaki matuka da gasken gaske Dan wannan shine karo na farko
da irin haka ta faru da matan nasa duk tsawon shekarunsu. Bai taba rabasu akan sun
Sami matsala ba Koda wasa, dan haka ya Kira Ammah a waya yace tazo part dinsa Yana
son ganinta.
Batayi mamakin ganin Mama a zaune ba tasan za'a Rina tunda kaf tasan halin Mama na
zahiri.
Gaishe da Abban tayi suka Kuma gaisa da Mama, tambayar ta Abban yayi ko akwai
abinda ya hadasu da Ammah ne?.
Ba wani kwana kwana ita Daman tun can baya Bata da munafurci ko kadan. Dan haka ba
wani ta fadawa Abban duk abinda ya faru tunda Saida ta tutsiye Zahrar akan ta fada
Mata abinda ya hadasu da Salma da kuma abinda mamar ta fada, shi kanshi Abban yayi
mamakin abinda Salma tayi sosai, itama Mamar ya nuna Mata kuskurenta na fadar
wannan maganar ya Kara da cewa.
Ban tabi yiwa zahra kallon ba nine na haifeta ba, bil hasal ma shine dalilin da
yasa ban aura Mata Daya daga cikin 'ya'yana ba, ita kadaice ba uwa ba uba tun
batasan inda kanta yake ba, mu ta sani a matsayin iyaye sauran yaran Kuma 'yan
uwanta. Idan na aura Mata wani a cikinsu ba zata Zama feel free tare da ni ba, idan
damuwa ta shiga ba Wanda zata fadawa kinga ai anyi adoh badan kyau ba".
" Haka ne suka fada.
"To karna Kara Jin makamanciyar irin wannan maganar, ba Wanda ze kawo min rarraba
kan iyalin gidana. Zahra 'ya tace kawai na saka sunan mahaifinta ne Dan haka
shari'ar musulunci tazo dashi, badan in nunawa duniya bani na haifeta ba, a kiyaye
kodon gaba".
"In Sha Allah".
Suka fada.
Bayan tafiyar iyayen yasa suka turo yaran yayi musu fada sosai sanan ya Kare da
nasiha.
Tun daga lokacin abubuwa na zahiri sukayi sauki sosai.
Kusancin Zahra da Hameeda ba abinda ya taba shi saima Kara shakuwa sukeyi a kullum
suna Jin dadin butun, Zahra suna waya sosai da Ummee da Mama Hanifa harma da uncle
Haisam a wasu lokutan.

Lokacin da hutunsu ya kusa karewa duk sai Zahra ta nemi walwalarta ta rasa ko da
yaushe kamar marar lafiya ana saura kwana biyu ta tafi Ammah ta matsa Mata taje
Kiran da Baba malam yake Mata, dan sau kusan uku yana turo Yara tana cewa gata Nan
Amman sai tayi burus da zancen.
Har dai ta Kai Ammah karshe tayi magana. Hameeda tace ta rakata suje tare, yau
gurin malam din ba kowa ba Kuma rumfar karatu tunda ranar basa karatu. Gurin ganawa
da mutane suka sameshi su Habib suna ta gyaran Shirin kantar littafai.
Da sallama suka shiga suka gaishe da malam din sannan suka gaishe dasu Habib, sai
sukayi shiru.
Malam ne yace "Zahra'u Ashe lokacin komawar taki har yayi ko?"
Kara risinawa tayi tana fadin "eh lokacin yayi yayi Baba gobe zan tafi in Sha
Allahu amma a Istanbul zan tsaya sai wani satin zan wuce syprus din".

"Masha Allah. Allah ya taimaka, ki Kara hakuri akan lamuranki duk wani bawan Allah
na kwarai sai Allah ya jarabce shi Dan ya gwada imaninsa ki dauki abinda yake
faruwa dake Daman haka Allah ya rubuta Miki taki kaddarar kada ki yanke kauna daga
Rahamar Ubangiji. Ga addu'oi nan da littatafan addu'a ki tafi dasu ki ringa yinsu
Kuma kada a shagala da ambaton Allah a duk inda aka Sami kai, Allah yayi Albarka ya
bada nasara ya kiyaye hanya".
"Allahumma Amin suka fada a tare".
Habib malam ya yiwa magana ya Miko ledar da aka saka sakon nata, Hameeda ta karba
suka Kara yiwa malam godiya suka fito suka shiga cikin gidansa Zahra ta Kara duba
jikin iya Abun ta Kuma yi Mata sallama.
Basu koma gida ba, gidan su mujiba suka shiga Bata Nan ma sai Maman ta suka barwa
sallahun tafiyar zahrar suka nufo gida, sunzo dai dai masallacin gidansu ne sukaga
Ya Abdul Hakeem da Dodon Zahrar a zauna a kan carpet karami a gefen masallacin suna
hira Kai da gani da kyakykyawar alaqa a tsakanin su.
Gaishesu sukayi suka wuce, Hameeda ce ta kalli Zahra tana fadin "Kinga wancen Guy
din yanda Salma ta mutu kansa ba magana! lokacin data Fara ganinsa munzo hutu
wallahi kamar zata zauce akansa sai da Mama ta taka Mata burki taci Mata mutunci
akan ta rasa Wanda zata so sai Almajira Wanda ba'a San asalinsa ba, duk yanda taso
ta nunawa mamar wannan da banbancin da irin Wanda ta sani amma Sam taki fahimta Dan
har so tayi tayi Mata duka tana fadin Dan lalacewa ta rasa Wanda zataso sai fakiri
Mai allaziwahidin Dan salon Abba yaji ya Goya Mata baya tunda Wai ance sune suka
kawo shi garin bandai San kan labarin ba gaskiya". Ita dai Zahra Bata tofa tataba
daga uhm sai umh umu uhm, har suka karasa gida.
A Daren sun raba dare suna Hira da Ammah a Nan ta dunga yi Mata magiyar ta daure
taje gurinta ko zuwa karshen shekara ne ta ganota ba ta tura Mata Ya Abdul Hakeem
ba.

Karfe shida Mai kyau sun dauki hanyar Kano ita da Ya Abdul Hakeem da Hameeda da
magaji.
Nan suka zauna da zahra suna ta Hira kafin lokacin tashin su yayi, in da wani Abu
da ya damu Zahra a gurin Bai wuce kallon da wani matashi ya kureta da Shi ba, duk
inda zata dago Kai sai sun hada Ido dashi, Sam ya hanata sakat da idanunsa idan ba
idanunta kemata gizo ba har wani lumshe ido yake da wani kankance su. A haka har
lokaci ya cika aka Fara shiga jirgin hand bag ce kawai a hannun Zahra tunda kayan
an tafi dasu tun zuwansu lokacin da ta juya ta Fara tafiya ba zato taji hawaye a
idanunta abinda ta dunga kokarin kar tayi kenan tun daga gida lokacin da Auta
Musaddiq ya fasa Kuka da suka taso Amma sai gashi ta kasa jurewa itama Saida suka
zubu, juyawa tayi kadan lokacin da zata hau steps din sai taga Ya Abdul Hakeem ya
Kama hannun Hameeda sun juya sun Fara tafiya tana share hawaye da dayan hannun
itama ta juyo hannu Zahra ta dago Mata alamar bye sannan ta Haye zuwa ciki.
Kusa da wata Mata ta zauna da alamar kamar zatayi sa'ar Ammah, ta gaisheta.
Saida jirgin ze tashi ne taji na gefenta Yana fadin "duk tunanin gidan ne ya hanaki
jin sanarwar a daura belt da ake ne?" Ya fada in a soft voice. Dago Kai tayi ta
dubi Mai maganar dake gefenta, wannan Wanda ya dameta da kallo ne kafin su shigo,
ita Sam batama San sanda ya zauna kusa da ita ba.
"Nagode" ta fadawa tana saka belt din lokacin da jirgin yayi balance a sama ne ta
cire belt din ta bude computer dake jikin kujerar dake gabanta tana kallon location
din da Suke bi tun tana Gane garuruwan data sani ko take jin sunansu har aka shigo
Wanda sai dai ta karanta kawai. Jefi jefi suna Dan magana da matar dake kusa da
ita. Nan kusa da ita dai Bata Kara kallonsa ba tunda taga shi kallon mutane kamar
dabi'arsa ne.
Sanyi kamar tafiyar awa daya taji yana Mata magana da farko yi tayi kamar bataji
ba, Saida matar dake kusa da ita tace "bakyaji ba ana Miki magana, ko kina da
aurene?".
Kai ta girgaiza alamar A'a.
"To meyasa kina Jin Yana Miki magana Kika kyale shi? ba Dadi irin haka baka
wulakanta mutum ba kasan gaba abinda Allah zeyi ba kinji".
A hankali take Mata maganar yanda ita kadai zata iya ji.

"Tom nagode in Sha Allah zan kiyaye". ta fada mata.


Bai hakura ba har Saida ya Sami kan Zahra duk da ba wani sakewa tayi dashi ba Amma
dai hakan yayi masa.
Lokacin da suka sauka haka ya dunga bin Zahra kafa ya kafa har ta dauko kayan ta da
aka gana screening suka fito, a Nan ya fada Mata sunansa Mushahu shi Dan Kano ne
Yana aikin government Yana Kuma kasuwwnci yanzu ma harkar kasuwancin ta kawo shi
kasar. Zahra ma ta fada Masa sunanta da inda take karatu da Dan zaman da zatayi
anan kasar kafin ta wuce.
Bai bar airport din ba har Saida Mama Hanifa tazo daukar zahra, da yake Mushahun
wise ne sosai ya sake da Mama Hwnifar don Basu rabu ba har Saida ya karbi address
din gidanta, saida suka bacewa ganinsa sannan Shima ya nemi taxin cikin airport ya
nufi hotel din da yake sauka idan yazo kasar da buri kala kala a zuciyarsa kan
Zahra.
Satinta daya ata nufi syprus kafin lokacin Mushahu ya Kai Mata ziyara yafi sau hudu
ba karamin samun shiga yayi a gurin Mama Hanifa ba.
Zauwanta makaranta da kwana daya Sajida da Khadijah da Fatima suka dawo Anisa ce
Bata dawo ba suna Umara da Yayarta sai Kuma sukayi Dan Samu matsalar visa.
Karatu Suke ba Kama hannun yaro Koda yaushe suna busy da karatu, tunda Zahra ta
rabu da Musbahu a turkey Sam ta aje batunsa a gefe duk da kusan Kullum saiya kirata
sun gaisa Yana ta kafa gwamnatin sa a gurinta. Bazato ba tsammani ranar wata
Saturday taje weekend gidan Uncle Haisam ya kirata da number din kasar Yana fada ya
shigo kasar tayi jiransa Nan da awa daya ze shigo makarantar, ba karamin mamaki
tayi ba da jin hakan, dan harga Allah batayi zaton da gaske yake ba da yace Mata
Yana Nan zuwa syprus din.
Nan da Nan ta fadawa Aunty Jinan matar uncle zata koma school yau suna da wani
group Assignment data manta zasuyi ta taho, Bata Hana ta ba tunda Daman uncle din
baya kasar sunje wani aiki south Korea, snacks Aunty jinan ta hada Mata masu yawa
ta tafi dasu. Allah ya taimaketa ta fito da card dinta na shiga bus ko train,
mintina talatin masu kyau suka kawota kyrenia city.
Lokacin data shiga hostei dakinsu ta wuce ta Kara gyara jikinta.
Wani karamin basket da dauko ta zuba snacks da drinks masu sanyi, turare ta Kara
fesawa har Brandy wadda Suke daki daya take tambayar ta ko zataje wani park ne ta
huta yau weekend?
Eh kawai tace Mata tayi gaba ta fita daga dakin, gurin su Sajida ta nufa akayi
rashin sa'a duk basa Nan sai Anisa kawai ta Samu tana sallah.
Zama tayi tana tunanin yanda lamura Suke ta juya Mata kamar a almara ko wannan din
shi ya zata Kaya a kansa? Dan haka Nan taji bazata iya yi Masa rashin kirki ba Dan
duk Wanda ze Bata kudinsa da lokacin sa ya biyoka har wata kasar duk da baka bashi
fuska ba to kuwa Bai cancanci wulakantawa ba a gurinka.
Kafin Anisa ta idar da sallar wayar Zahrar tayi Kara alamun Kira ya shigo, number
dazu ce ta daga tayi sallama, daga can ya fada Mata ya shigo ciki da inda yake.
Bayan sun gama wayar ne Anisa ta idar da sallar ta kalli Zahrar tana fadin "yaushe
Kika dawo nayi zato sai Monday da safe Zaki dawo?".
"Ke dai Bari kawai wallahi guy din Nan Dana fada muku mun hadu a airport din Kano
Yana kallona har ya bini gidan Mama Hanifa?"
Kai Anisa ta gyada alamar ta gane.
"To shine fa dazu ya kirani Wai gashi a kasar ya cika Alkawari zuwa anjima ze shigo
Nan gurina, shine yasa na dawo yanzuma kiransa ne ya shigo Yana gurin garden din
can na gurin second gate".
A gurin suka same shi Yana tsaye kusa da wani kangaroo na siminti Yana kallonsa
har da kanana a kusa dashi yayi kyau sosai kamar na gaske, ya shagala da kollon har
baisan sunzo gurinsa ba Saida Anisa tayi Masa sallama sannan hankalinsa ya kawo
kansu. Wani irin mahaukacin kyau yaga Zahrar ta karayi a idonsa, kasa dauke
idanunsa yayi daga kanta. "Masha Allah!"
Ya furta a hankali Yana fadada fara'a akan fuskarsa tare da amsa sallamarsu.
Karkashin wata bishiya Anisa ta nuna masa inda akayi kujerun sumunti masu kyau
sosai, bayan sun zauna ne Anisa ta gaishe shi tana Masa ya hanya, sannan Zahra ta
gaishe shi itama, duk sai taji duk wani iri saboda Sam lamarin maza gaba daya ya
Gama fuce Mata daga Rai duk da bazata ce sun yaucareta ba Amman lamarin su a
gurinta Mai girma ne Dan duk yanda taso ta manta abunda ya faru a baya Bata iyawa,
Samun kanta tayi da wani irin Jin bazata iya watsa masa kasa a ido ba.
Sun jima suna tattaunawa da Anisa a fakaice Yana yiwa kansa campaign a gurinta,
Anisar ta gabatar Masa da abubuwan da suka kawo masa, ita dai Zahra tana jinsu suna
ta Hira kanta na kasa tana Dan Wasa da wani zoben white gold da Aunty Nawwara ta
saya Mata lokacin da sukaje Umara.
Anisa ta jima sosai kafin tace zataje ta duba idansu Sajida sun dawo.
Bayan tafiyarta Musbahu ya yayi duk yanda zeyi ya janyo hankalin Zahrar ta sake
dashi Kuma Alhamdulillahi kafin wani lokacin ta Dan sake ba kamar lokacin da suka
zoba, a nan yake fada Mata shifa da gaske yakeyi yafi son kafin ta Gama makaranta a
Gama komai tana gamawa kawai ayi bikin tayi service a gidansa. Saida aka dauki
lokaci sosai sannan su Sajida suka karaso gurin bisa jagorancin Anisa, sun jima
suna Hira sosai anan yake fada Mata Shima Dan kano ne sokoto road, ita Kuma ta fada
Masa tana Jambulu Amma da suna zaune a Gwammaja ne.
Ya jima sosai kafin ya tafi,washe gari Sunday yaso su fita Amma Zahra ta nuna ba
wannan maganar duk yanda yakai da naci ta Kiya har su Sajida suka saka Baki Amma ta
qiya. Satinta daya ya koma inda ya sauke Mata kudaden masu yawa ya Kuma yi
Alkawarin gabatar da kansa gurin iyayenta tunda bada Wasa yazo ba, itama Kuma Bata
Hana ba tunda da gaske taji yes zata iya rayuwa dashi idan Allah ya amince.
Bayan barowarsa kasar da sati daya ya gabatar da kansa ga Alhaji Jafar a matsayin
Mai son auren Zahra, Bai rufe Masa komai ba har zuwan da yayi syprus din,sai dai ya
bashi hakuri akan zuwan daya Farayi kafin yazo gare shi, ba komai Alhajin ya nuna
masa sai dai yace irin hakan bashi da kyau kodon gaba mutum yabi 'ya mace wata uwa
duniyar batar da sanin magabatanta ba akwai hadarin lalacewar tarbiyya ga Wanda
Allah yasa shaidan yafi karfin zuciyar su.
Alhajin yayi Masa tambayoyi sosai akan Sana'a da Kuma asalinsa, sannan ya fada Masa
shima mahaifinsa ya rasu tun Yana level one hundred a jami'a, a labarinsa daya fada
masa nan ya gano kanin mahaifansa sunyi makaranta tare dashi a Bauchi.
Bayan tafiyar Musbahun da Alhaji Jafar ya tada mutum takanas yaje har Kano da
taimakon abokinsa Alhaji Muttaqa akayi Masa bincike kan Mushahu Kuma Alhamdulillahi
ba'a Sami wani abun ashsha ba a tare dashi Dan mahaifiyar ma ta fito ne daga cikin
manyan gidajen sarautar Kano.

Bangaren Zahrar kuwa kusan Kullum suna tare da Musbahun a waya Dan har ya haddace
lokacin agogon kasar, tun tana daridari har ta sallama tare da karfafawar su Sajida
kafin su gama semester din sun shaku dashi sosai Bata rufe Masa matsalar data
fuskanta a baya ba, nuna Mata ma yayi rabonsa ne ya kawo aka ringa samun akasin na
bayan ya Kuma yi Mata Alkawarin ruwa da iska ba abunda ze girgaiza tarensu bare har
akai ga rabuwa Koda kuwa Aljani ne ya aurata in sha Allah sai yaga bayansa, yayi
Mata alkawura da dama ya nuna Mata Babu wani abu da ze girgaiza shi koya bashi
tsoro akan lamarin aurenta.

Magana tayi nisa Dan har iyaye sun shiga abinda yayiwa Ammah Dadi kenan Dan wannan
karon Kam Zahra tayi Dace da Dan manyan mutane sosai, dan basu bar garin ba Saida
suka shaida lokacin aure idan ta gama service da wata daya duk da sunso ayi bikin
kafin tayi service din sai Alhajin ya nuna musu suyi hakuri tayi idan ta gama saita
zauna guri daya ba daga kaita ba ba dadewa ta Fara fita kullum, Kuma ya Hana kayan
lefe Dan Alkawari yayi ankawo biyu an karbe to kuwa ko waye zata aura sai dai ya
aje Mata kayan idan taje gidan ya Bata.

Lokacin dasu Zahra suka Gama karatunsu har da Ammah da Hameeda akaje bikin
graduation dinsu mutanen Jordan ma sunje har Mama Hanifa.
Bayan kammala taron sun Kara kwanaki a kasar, Zahra ta raka Hameeda kuraren
shakatawa da yawa tayi kallo tayi santin inama Abba ya dawo dasu Nan Suma gashi ita
har ta Gama Amma su Kullum karatunsu ba cigaba ana faman strike tunda a yanzu ma
shine ya dawo dasu gida har ta samu damar zuwa itama.
Ranar da zasu taho sun Sha kukan rabuwa dasu Sajida tunda su saura shekara daya su
gama.
Murna gurin Zahra ba magana ji take kamar ta sauke wani abu Mai nauyi daga kanta.
Musbahu yaso zuwa graduation dinsu Zahrar Amma lokacin Yana busy yaje wani special
assignment a Kenya dole sai hakuri yayi, Amma Yana dawowa ya yiwa Azare dirar
mikiya a ranar Zahra taga zallar so a gurinsa Dan ji yake kamar ya dauke ta yayi
gaba da ita, itama ta bashi kulawa kamar me,Hameeda tazo sun gaisa sun Dade suna
Hira dashi tambakar sun shekara da sanin juna, sunan mujiba ma ta shigo suka gaisa
ba shi yabar Azare ba sai kusan magariba Dan ma Zahrar nata Masa magiyar ya tafi
saboda rashin tsaro irin na kasar.
Tun daga lokacin hanya ta aure shi tsakanin kano da Azare. Mushahu na mutane ne
kusan duk Wanda ya kwana ya tashi a Nan kukkuken unguwarsu Zahra yasa shi Koda kuwa
ba gaisawa suke ba, wata kila ya taba yiwa wani alheri a cikin yaran gidanku Dan da
gaske hannunsa a sake yake gurin Alkhairi.
Sunyi sabo sosai da jama'a a Nan har gurin malam Bukar Yana zuwa sauda dama idan ya
shigo garin, wasu ma daga cikin samarin gidan malam din sunyi sabo sosai.
Lokacin da results dinsu Zahra ya fita Sam bataje ba Auncle Haisam ne yayi Mata
komai Allah ya taimakeka ta fito da first class degree a akan anatomy.
Allah ya taikata da taimakon Ya Hassan aka kawota bauchi service, bayan zaman camp
sukayi posting dinta Dr Sulaiman Adamu memorial college of Hygiene and
Environmental health science Azare.
Ammah taji dadin hakan sosai haka shima Mushahun yaso hakan kwarai da gaske.
Zahrar najin dadin aikin sosai da sosai domin teaching Yana cikin hobbies dinta.
Bayan sun Gama ne da wata daya kamar yanda akayi Alkawari aka Fara kokarin Fara
shidimar bikin ta dai dai lokacin Kuma akayiwa su Ummee rasuwa a saudiyya abinda ya
Hana su zuwa kenan da har Ammah tace a daga bikin tunda rasuwar ta jikinsu ce kanin
Baban Ummeen ne ya rasu,Amman sai sukace Dan me ayi idan komai ya lafa zasuzo suga
daki kawaii.
A satin da za'a Fara bikin kusan Kullum Mushahu da Abokansa shakikai su Deeni da
Aliyu Wanda Suke cussings suke ta zirga-zirgar ganin abubuwa sunyi yanda ake so duk
wasu programs a nan za'ayi dinner ce kawai zasuyi a Kano, sun Kama dakuna uku a
hotel idan zasu zauna har zuwa Daurin aure.
Saura kwana biyar Daurin auren ne wani abun al'ajabi ya faru da Hajiya Nafisa Maman
Mushahu wadda suke Kira da Ammi.
Cikin dare tana barci ta farka a matukar razane saboda wani mugun mafarkin da tayi
da Musbahun akan auren, addu'a tayi ta koma ta kwanta ai kamar jira ake barcin ya
dauketa sai abunda ta gani a wannan mafarkin yafi wancen muni, wasa-wasa barci ya
gagareta a wannan Daren kafin safe duk ta wani hargize ga wasu irin tunane tunane
sun cika Mata zuciya na rashin kwanciyar hankali kafin yamma gaba daya ta Zama wata
marar nutsuwa ba shiri ta Nemo kanwarta Aunty Jamila a waya Nan da Nan tazo tunda
ba aure gareta ba, duk ta kwashe komai ta fada Mata akan Bata son auren Musbahun
kwata kwata ita fa ko a cikin ranta ta tuna da zeyi aure ji take kamar zata zauce,
da farko Aunty Jamilar ta dauki abun Wasa Amma ganin da gaske abin yake yasa ta
Kira Babban yayansu Alhaji sulaiman da kanin Baban su Musbahun Alhaji isma'il, Suma
da farko sunyi zaton na Wasa ne Amma da suka matsa akan ta Fadi dalilinta na Hana
yuwuwar auren sai abun ya ta'azzara ya Zama kamar Mai tabin hankali, ganin abun
Yana neman ya Zama wani iri ne yasa Alhaji sulaiman ya kirawo Aliyu tare da
tambayar suna ina?.
Aliyun yace gasu Nan a hanya sunje Azare ne Amma har sun wuce wudil sun kusa kano
ya fada Masa lallai direct su nufo sokoto road su duka.
Haka suka shigo suka tarar da wannan dambarwar ana ta fama da Ammi.
Ai tana arba da Mushahu ta Kara tuburewa tana fama fadar wallahi matukar ya kafe
sai auri Zahra Bata yafe Masa nononta da yasha.
Su dai Basu ankara ba sai ganin Mushahu sukayi ya sulale ya zube a sume, da sauri
Aliyu ya kawo ruwa aka zuba Masa Amma a banza ganin haka yasa suka nufi Asibitin
Nasarawa dashi. Haka aka dunga juyawa da Ammi Amma ta kafe kamar kafiran farko duk
Wanda ake tunanin ze kawo gyara a lamarin an fada Masa Kuma yayi bakin iyawarsa
Amma ba wani ci gaba da aka nemi a Zafafa sai lamarin yaso ya koma Mata tabin
hankali abinda daya tada hankalin Babarsu kenan Hajiya Yaya tace dole a hakura da
auren tunda abin yazo da irin wannan lamarin marar Dadi daman tun farko ita bataso
lamarin ba sai dai yaran yanzu ne baka hanasu abinda suke so, tunda Daman fa ance
shine na uku a Wanda zasu auri yarinyar ana fasawa to shima gashi tun ba'aje ko Ina
ba lamarin ya Zama haka.
Tashin hankali iya tashin hankali Musbahu ya shiga Dan dakyar aka Sami nutsuwarsa
dan kwata kwata ya daina magana da kowa ya rufe duka wayoyinsa shima Deeni ganin
kiran Zahra yasa ya rufe layin da suke wayar da ita, Aliyu ne kawai Bai rufe wayar
ba Amma baya picking idan ta Kira a halin hake ne su Alhaji sulaiman sukaje Azaren
da labari marar Dadi Wanda ya kawo karshen 'yar Wala walar da akeyi da Zahra akan
aure ta kawo karshen duk wani makirci da bita da kulli da ake Mata na rushe aurenta
idan ya taso abinda ya girgaiza duniyar Wanda suke fake suna tsula ta'addanci ta
karkashin kasa.


AUREN HUCE HAUSHI



MAMAN FATIMAH

Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu. Dan Allah ayi hakuri da


matsalar da aka samu gurin turo page fourteen sau biyu hakan ya faru ne saboda wasu
dalilai Amma na karshen Wanda na turo shine cikakken fourteen din yanzu kuma na
hade fifteen & sixteen guri daya na gode.

Page
Fifteen
&
Sixteen

BACK TO STORY.

________ Gurin Zahra su Sajida suka shiga tana kwance a gado idanunta a rufe
tayi zurfi cikin tunanin, Sam bataji shigowar su Sajida ba Saida mujiba ta Dan
zungure ta bude ido ta yunkura ta tashi zaune tana dafe kanta dake Sara Mata.
Sajida ce ta zauna kusa da ita ta Kama hannun Zahrar tana fadin "bestie Dan
Allah ki rage tunani kada wani ciwon ya kamaki, ki yawaita addu'a komai yayi zafi
maganinsa Allah. Kuma wani hanin ga Allah baiwa ne, ke kanki Baki taba tunanin abun
ze Zama haka ba, Kuma Allah ya juya lamarin yanda yaso, to saiki gode Masa bisa
ni'imar da yayi miki, Kuma nifa mujiba Ina doubting akan wannan da aka daura musu
aure, Kuma ki rubuta ki aje zakice na fada Miki kije kiga gidan da za'a Kai bestie,
Kuma ki duba kiga irin kayan da aka kawo yanzu kinsan duk Wanda ya hadasu first
class ne a gurin gayu wallahi komai bana banza Amma Kuma Wai almajiran malam ne
gaskiya I doubt much".
Ta fada tana kallon mujibar.
Ita dai Zahra ta rasa inda zata Kama komai ya kwance Mata, su damuwarsu kaya da
gida, ita Kuma tata damuwar ta yanda za'ayi zaman ne, har yanzu gani take kamar a
mafarki Wai wannan karon ma Saida aka samu akasi,ta rasa daga Ina matsalar take,
shi kuma auren da aka daura meye ze biyo baya tasan idan ba wani nufi ba na Allah
shima sai an Sami wani kalubalen a cikinsa.
A hankali ta furta "Ya Salam! Allah ka shiga cikin lamarina, wallahi bestie
komai ya kwance min bani da sauran dabara,kwakwalwata ta daina aiki yanda ya kamata
kinsan Allah nifa kamar ma tsoronsa nakiyi Dan tunda na Fara ganinsa naji wani irin
Abu a jikina wanda ban tabaji ba a kan ko wane namiji sai shi, Kuma yayi min abinda
ya kamata na dauki mataki Mai karfi amman wallahi ko magana kasayi Masa nayi,
yanzu kuma a haka zan rayu dashi? Ni wallahi bana sonsa Sam Kuma fa Shima yace baya
son abin yake ba kawai dai baze iya watsawa su Abba kasa a ido bane". Ta karasa
fada hawaye na zubo Mata a fauska.
Lallashinta sukayi da kyar tayi shiru kafin mujiba tace "haba Zahrar ki daina
kuka idan kina daga hankalin ki na Ammah ma baze kwanta ba, Kinga irin haka ba Dadi
duk da an aura miki Wanda babu soyayya da shakuwa a tsaninku, ita a hakan ma yayi
Mata da ace wannan karon ma an fasa aure gara hakan tunda naga alama da ita ake
fadan ke kin ratso ne kawai ake fakewa da lamarin ki Dan a Hana duniyar ta zaman
lafiya da kwanciyar hànkali, Kuma Baki san dalilin da yasa Abba yayi hakan ba,
kinsan dai Abba baze taba aura Miki baragurbi ba kedai kiyi ta addu'a muma muna
tayaki, Bari na tambaye ki Mana idan kina addu'a bakya cewa Allah ya Baki miji na
gari?"
Hannu tasa tana share guntun hayenta kafin ta harari mujibar tana fadin "Ina
yi Mana kuma kawai saina yi sallah na kasa wannan addu'ar dan na Zama abinda na
zama ko?"
"A'a ba haka nake nufi ba bayani zan miki shi yasa nayi Miki tambayar dai,
Allah ya huci zuciyar Amarya".
"Kina jina mu 'yan adam muna rokon Allah ya zaba mana abinda yafi Mana Alkhairi
Amma wani lokacin inda kake zaton alherin ne to sai kaga ba'a Nan yake ba, idan
yazo ta inda baka zata ba tunda bakasan gaibu ba, sai kayi watsi dashi idan bakayi
sa'a ba haka abun ze kwaranye baka mori komai ba, alhalin Kai ka roka aka baka sai
kuma ka Raina abinda aka baka ba tare da kasan shine alherin ba. To Dan haka nake
so ki yiwa Allah da manzonsa ki rike abinda Allah ya Baki tunda shi Kika roka Kuma
ga abinda ya Baki sai kiyi ta Tahamidi ga Allah kawai, ki nemi Allah ya saka muku
kaunar junanku da soyayya da jinkai. Dan kinsan dai idan ba wata kaddarar Ubangiji
ba Babu abinda zesa ya rabu dake tunda ya karbi auren Nan wallahi ko rantsuwa
nayi bazanyi kaffara ba yana so, dan haka ki daure kiyi Masa biyayya shi arziki
nufin Allah ne, naji ana ta 'yan kananun magamganu ki toshe kunnenki kada ki bada
barakar da wani ze kushe Miki miji dan bashi da kudi, Allah ne Mai azurtawa lokacin
daya so sai kiga wata Rana sai dai a tada labarin abun".
Sun Dade suna kawo Mata misalai da yawa na irin wannan auren nata daga baya Kuma
ya Zama Alkhairi.

********** A matukar gajiye Mahmud ya shigo cikin gidan misalin karfe biyar na
yamma tun safe ya kebe kansa a dakin daya Kama na hotel yake ta faman aiki yaso
kwarai ya Gama da wuri kafin yamma amma abun ya gagara Dan da gaske aikin ya dauki
hankalinsa sosai ga tafiyar dake gabansa Banda Allah yasa wasu abubuwan sun
daidaita a jiya da dole tsakanin gobe da jibi dole yabar garin ko baya so. Amma
cikin taimakon Ubangiji sai komai ya Fara daidaita, shi kanshi Yana Jin idan ya
tsallake ya tafi daidaita wanna gabar Bai kyauta ba Sam, dan jama'a zasuga kamar ya
gujewa auren gatan da akayi Masa ne ya watsa musu kasa a idon an Masa gata irin
wannan sun dauki yarinyar su Mai tsada sun bashi ba tare da sun San ko waye shi
ba, ko la'akari da karancin samunsa suka aura Masa.

Su Habib ya tarar a falon Yana karatun Alqur'ani, Abubakar Kuma Yana ta faman hada
Nile sat.
Su duka suka amsa Masa sallamar Nan falon ya aje jakar laptop dinsa abinda bai taba
kwatanta zuwa da ita ba kenan Dan duk aikin da zeyi sai dai yayi acan hotel din ya
barota, amma yau dole tasa ya taho da ita nan saboda so yake ya raba dare Yana aiki
shi yasa ma Kai tsaye ya nufo gidan da ita yasan bashi da matsala dasu duka biyun.
Abubakar ne ya tsaya da aikin Yana kallon Mahmud Yana fadin "Dan Allah Ina ka
shiga Wai bakasan kana dagawa Baba malam hankali ba? shifa yafi son daya juya ya
ganka, gashi ka Kama ka rufe wayar ana ta Kira a rufe".
Girarsa ta daman ya dan shafa kadan kafin ya zauna Yana fadin "cool down Mana my
man Ina kake tunanin zan tafi? Wallahi aikine yayi yawa na wannan NGOs din bakaga
har kayan aiki suka bani ba tun zuwan da sukayi wancan karon, yanzu haka ana koya
min yanda zanyi amfani da ita laptop din ne yanda zanji dadin aikin, Bari nayi
wanka sai muje gurin Baba malam din nayi Masa bayani yanda ze fashimta, sunce ma
nan da sati daya ko biyu zasu kiramu zuwa babban taro da za'ayi".
Tunda ya Fara magana Habib ya dakata da karatun da yakeyi yana bin Mahmud da kallo
haka nan kawai yaji Kamar ba gaskiya Mahmud din ya fada musu ba, Kamar yana boye
wani Abu, shifa tun lokacin daurin aurensa ya lura da yanda Kamar yake baiwa Sameer
umarni a wasu lokutan sai idan ya farga ne yakan yi maza ya canza taku, sannan a
watannin baya ya taba jin yana waya a kusa da dakin da suke taron abinda ya shafi
makaranta lokacin yana duba wasu sabbin forms da aka kawo na Enterprinuership da
za'ay a gurin Sam baisan Yana ciki ba tunda kofar a rufe take ji yayi sosai Yana
bada umarnin yanda abin ze kasance harda makudan kudin da za'a kashe gurin sawo
kayan sana'ar da za'a koyar harda kudin da za'a participants din tunda program din
harda matasan unguwa a cikinsa duk za'a Kuma bada kayan sana'ar da mutum ya koya
kyauta, tun lokaci yayi masa alamar tambaya sai dai ba wata kafa daya Bari wadda
za'a fashimci komai. Bai tabbatar da abinda yaji ba Saida akayi komai Kamar yanda
ya bada umarnin, ga Kuma lokuta yawa sai yayi batan dabo ka nemeshi ka rasa Kuma
har yanzu baisan takamaiamai Ina yake zuwa ba duk kuwa iya kwakwarsa.
Jakar ya dauka yayi gaba Yana fadin Bari na Dan watsa ruwa na fito. Da ido suka
bishi har ya shige corridor din daze kaishi bedroom dinsu,kowa Yana ayyana wani Abu
a zuciyarsa.
Ya dauki Kamar minti hamsin kafin ya fito cikin Riga da wando na shadda Fara tas, a
gaggauce ya fito ganin lokacin sallar magriba ya kawo jiki.

***
Da dare Zahra tana dakin Ammah suna Hira da Inna maimuna tana Kara nusar da ita
yanayin rayuwa Sajida ta shigo da waya a kunnenta ta gaishe da innar ta Mikawa
Zahra wayar tana fadin "Baffan Rimi ne yake son magana dake"
Amsa tayi tare da sallama, cikin daki Inna ta nuna Mata da hannu ma'ana ta shiga
ciki tayi wayar, Dan sajidar tana Mika Mata ta juya ta koma, haka Nan ta tashi duk
da Bata San nufin innar na hanata waya a falon ba.
Gaishe da Baffan tayi tunda Daman ya Santa tun suna makarantar kazaure sunje masa
ita da Sajida lokacin da Zahrar ta zauna a kano gidansu sajidar sanda akayi musu
hutun midtrem break maimakon taje Azare sai umman sajidar ta nemi Alfarmar Ammah ta
barta tayi hutun a gurinta,to kafin su koma ne sukaje Rimin sumailar gurin kakan
sajidar, tun lokacin ya baiwa Zahra magunguna sosai yace tayi amfani dasu har
Sajida na mita ita Bai Bata irin na Zahra ba, a lokacin murmushinsu manya yayi Yana
fadin "yanda aka saka rayuwarta a gaba ke ba Wanda ya damu da taki rayuwar ita
akwai tarnaki Mai yawa a kanta Kuma Naga jikin nata ba wani abun azo a gani na
tsarin jiki.
Gaisuwar Baffa ya amsa Yana fadin "Ashe haka lamura sukayita faruwa ko Fadima? Dazu
Babar taku tazo min da bayanin abinda ya ringa faruwa dake akan aurenki, yanzu haka
tana Nan zata kwana saboda akwai abinda nasa ayi Miki gobe in sha Allah zatazo Miki
dasu da yanda zakiyi amfani dasu in sha Allah ba abinda ze Kara faruwa dake, lallai
akwai shedancin mutane akan lamarin Amma mu dauka Daman haka Allah yayi nufi, wanin
Allah Bai Isa yayi maka komai ba face da izinin Ubangiji, ga Uwar taki ku gaisa".
Ya mikawa Maman Sajida wayar.
Bayan ta gaisheta ta Kara da yi Mata nasiha sosai itama, sannan ta fada mata gobe
in Sha Allah daga Rimin Nan zasuyo ita da Babban danta Wanda some times shine
direban ta idan zatayi doguwar tafiya, kafin sukayi sallama.
Dakin Ammah Zahra ta shiga ta fada Mata yanda sukayi da kakan Sajida, godiya sosai
Ammah ta ringa yi tana Kara jinjina kaunar da bayin Allah nan.suke yiwa Zahra
dalilin 'yarsu gashi saboda matsalar Zahrar zata taso tazo har Azare.
Washe gari tunda wuri Zahra da Sajida suka Gama gyaran dakin Ammah sukayi wanka
sannan sukayi breakfast gurin karfe Sha daya Maman su Sajida da yayanta Ya Abba
suka karaso murna gurin Sajida ba magana, dakin Ammah suka nufa da Maman Zahra
tasonsu Fara shiga gurin Mama su gaisa Amma Sajida ta Hana tana fadin "A'a ki Bari
mu shiga inda ya kamata idan min Gama abinda ya kawo ta sun gaisa da kowa so kike
azo a zaune Mana a hana ruwa gudu".
Tarba ta girma Ammah tayiwa Maman Sajida itama ba wata babba bace Dan Bata Kai
sa'ar Ammah ba, an sauki Ya Abba a dakin da suke sauke bakinsu yayin da magaji ya
shiga shidima dashi.
Bayan Maman su sajidar ta Gama cin abubuwan da aka kawo Mata suka sake gaisawa dasu
Ammah da Inna maimuna ta jajantawa Ammar abubuwan da suka ringa faruwa, ta Kuma
Dora musu da bayanin da mahaifinta yayi Mata akan matsalar Zahrar inda ya bada
tabbacin ko waye yake wannan shegantakar a kusa dasu yake sosai, Kuma dashi ake
faduwa da tashi, kuma yace kada Wanda ya kawo wani Abu da sunan naci kona Sha yace
a baiwa Zahra da sunan tsarin jiki ko na gyaran aure a barta taci sannan a kula da
Koda abincin cikin gidan ne in dai ba ita Ammar ta dafa da hannunta ta Bata ba daga
Nan har tabar gidan.
Wata babbar leda ta dauko wadda sukazo da ita ta bude ta Ciro jarka da ruwa a cikin
Mai kalar yellow na za'afaran ta dauko wani garin magani Mai laushi ta hadasu da
jarkar ta mikawa Inna maimuna tana fadar.
"Ga wanna ruwan addu'a ne da garin magarya zata dibi ruwan addu'ar ta zuba garin
magaryar ta Sha ta shafe jikinta safe da yamma,wannan Kuma kafa da hannu kawai zata
Riga turarawa sai Addu'oi da ya bada a Bata zata ringa karantawa safe da yamma".
Godiya sosai su Ammah suka shiga jerawa Maman Sajida Kamar ba gobe har sai da ta
ringa fadin "Haba Hajiya meye amfanin taren abinda ya shafi Zahra ai ya shafi
sajida wallahi shekaranjiya data Kira ta fada min hankalina ba karamin tashi yayi
ba wallahi na dauka abin ya kwaranye tunda an dauki dogon lokaci kafin a Kara
maganar Auren".
"Wallahi kuwa muma mun dauka na bayan da aka fasa ko matsalar namijin Aljani ne ya
aureta Amma duk inda akaje da ita sai a ce ba wani iska a jikinta".
Inna maimuna ta fada.
Sun tattauna sosai da Maman Sajida Saida akayi sallar Azahar Sajida ta raka mamanta
dakin Mama su gaisa, sun Sami kawar Mama Asabe sun hada Kai suna kus-kus bazaka
taba cewa da mutane ba.
Sun gaisa sajida ta fadawa Mama mamanta ce, Basu jima ba suka fito Mama ta biyosu
har kofar part dinta Nan godiyar ziyarar.
Sai kusan karfe uku su Maman Sajida suka juya Kano Sajida tace ita saita raka Zahra
gidanta zata dawo.
Tun da Mahmud ya Kira Zahra sau daya Bai sake kiranta ba, yau yaji ya kamata ya
Kira yaji lafiyar ta ko banza fa yanzu tana karkashin ikonsa ne cinta da Shanta da
duk lamuranta suna wuyans Kuma ai Bai kyauta ba gaskiya ace yayi burus da lamarin
ta abun sai yayi Mata yawa.
Sai gurin Tara na dare ya lalubo numbarta ya Kira, harta gama ringing ba'a dauka
ba sai kawai ya share ya tura Mata text massage ya fada Mata Daman ya kirane yaji
lafiyar ta.
Tun bayan tafiyar Maman Sajida Ammah da Inna maimuna suka shiga hasashen abinda
kakan Sajida ya fada na hasashen Mai yiwa Zahra bita da Killin nan duk iya nazarain
su Basu gano ba sai suka.barwa Allah amma dai innar ta soke kwanan Zahra a can
gurinsu tace su dawo dayan bedroom din Ammah suna wanna ita da Sajida da ita innar
ya ishesu ita ko katifa sai a saka Mata a kasa ta kwanta.
Hakan akayi su Zahrar suka tattaro suka duk wani Abu na amfaninsu suka dawo dakin.
Kafin su kwanta Saida Inna maimuna ta saka Zahra tayi amfani da duk magungunan da
Maman Sajida ta kawo Mata, wanna ne dalilin dayasa innar tace su dawo nan tunda
komai na duniya Yana son sirri, duk da Hameeda ce kawai ke kwana a tare dasu Zahra
Dan Salma tunda suka dawo ma Bata taba kwana a part din nasu ba.
Tun Hameeda na jiransu Zahra su shigo har tayi barci.
Saida Zahra ta Gama amfani da duk abubuwan da aka kawo Mata sannan ta dauko wayarta
rabon data dauko ta tun bayan sallar Azahar data hau online ta duba sakonnin
whatapps.
Sajida da Inna maimuna Kuma sunta hirar duniya abunsu.
Missed calls ta gani har hudu uku na mujiba ne sai Kuma wani daya number ce amma
kallo daya tayi Mata ta gane ta waye, ji tayi gabanta ya fadi to neman me yake Mata
da wanna tsohon Daren haka kawai ya dagula Mata sauran lissafinta. Fita tayi daga
call history din sai Kuma taga envelope alama massage ya shigo budewa tayi sakonsa
ta gani a hankali ta furta ta "Ya salam".
Allah da gaske fa take jin wani irin lamari a tare da shi.
Da safe ma innar ta saka Zahrar gaba Saida tayi duk abinda ya kamata kafin ta fice
tabar dakin dan tun kafin ta Fara Sajida tayi waje ta Basu guri. Saida tayi wanka
kafin ta fito yin break bayan sun gama ne Ammah tace Zahra taje Abbansu na kira,
gyalen rigar ta yafa a kanta ta nufi gurin Abban, lokacin data shiga ya Gama break
Shima, guri ta Sami ta zauna kusa da kujerar da yake Kai tana fadin "Abbana Ina
kwana?"
Jaridar dake hannunsa ya aje Yana fadin "lafiya kalau uwata, Ina fatan ba wata
damuwa ko?"
Kai ta gyada kafin tace "ba komai"
"Masha Allah ya fada.
Kafin yayi gyaran murya ya Fara fadin "Uwa inaga in sha Allahu jibi da yamma Zaki
tafi gidanki Dan dazu ne malam Bukar ya roki wannan alfarmar saboda shi Mahmud din
ne zeje wani taron da kunyar da suke aiki dashi suka shirya to Kuma yace baya son
ya tafi Baki tare acan gidan ba kada abin ya Zama na magana ace ko ya gudu ne ya
barki a nan, to Nima din na karbi nasa hanzarin tunda Masha Allah jikin naki yayi
sauki sosai Kuma Baki bani kunya ba kin kwantar da hankalinki".
"To Abba"abinda ta fada kenan tayi shiru, Mamace ta shigo dakin itama Tasha wanka
sai baza kanshi take Kamar Kullum. Da barkwwnci ta shigo tana fadin "A'a bamu Gane
ba, irin wannan kebewa tsakanin 'ya da uba mu ba'a neman ayi shawara damu".
Ta fada tana fadada murmushinta.
Gaisheta Zahra tayi kafin mamar ta gaisheta da Abban tunda ba itace da girki ba.
Bayan sun gaisa ne yake fadawa mamar "Ba wani shawara muke ba wadda Bata shafeku ba
Ina fada Mata ne jibi in Sha Allah zata tafi dakinta tinda Allah yasa ta warrare
Kuma shi mijin nata ne zeyi tafiya shi yasa nake son ta tafi dakinta".
Nisawa Mama tayi kafin tayi magana.
"Kamar Yaya zeyi tafiya daga Kai masa yarinya basai ya tafi da ita ba salon ya cuci
yar mutane ya lallaba ya budu ya barta tunda tsintacciyar mage ai Bata mage,
gaskiya Abban Yara ka tsaya ka duba lamarin nan Mana kada fa azo ana Dana sani kaga
masu iya magana na cewa keyace".
Abban ne yace "ba abinda ze faru sai Alkhairi Amma Jibi da izinin Allah uwata zata
tafi dakinta, tashi kije Uwata Allah yayi Miki Albarka yanda Kika yi min biyayya
Ubangiji ya Baki 'ya 'yan da zasu yi Miki biyayya kema".
A zuciyarta ta amsa da "Amin"
Saida Abbai yaga ta fice gaba daya sannan ya dawo da dubansa gurin Mama yace "haba
Rabi'a har yaushe Zaki dinga magama irin wannan a gaban kankanuwar yarinya Kamar
Zahra ai Bai kamata ba ki duba kiga yanda aka dunga walagigi akan auren yarinyar
nan a baya yanzu Kuma anyi aure Zaki ringa fito da maganganun da zasu iya sakata a
wani Hali ai kwantar da hankali uwata take bukata ba irin haka ba, mu bita da
addu'a in sha Allahu Alkhairi na hada Wanda a gaba duka sai sun gode min koda kuwa
bana duniyar ne".
Tunda Zahra ta shigo ta kwanta a kan sofa a nan falon Ammah na kallonta tasan kan
zance dan tunda Abba ya dawo daga masallaci ya fada Mata, zancen da suke da Inna ma
kenan ta shigo suka bar zancen.
Da hantsin Ammah ta Kira Aunty Hasana ta fada mata.
Zuwa Sha biyu tana gidan suna zaune a falon Ammah Mama ta shigo ita da kawarta ta
amana Asabe wadda kwanan Nan ta mayar da gidan gurin zuwanta sabanin baya da sai a
share watanni Bata zoba, Nan suka zauna akaci gaba da tattaunawa akan tarewar Zahra
har Asabe ke fadin zata saka wata 'yar gusau da suke makwaftaka ta yiwa Zahra hadin
kazar amare da daka shine nata Gudunmawar.
Da yamma Aunty Hasana ta umarci Sajida da Hameeda da zilai Mai aiki suzo suje gidan
Zahrar a gyara abinda ya kamata tunda jeren ya dan jima da yi.
Sun fito zasu tafi ne Abdul Hakeem ya tsayar da Auntyn Yana fadin "sai Ina Kuma
Aunty mu?"
"Gidan Zahra zamuje a Dan Kara gyarawa jibi Abba yace za'a kaita kaga kuwa ai dole
a shiga a duba ayi abinda ya kamata".
Komai tsab suka sameshi da gani ana gyarawa Kullum dan har wani hadaddan kamshin
freshner ke tashi a falon haka bedroom din Shima komai neat yake a toilet ne abin
ya bawa Aunty Hasana mamaki an zuba kayan wanka masu azabar tsaba Bata Kara
tsinkewa da ta janyo locker ta jikin mirror taga wasu designers din turaruka na
Mata Kuma da yawa na kamfanin Al -haramain ne harda irin Wanda Zahra take amfani
dasu.
Ita dai Hameeda Yar kauye ta Zama a gidan Dan ko a mafarki Bata taba kawo Wanda aka
aurawa Zahra, ze Kama hayar gida irin wannan aljannar duniya haka ba.
A kitchen ma Nan Hameeda da zulai suka lalace komai na gurin saiya burge mutum, Nan
ma Saida Auntyn taga wani fregde ash colour a cikin Dan ack din jikin kitchen din
irin Mai kofa Kamar ta wadroof ko ba'a fada ba kasan kudi sunyi kuka a gurin.
Burner Auntyn tasa aka jona aka zuba turarikan wuta Wanda aka hadowa Zahra daga
Saudi Arabia tun wancen lokacin tunda basa komai saima Kara kamshi. Basu baro gidan
ba sai kusan magariba.
Aunty Hasana taso ta wuce da Zahra gidanta amman Ammah tace A'a ba inda zata so
suke ace Mata tsohuwar banza idan so suke su tafi to ita zahrar ta Kira ta fadawa
mijinta idan ya amince ita nata Mai sauki ne ita kuma Zahra tace lahlah a barshi
kawai.
Wajen goma saura aunty Hasana ta dauki yaranta suka wuce gida. Da safe Saiga Asabe
da dahuwar kazar amare da jarkar zumar Mata da ta tsimi tayiwa gidan tsinke, part
din Ammah ta shigo direct, bayan sun gaisa ne ta mikiwa Ammah babbar ledar data
zubo kayan tana fadin "Ina Amarya tazo gashi na cika Alkawari tazo ta cinye ta bani
kashin tace a koma Mata dashi zata hada Mata wani Abu dashi. Inna maimuna ce tace
"ai kuwa yanzu taci abinci ta shga daki saidai a aje zuwa anjima sai taci ko gida
ne sai a aika Miki da Qashin, mun gode kwarai madallah Allah yabar zaman tare".
Asaben ta amsa da "Amin ai bama sai an tashi mutum ya kaiba Nima saina jira taci
din ko Nan da yamma ne" ta fada tana mikewa tayi musu sallama ta nufi dakin Mama.
Bayan fitarta ne Ammah ta dubi Inna maimuna tana fadin "nifa jikina Bai bani ba
akan taci wanna abun Dan ni tunda ta fada jiya naji abin Bai kwanta min
ba,mutuniyar da gaisawa ma sai ta kure akeyi da ita Amma fa ki duba sai wani rawar
jiki take akan abinda Bai shafe ta ba ko alama, Kuma kar nice wani abun arziku
sukeyi da zahrar Dan ko gaisawa saita kure, Amman ki duba ki gani yanzu sai haba
haba take da Zahra.
Dakin Ammah aka shiga da kayan ammar tace zata cire tsokar tabar musu kashin, hakan
ne ya kasance tayi komai ta baiwa auta ya kaiwa Asaben dakin Mamar.
Saida Asaben ta tabbatar auta ya fito ta kwashe da dariya tana fadin "wallahi Maman
yara kinsan ta kan mugumta, yarinya har yarinya amma ta Kare a auren marar asali
Wanda ko danginsa ba'a sani ba"
Kwafa Maman tayi "barni kawai Asabe wallahi tun lokacin da aka dauko yarinyar nan
hankalina ya kasa kwanciya, saboda babu ta inda Allah ya rageta duk abinda ake so
jikin 'ya mace to Allah yayi Mata ga uwa uba yanda mazan zamanin nan suka jarabtu
da son Mata irinta nasan ba karamin mutum ne ze dauke taba Ina zaune sai dai na
Zama 'yar kallo ga nawa 'ya'yan a gabana, wallahi baze yuwu ba ai hankalina Bai
Kara tashi ba Saida na raka Aunty Ladi gurin wani Mutum a can jos nayi Masa maganar
Asma'u to cikin binciken ne maganar yarinyar ya Fado yake fada min na kyale maganar
Asma'u don ba yanda zanyi da ita jikinta a shirye yake haka Shima Alhajin ba abinda
zeyi tasirin da ze rabashi da ita, Amma ga wata yarinya Nan duk gidan ba 'yar da
zata wuceta a sa'ar rayuwa a gurin aure Dan mijin da zata aura ba karamin mutum
bane Kuma dai..... Sai kawai bawan Allahn Nan yayi shiru da bakinsa nayi nacin
duniyar nan Amman yaki karasa mana zance, haka muka tasho Aunty Ladi nata zugani
kada na kuskura na Bari ta auri Mai maiko duk yanda zanyi nayi Naga hakan Bata faru
ba. Nayi ta fama duk Wanda zezo gidan Nan gurin yarinyar nan zezo duk kuwa da Fadi
tashin da nake akan su Salma amman a banza, maganar dai daya ce Zahra, ni Kuma nayi
Alkawarin badai Zahra tayi aure ta barmin Yara a gida ba,Kuma badai ta auri Mai
rufin asiri ba, gashi kuwa ta Kare a Wanda ko asalin kirki bashi dashi Abu daya ya
tsaya min a Rai yanda Naga gidan da zata zauna da abin yaso razani sosai Dan ba
haka na zata ba, amman duk da hakan ma yayi tunda ai gidan ma Malaminsa ne ya bashi
aro su zauna, Kinga kuwa karshe sai dai a Kare a yawon haya cikin Yama yamar matan
alarammomi, Kuma wannan kayan da ake qafafar an saka a gidan karshen wasu kayan
saidai a sayar Dan Babu abinda za'aci dasu Dan an sawo da zimmar su tafi Abuja sai
gasu sun Kare a gidan Alaramma".
Ta fada cikin izgilanci.
**
Duk yanda Zahra taso ta kwantar da hankalinta abin ya faskara dan da gaske zulumi
takeyi na yanda zata fuskanci wannan sauyin da yazo Mata a bazata Wanda Bata tab'a
tunanin hakan ba ko cikin mafarki, lallai tayi zaton daga kan Mushahu komai ya
kwaranye Amma sai wata matsalar ta taso wadda tafi ta baya.
A kwance ta wuni duk ta tsangwami kanta Sajida sai tausarta take duk da itama tata
zuciyar a kusa take Dan da gaske tana tausayin zahrar ba kadan ba.
Gurin karfe biyu ne sukaji alamar Kamar anyi Baki a gidan da alama ma da dan
damarsu.
Sajida ce ta fito ta gaishesu zata koma cikin ne Ammah tace taje ta Kira Mama tace
tazo su gaisa da Baki Iyayen Musbahu ne daga kano.
Ta fita tana mamakin to meya kawo su Kuma.
Tare suka shigo da mamar Dan sajidar na fada Mata ta nufo dakin cikin rawar jiki.
Ciki Sajida ta wuce yayin da mamar ta zauna tana gaishe da bakin nasu Kafin Inna
maimuna ta Fara Mata bayanin Maman Musbahu ce tazo da 'yan uwanta ta bada hakurin
abinda ya faru Wanda ita kanta Bata San yanda akayi ba sai daga baya ake fada Mata
shine tazo taji ko da yanda za'ayi a gyara matsalar tunda ta dawo hayyacinta take
cikin damuwa domin kwata kwata Musbahun baya cikin nutsuwarsa tun bayan samun
labarin an Aurar da zahrar, ganin lamarin nasa ba sauki ne yasa suka nufo nan Ashe
har da yaron sukazo sun jima a gurin Alhaji ma kafin su shigo nan din, hakuri kawai
ya basu akan aikin Gama ya Gama tunda yanzu matar wani ce ita.
Kallonsu Mama ta karayi tana tambayar "Ina mamar tasa take"
Hajiya Nafisa kanwarta ita ta nuna Maman Musbahun tana fadin "gata nan"
"Ayya Allah sarki Hajiya sai hakuri Allah Bai nufa matarsa bace ba sai dai yazo ya
duba wata tunda da sauran yaran a gidan".
Mama ta fada tana kafe Hajiyar da ido.
"Kayya a yanzu dai bana tunanin haka zata yuwu sai ko a gaba tunda ban taba ganin
abinda Musbahu ya kwallafawa Rai ba Kamar auren yarinyar nan tunda kuwa ya rasa ta
bansan Kuma lokacin da ze Kara maganar wani auren ba".
Sun Dan Jima kafin Ammah ta tashi ta shiga gurin su zahra tace ta fito su gaisa da
Baki zasu tafi.
Jiki ba kwari ta nufo kofa doguwa rigace a jikinta kirar Bahrain Mai duwatsu har
kasa blue black gyqlenta kwai ta Dora a kanta Dan Sam Zahra Bata fiye son saka hula
ba a kanta Dan Sam santsin gashinta baya Bari hular ta zauna ta dunga zamewa kenan.
Cikin takunta na nutsuwa ta shigo falon hade da sallama Kanta na kallon kasa ta
karaso cikin nutsuwa ta zauna gefen Ammah a kasa kan carpet, tunda ta shigo suka
bita da idanun kowa da abinda yake ayyanawa a zuciyarsa.
"Masha Allah! tubarakallah 'yata matso kusa dani dole my son yayi kamar ya zauce
da labarin rasaki ya riskeshi" abinda Aunty Nafisa ta fada kenan tana nunawa Zahra
kusa da ida, jiki ba kwari ta karaso ta zauna tana gaishesu.
Suka amsa jiki a sanyaye su kansu sun San dansu yayi wani babban rashin da maida
shi sai nufin Allah, tunda Daman shiya hada shi da Zahrar kuma shiya raba lokacin
daya so.
Nan sukayi sallama suka fita cikin matukar jimami Dan da gaske sunyi rashin sirika.
A daki Zahra kwanciya bayi ta rufe fuskarta da hannu biyu Batasan lokacin da hawaye
ya zubo Mata ba, Wai shike nan komai ya Zama past tsakaninta da Musbahu duniya ba
tabbas. sajida na kallonta Bata hanata ba Dan itama Saida ta matse, lokacin zahra
na falo Mushahun ya Kira wayar ta, sajidar ta dauka yanda taji maganarsa ko
rantsuwa tayi bazatayi kaffara ba kuka yake shima da idanunsa Dan abinda ya fada
kawai ya karya Mata zuciya, kalamai ne na bankwana ga masoyi da da given off akan
Abu, da kyar ta iya fada Masa ba zahra bace itace magiya yayi Mata dan Allah ta
fito Masa da zahra yayi Mata sallamar karshe Amma hakuri kawai ta bashi tunda yanzu
Zahra matar aure ce bashi da hurumin yin magana da ita.

Sun Dade a haka kowa da abinda yake sakawa a zuciyarsa nkafin su jiyo maganar
Magaji Yana fadin "Ammah ga Ya Mushahu zaku gaisa yazu tafi ne".
Su biyu suka shigo suka gaishe dasu Ammah a nan Inna maimuna ke fadin "kayi hakuri
da hukuncin Allah kaji kada kayi fushi da mahaifiyar ka itama bayin kanta bane duk
uwa bataqi ace danta yafi kowa sa'ar abokiyar Zama ba, irin wannan matsalar ta Jima
tana bibiyar yarinyar Nan to munyi zaton daga kanka abun ya Kare sai Kuma ya canza
salo akan mahaifiyar ka, kayi hakuri ka fawwalawa Allah komai shi ze baka wadda
tafi Zahra daman Allah hukunta kai ba mijinta bane ayi hakuri".
Kansa Yana kasa tunda ta Fara maganar wani Abu ya tsaya masa a makogwaro yaji Sam
ya kasa magana sai Aliyu ne ya amasa da "ba komai Mama haka Allah ya nufa, Allah ya
Basu zaman lafiya mu zamu koma".
"To Allah ya tsare ya baka mace ta gari wadda zata maye maka gurbin Zahara'u" Inna
ta fada ita kuwa Ammah kasa magana tayi dan da gaske yaran tausayi suke Bata sun
kwallafa Rai da juna Amma akayi musu karan tsaye, a zuciyarta ta ayyana "Allah ka
biwa yaran Nan hakkinsu duk Mai hannu a cikin Bata lamarin Nan kayi Mana sakayya da
gaggawa Dan isar Annabin Rahama Muhammad s.a.w.w."
Ta window zahra ta leka lokacin da suka fito daga falon kamar ance ya juyo sai
ganin zahrar yayi tana kallonsa da sauri ta juya ta rufe fuskarta da hannu ta saki
wani marayan kuka ta zube a gado. Su Kuma suka fita zuciyarsa Kamar zata Kama wuta
dan ganinta ba karamin fami ya zamar Masa ba, har ji yayi Yana wani layi Kamar ze
fadi.
Magaji ne ya shigo falon Yana fadin "Sun tafi, wallahi Ammah naji tausayin Ya
Musbahu sosai kinsan har gurin Baba malam yaje Amma magana daya dai kowa yake fada
masa yayi hakuri, bayan mun fito ne yace na nuna Masa mijin Aunty zahrar na fada
Masa ai shine suka Fara gaisawa dashi bayan sun gaisa da malam, shiru yayi sai
kawai Naga ya dafe kansa Yana girgizawa, yace na hakura da zahra nasan wannan baze
taba sakin zahra ba. wallahi Ammah sai Naga yana goge hawaye gaskiya Allah saiya
saka musu wannan ai zalunci ne Kullum idan Aunty zahra ta samu miji sai an samu
matsala".
Ya fada Yana Jan tsakin takaicin.

"To magaji babu yanda za'ayi haka Allah ya hukunta sai hakuri".
Bayan tafiyarsu da Kamar awa daya Abdul Hakeem ya shigo ya fadawa Ammah tazo Abba
Yana kiranta.
A bedroom dinsa ta sameshi Yana tsaye ya goya hannunsa a baya Yana Dan Kai kawo a
tsakar dakin.
Sallam tayi Masa ya amsa sannan ya sauke hannunsa ya nufi gefen gadon inda Ammah ta
zauna tana tambayar "Lafiya kuwa Abba meya faru Naganka a haka?"
Ajiyar zuciya ya sauke Yana fadin.
"Da matsala gaskiya yaron nan ne yazo a rikice yana kuka Kamar yaro karami da kyar
muka lallashe shi nida Abdul Hakeem ga mahaifiyarsa da 'yan uwanta kingansu dai
nasan mazan ne suka ce ba ruwansu shine ita da kanta ta taso tazo wallahi hawaye
bibiyu ta rinka yi min akan na rufa Mata asiri na warware wancan auren a maida kan
Musbahu abin har abin tausayin wallahi, shi yasa na turosu cikin Dan ku Basu hakuri
tunda wancen zance ya wuce Kuma ji nayi da nauyi na Kira malam wallahi tunda ganin
Mahmud nake Kamar Dan cikinsa Kinga na Kira shi akan maganar ai Bai kyautu ba, to
bayan sun tafi ne Abdul Hakeem ya Kira Hassan ya fada masa shine ya kirani Yana min
magiyar Dan Allah a rakata dakinta yau basai gobe ba da tun farko ma ankaita da
hakan Bata faru ba yasan wasu ne daga nan zasu Gaya Masa tunda Yana da mutane
sosai suce ai tana gida ma yayi bata tare ba suyi tunanin ko Babu auren ne, Dan
haka Nima nayi na'am da maganar tasa, kuje kuyi duk abinda ya kamata da magariba
zan mikata dakinta da kaina in Sha Allah, na Kira malam ma na fada masa."

"To hakan yayi duk abinda ka yanke dai dai ne Allah ya nuna Mana lokacin".

"Amin ya amsa"....
✨✨

AUREN HUCE HAUSHI


✨✨
❤️❤️
❤️❤️
💋💋
💋💋

MAMAN FATIMAH.

PAGE SEVENTEEN (17)


_________ Karfe biyar mai kyau motar da Alhaji Jafar ya tuko da kansa daga shi sai
Zahra a ciki daga bayansa Kuma Abdul Hakeem ne a wata motar ya biyo Abban nasu bisa
umarninsa,suka dira kofar gate din gidan Zahra,sau biyu Abban yayi horn Mai gadin
ya leko da yaga Alhaji ne da kansa tunda daman ya San Alhajin farin sani yayi
sauri ya bude kofar suka shigo gaba daya, da sauri Mai gadin ya karaso Yana budewa
Alhajin kofa Yana gaishe shi yayin da Abdul Hakeem ya budewa Zahra ta fito suka
zagaya Gurin da Abban yake, Abdul Hakeem suka gaisa da Mai gadin sannan Abban ya
Kama hannun Zahrar ya nufi kofar main falon da ita, tasha farar laffaya Mai adon
kananan flowers pink, jikinta kamar an Mata barin turare sai tashin kamshi take Mai
Dadi. A bakin kofa suka Hadu da Mahmud din ya nufo kofar da sauri Dan Yana bedroom
dinsa yaji shigowarsu tun bayan anyi la'asar Baba malam yace Alhajin yace ya same
shi a can gidansa da yamma za'a kawo Masa iyalinsa.
Matsawa Mahmud din yayi daga bakin kofar Yana yiwa Abban sannu da zuwa sannan ya
mikawa Abdul Hakeem hannu suka gaisa, kan kujera Abban ya zaunar da Zahra sannan ya
umarci Mahmud daya zauna kusa da ita shi Kuma ya zauna a kujerar dake kallonsu,
Abdul Hakeem Shima ya zauna, sai falon ya dauki shiru, gyaran murya Abban yayi
kafin yace "Abdul Hakeem yi Mana addu'a' bayan yayi doguwar addu'a sun shafa
Abban yace "To Mahmud ga matarka nan na kawo maka bani na baka ita ba Allah ne ya
baka ni nawa idawa ce, gata Nan amanace a gurinka kada ka zalunce ta duk inda
yanayin rayuwa ya kaiku na baka ita ne saboda na yaba da nagartarka na Dade Ina
monitoring dinka ban tabaji ko ganin abun ashsha ba a tare da kai, kullum addu'ata
Allah ya bani ikon sauke nauyin marainiyar Allah dake hannuna, kuma Alhamdulillahi
na sauke gata nan marainiya ce Bata da uwa Bata da uba ba wa ba kani ita kenan
iyayenta duka suka rasu suka barta, kada ka zalunce ta Dan girman Allah ka tausaya
Mata saboda Mai rauni ce, ka zamar Mata uwa uba abokin Shawara kuyi dariya tare
kuyi kuka tare ka jibinci lamarinta gwargwadon iyawarka. Ina Kuma Kara gode maka
bisa share min hawayena da kayi baka watsamin kasa a ido ba lokacin Dana baka
aurenta, na gode kwarai Allah ya saka maka da Alkhairi ya yaye maka damuwarka ya
kawo maka mafita a bisa lamuranka".
Suka amsa da "Amin"
Sannan yaci gaba da fadin "ke Kuma Uwata ga mijinki nan kiyi Masa biyayya abisa
abinda Bai sabawa Allah ba, ki girmamawa shi ki kiyaye bacin ransa ki kiyayie
mutuncinsa da rike Masa sirrinsa kindaraja mas iyayensa da 'yan uwansa lokacin da
Allah ya hukunta ku hadu dasu,nkiji tsoron Allah a cikin zamanta kewarku ki saka
hannu ki Barbi duk abinda ya biyo bayan aurenki dashi Mai Dadi ko sabanin hakan.
Dan Allah ki kwantar da hankalinki kiyi hakuri da abinda Allah ya hukunta a kanki
komai Kika gani rubutacce ne daga Allah sai dai mu 'yan adam mu karasa shi, Amma
tun ran gini tun ran Zane dama haka kaddarar take, ko shi mijin naki idan yayi
nazari zega wata kila wannan kaddarar auren ce ta rabo shi da asalin inda yake, to
Dan haka kowa ya rike tasa kaddarar wata Rana sai labari komai na duniya Yana da
iyaka ikon Allah ne kawai bashi da karshe, Allah yayi muku Albarka ya kauda fitina
a tsakaninku ya tabbatar da Alkhairi a cikin rayuwar aurenku, Mahmud sai anyi
hakuri da Mata su masu rauni ne kwarai da gaske".
Tunda Abba ya Fara magana yaji kamar ya dauko wani gaigimemen dutse ya Dora Masa
aka.
Cikin ladabin da baisan Yana dashi ba ya furta "in Sha Allah Abba ba wata damuwa
Kuma amana na karba na rike Allah ya bani ikon saukewa nike da godiya Allah ya saka
da Alkhairi ya Kara Nissan kwanaki masu Albarka"
"To Masha Allah, Abdul kayi Mana addu'a mu tafi kada almuru tayi Mana a nan, Uwata
ki daina kukan Nan haka bana sonsa kiyi hakuri kowa da haka ya girma Allah yayi
Miki Albarka, ga makullin motarki wadda mukazo da ita takice na sai miki, kudin
dayar ta wajen Abbie suna gurin Alhaji muttaka tunda aka sayar da ita nace ya juya
Miki kudin zuwa lokacin da za'a bukaci wata motar Dan haka in Sha Allah cikin sati
Mai zuwa za'a kawo Miki dayar ma".
Suka tashi suka fita Mahmud yayi musu rakiya har gurin mota Saida suka tafi sannan
ya dawo ciki, a inda ya bar zahrar anan ya sameta ta kwantar da kanta a kan
cinyoyinta tana kuka Mai tsuma zuciya a hankali ya zauna kusa da ita yasa hannu ya
dago kanta daga jikin cinyoyinta idanunta a rufe sai tsiyayara da ruwan hawaye
suke. Ba zato ba tsammani kawai taji ya sakata a girjinsa ya kwantar da kanta ya
saka hankici Yana share Mata hawaye, daya hannun Kuma Yana tapping din bayanta
kamar yanda ake yiwa yaro idan ana so yayi shiru Yana kuka, jikinta gaba daya ya
dauki rawa ta taso da niyyar zare jikinta Dan wani Abu takeji duk ilahirin jikinta
Amma Dan bawan Allan nan yayi kememe yaki sakinta ba arziki ta hadiye kukanta, sai
sauke ajiyar zuciya kawai ba kakkautawa saida ya tabbatar ta Samu dan nutsuwa
sannan ya saketa Yana fadin " sorry Baby ki daina kuka bana son kuka Sam koda kuwa
na karamin yaro ne".
Hannunta ya Kama ya mikar da ita ya nufi daya daga cikin bedrooms dinta guda biyu
da suke mallakinta, Saida ya zaunar da ita a gefen makeken gadon sannan ya juya ya
nufi kofa Yana fadin " it's time for prayer"
Ya fice Yana ja mata kofa.

Sai ta dauki kusan minti biyar kafin ta Samu kuzarin warware Laffayar dake nannade
a jikinta, doguwar rigar material ce a jikinta anyi Mata dinkin fitted gown tayi
Mata kyau sosai kofar data gani ta nufa tasan toilet ne, lokacin data shiga abin ya
girgizata irin kayan amfanin data gani a ciki ita ba bakuwar abin bace tasan ba
kananan kudin aka narkar ba a cikinsa, abin ya Bata mamaki sosai sai dai wa zata
tambaya? ta Jima a ciki kafin ta dauro alwala ta dawo dakin.
Ido ta ringa wurgawa ko zata ga sallaya tunda ita dai bakuwa ce a dakin can gefen
sofa taga wani stool kamar coffee table da sallayun akai ta shimfida ta Fara
sallah.
Tana cikin sallah ne taji kamar karar door bell kamar sau biyu, Saida ta idar ta
tashi ta fito har lokacin tana share hawaye jefi- jefi, gurin kofar ta karasa ta
bude Sajida da Hameeda da Mujiba ta gani ai batasa lokacin data fada jikin Sajida
ba tana dakin kuka Mai tsuma zuciya.
Ciki suka shigo Sajida na fadin "haba bestie wallahi Dana San har yanzu baki daina
kukan Nan ba da bazamu biyo bayanki ba, haba Ashe bazaki karbi kaddara yanda tazo
Miki ba? ki Kuma godewa Allah a kowane Hali Kika Samu kanki, bake Kika halicci
kanki ba ballantana ki tsarawa kanki yanda Zaki rayu, kin taho kina kuka duk kin
dagawa Ammah hankali itama, kin kyau kenan? haba kiyi hakuri Dan Allah ki share
hawayenki wallahi nasan yanzu zuciyar masu binki da mugun nufi tana can kamar zata
fashe Dan ba haka suka soba duk da bansa daga Ina matsalarki take ba, ai kodan
makiya kin kwantar da hankalinki ki rungumi mijinki ki ba mara d'a kunya, Amma kin
tsaya kina wani Abu kamar wata karamar yarinya"
Tayi tsaki tana kallon zahrar da tayi kozai kozai ido ya kode Mata abinka da farin
mutum.
Suma su Hameedar ban baki suka dunga yi Mata, da kyar ta hadiye kukan ta kallesu
tana fadin "wallahi bazaku Gane bane ni kadai nasan me nakeji, komai ya kwance min
Sam duniyar bata mun dadi".
"Hakurin dai zakiyi ki Kuma yawaita addu'a in sha Allah komai ze wuce kamar ba'ayi
ba, muda muke son next year by now mu dawo suna".
Sajida ta fada tana murmushi.
Wani kallo zahrar tayi Mata ta juya kanta gefe tana fadar "Allah ya kiyaye min wata
haihuwa can".
Mujiba ce ta kwashe da dariya tana fadar "A'a Banda cika Baki dai 'yan Mata Nan da
labari yasha banban zamu tsinceki kina faman 'yan amaye amaye, lokacin ne Zaki
gane Baki da wayo ko ba wata haihuwa can ba?".
Zumburo Baki tayi tana fadin "sai kiyi Kuma haka kawai Zaki jaza min, wani ciki ko
dadin fada ma Babu".
Saima zahrar ta zame ta kwanta, tana jinsu suna ta faman zolayar ta har aka Kira
sallar insha'i a Nan sukayi sallah kafin su shiga Kara gyara Mata Fallon da Kara
masa freshner da turaren wuta Hameeda ta Kara karfin A C a falon ta gyara cutains
din, bedroom din data fito suka shiga Mujiba bakinta ya kasa shiru tunda dai suka
Samu zahrar ta daina 'yan koke koken sai ta balle da santin gidan Dan bayan sun
idar da sallar ba inda Bata shiga ba ta leka can ta shiga can bedroom din Mahmud ne
kawai Bata shiga ba tunda a rufe yake, fada take "wallahi zahra ki Kara godewa
Allah, irin wannan haduwa haka wallahi ko makiyi Saida yaki fada Amma dai duk wani
gata kin same shi sai dai fatan zaman lafiya kawai".
Ita dai Zahra ba baka sai kunne.Dan ita kadai tasan abinda ke Kai komo a zuciyar
ta, su inda suka dosa daban ita inda ta dosa daban, ko tayi musu bayani ba ganewa
zasuyi ba, domin su duka ba wadda ta tab'a shiga irin gararin data shiga, rayuwa
Rumi rumi saika Gama sakankancewa da mutum Rana tsaka Abu ya lalace, uwa uba ganin
da tayiwa Musbahu ba karamin famu yayi Mata ba, saboda da ta cire shi daga ranta
kwata kwata ta hakura, Amma tana ganinsa komai ya rikice Mata da tana zargin kamar
da niyya mamansa tayi haka saboda ya taba fada mata Maman nasa taso ya auri 'yar
Yayarta shi Kuma ya ringa sharewa ana haka ne Allah ya had'a shi da zahrar abinda
ya kawo karshen wancan dambarwar kenan. Amman tasowar mamansa da 'yan uwanta dashi
kanshi takanas ta kano har Azaren don bada hakuri da neman gyara idan lamarin Mai
gyaruwa ne, sosai abin ya tashi hankalinta, wata sabuwar soyayyar sa ce ta sake
bijiro Mata idan tana tuna yanda yaci buri a irin wannan ranar da za'a kawo Masa
ita a matsayin matarsa ta sunna halalinsa, irin abinda yake fadin ya tanadar Mata
ita a wancen lokacin idan Yana fada kamar zata nitse kasa dan kunya Amma shi ko a
jikinsa.
Wasu sabbin hawayene suka zubo Mata masu zafi tana ayyana shike nan komai ta Zama
tarihi, ga inda kaddara ta kawo ta gurin da ba'asan darajarta ba ko alama sai aukin
taba Mata jiki da yake Wanda ta fashimci hakan tun haduwarsu ta farko, ba kunya ya
wani saka hannu ya rungumota Wama ya sani ko Dan duniya ne aka hadata dashi, tunda
ance ba Wanda yasan asalin sa kuma tasan yanda yake din nan ko bashi da sisi mata
zasu ringa kawo Masa rida tunda sun ganshi smart dashi.
Wani tsaki tayi tana ayyana to Ina ruwanki da wani smartness dinsa.
Mahmud Bai dawo gidan ba sai bayan sallar insha'i ganin takalma yasan akwai baki
cikin gidan baya raba daya biyu 'yan uwanta ne ko kawaye, dakinsa ya wuce yayi
wanka ya canza kaya ya fito falo, bai shiga dakinta ba daga inda yake yana jiyo
mganganun bak'in, ita dai baiji tata maganarta ba Sam Zama yayi yana daddana wayar
hannunsa.
Acan Kuma dakin Zahra Ya Abdul Hakeem ne ya Kira wayar Sajida Yana fada Mata su
fito su tafi ya dawo daman lokacin daya basu kenan bayan sallar insha'i lokacin
daya kawo su.
Sun fito falone suna zolayar Zahra Basu kula da mutum ba sai da suka sauko daga
steps din da ze sada ka da corridor din bedrooms din suka ganshi a zaune Yana ta
faman Danna waya, kallo daya Zahra tayi Masa ta kauda Kai haka kawai taji gabanta
ya fadi, ta rasa wace irin masiface wannan.
Kansa ya dago yana amsa gaisuwar su Sajidar Yana fadin "har zaku koma ne?".
Hameeda ce tayi farat tace "To ba dole mu tafi ba yallabai tunda angon yaki zuwa
ya sayi bakin amaryarsa ba Yana ganin Mai araha ce bai Sha wahalar komai ba aka
bashi ita".
Ba Zahra da aka ciwa fuska a fakaice ba hatta Sajida da Mujiba Saida sukaji kamar
kasa ta nutsa dasu a gurin Dan kunya, gaba daya suka zubawa Hameeda ido har shi
uban gayyar, wani abune Wanda Zahra Bata taba tunanin Hameeda zatayi Mata ba, dan
wannan cin fuska ne qarara bako kawaici a cikin maganar ko kad'an. Zahra kasa gaba
ko baya tayi ta tsaya a gurin kawai, su sajida ma rasa ta cewa sukayi shi kuwa uban
gayyar wayar dake hannunsa ya aje Yana kallon Hameeda direct kafin yace " waya
fada Miki Mai araha ce bakiji sunanta ba? Zahra fa kinsa ma'anar sunan kuwa?
tauraruwa fa a cikin taurari a gurinki take Mai araha Amma ni a gurina tafi zinari
daraja, bari na baku indai abin sayen Baki ne in dai shi ne abinda ke shaida Kima
da darajar mace a irin wannan ranar gurin kawayenta, ina zuwa". Ya fada Yana
mikiwa ya nufi hanyar bedrooms dinsu, tunda ya wuce zahra ta juya da sauri ta nufi
daki Bata yi musu ko sallama ba.

Bai jima da shiga ba ya fito da wata katuwar leda da Kuma envelope guda uku a
hannunsa. Yana zuwa directly Hameeda ya nufa ya Mika Mata ledar da envelope daya
sannan ya baiwa Sajida da Mujiba Suma dai dai Yana fadar "ga kayan sayen bakin Nan
a cikin wannan envelope din Kuma kunsha ruwa a hanya".
Ba kunya Hameeda tace yanzu naji magana ai shi tuwon girma miyarsa Nama mun gode".
Taja katuwar ledar tayi gaba abinta mujiba ma tabi bayanta har suka fita Sajida
Bata motsa ba ita kollon ikon Allah take akan Mahmud Wai wannan shine Almajirin da
ake ta yayatawa a aurawa Zahra har Hajiya Mama na yiwa Abba magiyar kada ya Fara
wanna danyan aikin tab wallahi da sake ita tafa abinda ta gani ga tare dashi ai da
hasashe ne take yanzu be taga zahiri. Ganin sun fita yasa sajidar aje Masa
envelope dinsa a gefen shi tana fadin "kabar abinka na gode, ni fatana ka rike min
bestie da mutunci da amana yafi ka bani duk abinda ka mallaka, bansan Kai ko waye
ba Amma jikina Yana bani kana boye wani Abu tun lokacin Danazo gidan nan da Kuma
irin kayan danaga an kawowa bestie nasan Kai ba kaskantanccen mutum bane, Ina
hadaka da girman Allah kada ka bautulcewa Iyayenta da suka baka ita kaji tausayinta
marainiya ce, Dan Allah nasan duk inda ka fito ba karamin guri bane ka Zama
garkuwarta ka zamar Mata bangon da zata jingina taji dadi duk rintsi. Dan Allah ka
Bata kulawa Zahra 'yar gata ce kaddara ce ta zaunar da ita a kasar nan da Kuma
kawaicin kakanninta suka hakura suka barwa Ammah ita, Dan Allah ga amana Nima na
baka kamar yanda iyayenta suka baka kaji tsoron Allah a cikin zamantakewar ka da
ita na San Nan gaba zaka samu zabinka ko Kuma tuntuni kana dashi Dan Allah kada ka
wulakanta ta.. na rokeka ka Zama adalin shugaba a gurinta idan kaji yanda rayuwa ta
dunga jujjuyata zaka tausaya Mata matuka, Dan Allah badan niba...."
Da tayi gaba ta nufi kofa Bata taji me ze fada ba domin hawayene suka ciko Mata
idonta idan tace zataci gaba da magana kuka zata fasa masa ne. A bakin kofa sukayi
kicibus da Mujiba wadda ta dawo kiranta ganin shirun ya yi yawa.

✨✨
✨✨
AUREN HUCE HAUSHI

✨✨
✨✨

💎PAGE EIGHTEEN💎

STORY

AND

WRITTEN

BY

MAMAN FATIMAH.

_________ Bayan wucewar Sajida Mahmud ya Dade Bai tashi ba, kwarai yarinyar ta
burge shi matuka, da gaske take son Zahra domin furucin da yarinyar can tayi yayi
touching dinta sosai, lallai ya tabbatar son da take yiwa Zahra bana Wasa bane shi
tun lokacin da Magaji ya fada masa ta baro syprus Dan kawai ta halarci bikin zahrar
ya jinjina Mata duk da suna hutu Amma yasan irin wadannan daliban ba kowane hutu
suke zuwa gida ba sai dai idan iyayen sun sunci sun tada Kai.
Envelope din data aje masa ya kalla yayi wani killer smile ya zurata a aljihun
Wando Yana Kara wani murmushin Wanda shi kadai ya barwa kansa sani.
Yaso ya shiga dakinta sai ya share kawai Dan yasa baya raba daya biyu kuka take Dan
da gaske koshi baiji dadin furucin da akayi Mata ba Kai tsaye bako rusunawa a ciki.
Lokacin da Abdul Hakeem ya Parker motar a parking lot na gidan Sajida ce ta farkon
ficewa daga motar zuciyar ta na Mata wani zafi Dan da gaske idan ta tsaya zata
shatawa Hameeda rashin mutunci ne na karshe Wanda zata Dade Bata manta ba, dan da
gaske an shirya ne kawai dan a tozarta Zahra a gabanta mijinta, shi yasa kenan
lokacin da zasu ltafi ta shiga part din Mama Kiran Hameedar akan ta fito suje, taji
Salma na fadin saura Kuma ki kasa fada ki dawo Mama ta tumurmushi banza, ita Sam
Bata kawo komai ba kawai dai ta dauka wani abune can tsakaninsu saida hakan ta faru
ta Gane me ake nufi da waceccen maganar. Tana jin Mujiba na kwala mata Kira lokacin
data nufi karamin gate wanda ze sada ta da cikin gidan, batabi ta Kanta ba tayi
wucewarta ciki ta kyalesu.
Koda ta shigo part din Ammah directly bedroom din da suka kwana ta wuce tana yiwa
su Aunty Hasana sannu har ta shiga ta fito tana fadin "Aunty Dan Allah idan su
Hameeda sun shigo kice su raba kayan su biyu kwai Banda ni". Ta koma da sauri Dan
tana jiyo maganar su a kusa alamar Nan suka nufo.

Tun shigar Zahra bedroom din Nan ta kwanta rub da ciki take risgar kuka Kamar ba
gobe, Hameeda ta Bata mamaki Bata taba zaton irin wannan ranar ba a tsaknainta da
Hameeda cewa take ko kowa ya nuna Mata naqi a bangaren Mama ita kadai zata tsaya a
bayanta duk runtsi duk wuya saboda a baya ba Mai cin fuskar ta a dakin Mama makukar
tana gurin Koda kuwa mamar ce, Amma yau Hameeda da bakinta Kuma a gaban idonta take
fadar magana irin wannan, to meya canzata daga Hameedar data sani Mai sonta da
kaunar ta da Bata kariya da kulawa a kowane janibi. Saida tayi Mai isarta har ta
baiwa uku lada, sannan ta hakurkurta da Kanta ta tashi zaune. Kanta taji ya Sara
Mata a hankali ta furta "Alhamdulillahi ala kulli halin. Allah na gode Maka duk
abinda kayi nufi a gareni na karba ka bani ikon cinye jarabawar Nan dan isar Annabi
Muhammad s.a.w.w".
Hannu tasa ta dafe Kanta dake matukar Sara Mata, wannan wace irin rana ce a gareta?
ranar da duk wasu masoya keda tarin burika a Kanta Amma ita ranar ta ta farko ta
kasance ranar cin fuska daga inda Bata taba zato ba, ba tarairaya duk burin da suka
dade sunaci na irin wanna ranar ya tashi a banza. "Astagafirullah Ubangiji ka yafe
min zunubina daya janyo min irin wannan rayuwar Mai tarin qalubale a cikinta".
Ajiyar zuciya ta sauke tana Kara dafe Kanta da gaske jinsa take Kamar ze rabe gida
biyu, ba zato ba tsammani taji an bude kofa Bata daga Kai taga ko waye ba dan
kamshinsa kadai ya Isa ya fada Mata Mai shigowar, Kuma ma waye ze shigo haka Kai
tsaye a irin wannan lokacin, sallama yayi Mata Amma Allah baisa ta amsa Masa a fill
ba ta dai amsa a zuciyar ta.

Takowa yayi a hankali har zuwa inda take zaune, har lokacin Kuma Bata daga Kai ta
dube shi ba farar ledar dake hannunsa ya aje kusa da ita ba tare daya tanka Mata ba
ya juya ya nufi kofa yana juya baya ta dago da sauri ta kalli bayansa kananan Kaya
ne a jikinsa sabanin dazu da yake sanye da wani lallausan yadi fari tas da hula,
sai taga Kamar yafi kyau yanzu akan dazun, kananun kayan sunfi karbarsa akan manyan
da yake sakawa, hannun daya saka ya Kama handle din kofar idonta ya Kai taga hannun
wani fresh dashi Kamar Mai rayuwa a kasashen sanyi. Ganin Kamar ze juyo ne yasa
tayi saurin kauda Kanta Dan kada ya kamata da wadannan idanun nasa tana kallonsa.
Kofar tabi da kallo bayan ya fice a hankali ta sauke ajiyar zuciya da gaske fa
mutumin Nan yana Mata wani irin kwarjini, ga wani tsare gida naba gaira ba dalili
da yake saiya karta Abu ya wani maze Yana Shan kamshi.
Karan bude kofar ne ya dawo da ita daga tunanin data shiga na wucin gadi, kusa da
ita ya zauna daf da daf dan ji tayi Kamar numfashi daya suke sharing dashi, a
hanakli yasa hannu ya dago fuskarta data Kama idon ta rufe, a zuciyar ta tace "na
bani ni Fatima shi Kuma kome faskar Nan tawa tayi Masa? shi dai ya taba jikina
kawai ya sani, muryar shi ta jiyo cikin deep voice yana fadin "Pls open your eyes
and look at me mana".
Kai ta shiga girgiza Masa alamar a'a.
Shi abin nata ma mamaki yake bashi, a ranar da suka samu wannan arangamar da ita
soron gidan Baba malam yaga ta rufe idanu ya dauka ko tsabar razanar zata fadi ne.
Amman sai yaga abin na neman ya Zamar Mata jiki indai zata ganshi to kuwa sai ta
rutse idanu Kamar taga wani abun tsoro, a haka zasu rayu da ita ai baze yuwu ba
gaskiya dole yayi wani abun daze cire koma meye yake haddasa Mata hakan a tare
dashi.
"Ok Ashe zamu kwana a haka kenan tunda bazaki bude idanun ba, ko Kuma wallahi na
shayar dake mamaki yazun nan".
Shiru tayi Masa kirjinta Yana fat, fat da sauri kusancin yayi yawa duk ya
kanainaye ta.
Batayi zato ko tsammani ba taji harshensa akan fata idonta Yana lasa yana busa
mata iskar bakinsa kamshin Lister mint mouthwash Yana dukan fuskarta ciki Shirin
fita hayyaci tayi baya da sauri ta fada kan gadon da baya idanun nata tar akan
fuskarsa da yana mata wani Yana Mata wani kallon kasa - kasa nan da Nan taji tsikar
jikinta tana tashi sai hawaye zurrr...
"Why! meyasa? Ai da sai ki barni na kwashe abinda yake hanawa kina kallon nawa
Mana, oya tashi abinci zakici bazaki kwanta da yunwa ba kisa na Fara karya
Alkawarin dana daukar Iyayena na kula dake,dan kowa amanarki yake bani da jaddadda
min na rikeki da amana da gaskiya cikinsu harda bestien mu kuwa".
Ya fada a kasalance Yana kashe Mata ido.
Sai Kuma ya dan zamo kadan ya dauko plate Wanda ita Sam Bata San lokacin daya ajesu
a gefenta ba, ledar ya bude wani kamshi ne ya doki hancinta Mai shegen Dadi kaza ce
wani irin gashi akayi Mata Kamar na tsire da vegetables a ciki ya juye Yana fadin.
"Oya tashi kici kafin ki kwanta kinsan yunwar dare tana kawo ciwon ulcer,kada ta
kamaki ace Ina barinki da yunwa ni d'an malam gara na Kara kiwataki duk wanda ya
ganki ace Masha Allah! Kamar ba matar Almajirin Baba malam ba".
Ya fada da alamar zolaya a karshen maganar tasa. Itafa Yana Bata mamaki wallahi
zata iya rantsewa idan aka saka Masa hannu a Baki baze ciza ba amma dubi yanda ya
wani zage yana magana Kamar bashi ba.
Ganin da gaske zata Bata Masa lokacin shi Kuma Yana da abinyi da yawa yasa ya matsa
sosai kusa da ita ganin Yana nema Kara mannata a jikinsa yasa tayi saurin tashi
zauna tana kikkibta idanu tana kallonsa. Da hannu ya nuna Mata plate din, cikin
Rashi kuzari a maganar tata tace Masa "na koshi bazan iyaci ba kaina ciwo yake".
Ta fada murya a shagwabe ga daman tasha kukanta.
Sai yaji ta Kara bashi tausayi abun ne yayi Mata goma da ashirin.
Cikin sigar lallashi yace.
"To kici ko kadan ne saina kawo Miki magani kisha kinji"
Ya fada yana Kara nuna Mata plate din da idonsa, kadan taci duk a takure shi har
mamaki take bashi a yanda yake ganinta ai ta wuce ace tana jin irin wannan kunyar
ko tsoron irin haka, tunda da gani wayayya ce ta ajin karshe, ga Kuma yanda ta
ringa ta'ammali da samari kala kala, a yanda yaji labari fa sau uku ana fasa
aurenta Wanda ba Wanda yasan dalilin hakan, yasan kawai rainin hankaline irin na
Mata, yanda zamanin ya Zama abinda ya Zama Amma dai ai gaskiya zatayi halinta komai
daren dadewa.
Ba laifi ta danci tace masa ta koshi tana kokarin fitar da kwalla. A zuciya yayi
yana jinjina saurin kukanta Kamar wata 'yar goye Sam yaga kuka ba wani wahala yake
Mata ba, tana kuka tun abun kukan Bai Samu ba to idan ya samu yaya za'ayi kenan?.
Kwashe kayan yayi ya fita dasu Bai jima ba ya dawo da p.c.m tablet a hannunsa da
ruwa marar sanyi, farm fresh yogurt ya Fara zuba Mata ta karba Tasha sosai dan
tana sonta sosai lokacin tana Jos har kamfanin take zuwa ta sawo musu, tayi Mata
Dadi sosai sanyin moderate ba Mai cutarwa ba.
Saida ya tabbatar da tadan samu relief kafin yace Mata.
"Ki tashi ki canza kayan jikinki ki kwanta idan kikayi barci kan ze daina ciwon, in
Sha Allah, Kuma na fada Miki tun kina Asibiti ki rage damuwa Bata maganin komai sai
Karin matsala Amma idan Kika hakura komai Mai wucewa ne Zaki sameni fiye da yadda
Kika tsammmata kiyi hakuri komai da Kika gani hukuncin Allah ne ba Wanda ya Isa ya
canza idan Ina tunani akan kaina na duba yanda connection din ya faru nasa ba Wanda
ya Isa ya tsara haka sai Allah Dan haka ki Barbi abinda ya Baki Koda bakya so kinda
ance wani hanin ga Allah baiwa ne tunda gashi ya Baki Dan malami sukutum ai
tsakaninki da Allah sai godiya". Ya fada Yana kafeta da idanunsa masu sakata
ladabin dole.
Kai kawai ta gyada Masa, ba baka sai kunne, mikewa yayi da cup da robar farm fresh
din a hannunsa ya nufi kofa a hankali ya juya very lockly suka hada ido kashe Mata
ido daya yayi Yana Dan murmushi Wanda Batasan Kona menene ba, sannan yace Mata
"good night".
Yaja kofar wasu sabbin hawayene taji Kuma ita harga Allah bada niyya ba jinsu kawai
tayi hakika tana tausayin kanta, da gaskiyar masu iya magana da suke cewa cusa Kai
ba kwarjini yawa ne yau ta gani ganin idonta Wai ita Amarya ce wadda zayati kwanan
farko a gidan miji.
"Ya illahiy!!! Wannan wace irin ranace haka? Yanzu da Musba.... Astagafirullah".
Ta fada da sauri tasan tunanin wani irin haka haramun ne da aure a kanta.
Ta jima a gurin tana sakawa da kwancewa Amma dai duk inda ta juya amsar daya ce
aikin Gama ya riga ya gama sai hakuri da zubawa ikon Allah ido Dan shine alimil
gaibi.

Tunda Mahmud ya shiga nasa bedroom din ya kasa samun nutsuwa Banda yayi namijin
kokari ya kauda kansa da lallai sai ya rage zafi gaskiya idan yayi haka baimata
adalci ba. Dan shi a nasa bangaren kamai ya gama zamar Masa daidai, saidai ita uwar
gayyar batasan wainar da yake toyawa ba dan idan da abinda shi Kuma Bai lamunta ba
yayi Mata dole yafison komai Daren dadewa taso shi da muradin kanta yafi son ya
koyar da ita yanda zata soshi fiye da kowane da namiji data taba so a rayuwarta, ba
Kuma ya son tasan koshi waye bama ita ba kowa ma dake tare dashi a nan, yafi son ya
Gina kanshi a gurinta a wannan matsayin na yanzu.
Wanka yayi ya saka pyjamas dinsa farare sol nasu laushi, yana jinsa cikin watan
irin nutsuwa, maimakon ya kwanta sai ya dauko laptop dinsa ya dosa aiki sai gurin
biyu da kwata ya ture computer din ya tashi ya nufi kofa ya fita dakinta ya nufa
dakin zahrar yana zuwa yana turawa yaji kofar a bude Kuma dakin da haske yayi zaton
ko barci ne ya dauketa tabar wutar Mai haske a kunne. Yana turawa ya ganta akan
sallaya tayi sujuda Amma shashhshekar kuka take Allah kadai yasan abinda take roko
tsakaninta da mahalicci ya jima a tsaye kafin yaja Mata kofar ya fita jikinsa a
matukar sanyaye dan ba karamin qima ta kara a idonsa ba ya Kuma Kara godewa Allah
da yayi Masa kyauta da wannan yarinyar yasan Allah sami'uddu'ai ne yasha raba dare
Yana rokon Allah ya bashi mace ma'abociyar addini, sai gashi a inda Bai taba zato
ba Dan gaskiya Bai taba kallonta a wata mujahida ba yafi Mata zaton bokon ya
rinjayi bangaren islamar ta.
Koda ya koma shima Bai kwanta ba Saida yayi nafilfili sannan ya kwanta da tunani
kala-kala a zuciya.
Hudu da minti arba'in ya farka ka'idarsa kenan ta tashi sallar Asuba, wanka yayi ya
saka jallabiya milk colour ya bude kofa har ze wuce sai yaga Bai Dace ba gara ta
tasheta ta.
Sanda ya tura kofar har ta Fara raka'atanul fajri ta Riga ta tashi, lallai ya
jinnina Mata gurin ibada sai yaji ya qara samun wata nutsuwa a tare da ita da sauri
yaja Mata kofar ya nufi falon jin za'a tada sallah.l

✨✨
✨✨

🔷AUREN HUCE HAUSHI 🔷

✨✨
✨✨

MAMAN FATIMAH

💎 PAGE NINETEEN 💎 (19)

AssalamuAlaikum warahamatullahita'ala wabarakatuhu.


Ina mika sakon jaje gan Alummar maiduguri bisa ibtila'in daya samesu na karyewar
Alo dam, Allah ya jikan wadanda suka rigamu gidan gaskiya Wanda Kuma suke gida da
Asibiti Allah ya basu lafiya, abinda aka rasa na dukiya Allah mayar musu da ninkin
abinda suka rasa.
_______________Mahmud tunda aka idar da sallah Bai shigo gidan ba sai kusan karfe
shida da rabi, ya Dan jima da Mai gadi kafin ya shiga ciki dakin Zahra ya nufa a
kwance ya sameta akan sallaya da gani batasan lokacin da barci ya dauketaba yasan
kusan kwanan zaune tayi, a hankali ya matsa daf da ita Yana karewa fuskarta kallo
idanunta sun dan tasa alamun kukan da tasha da Kuma rashin barci, wayarta ce a
gabanta a kunne tsugunawa yayi ya dauka Qur'an ya gani tana karantawa barcin yayi
gaba da ita, baiyi tunanin tashin taba kada ya katse Mata barcinta.

Kan stool na madubi ya zauna da wayar a hannunsa Yana dubawa haka nan yaji Yana
son ya shiga ya duba received calls da missed calls nata, a hankali ya ringa bi
Yana dubawa yawanci kawayenta ne sai Kuma Ummee da ya gani har ze aje sai yaga
Kamar number din guyn da zata aura Dan lokacin daya tafi da wayarta ya canza mata
wayar da sim card din a Nan ya haddace number din tasa sai Kuma yanzu daya ga
Kiran jiya dai dai lokacin suka bar gurin Baba malam, Nan da Nan yaji ransa ya sosu
duk da Kiran daga gurinsa ne ba daga gareta ba.
Tashi yayi tsam yabar dakin da wayar a hannunsa shima kwanciyar yayi, can cikin
barci yaji alamun ana Danna door bell da kyar ya tashi ya nufi kofa, Musaddiq ne da
Faruq din Aunty Hasana suke kawo break fast cikin ladabi suka gaishe dashi ya amsa
yana Basu hanya suka shigo da basket din dake hannun Musaddiq ya Dora akan dining
table.
Musaddiq ne ya juya ya nufi kofa yayin da Faruq yayi tsaye, har Musaddiq yakai
kofar fita daga falon ya juyo Yana fadin "Faruq me kake jira ne ka tsaya? kasan
driver Yana jiranmu fa"..
"Taya zamu tafi bamu gaishe da Aunty Zahra ba?".
Mahmud ne yace "Faruq Auntyn barci take sai dai zuwa anjima sai ku dawo kaji".

***
Cikin damuwa da matsanancin tashin hankali Mama ta tashi, tunda garin Allah ya waye
ta tasa kayan da Hameeda ta shigo dasu jiya a leda da envelope din kudin da mijin
Zahra ya Basu a gaba ko bakasan kayan kwalliyar Mata ba kaga wadan Nan kasan ba
Karabiti bane ga uwa uba kudin daya lafta musu ita abin har ya Fara Bata tsoro, dan
a zahiri kowa yasan fakiri ne wanda Bai ajeba bai bada ajiya ba amma a badini
abubuwan da yakeyi suna da ban mamaki.
Wayar ta ta dauko tayi dealing din wata number ba'a Dade ba aka daga Bata koyi
sallama ba ta Fara magana "Asabe kome kike kizo anjima da matsala babba komai Yana
neman ya dagule fa kizo kiga abinda wancan tsintacciyar magen ya baiwa su Hameeda
jiya harda fadin magana dan Hameeda ta fadin maganganun danace ta fada wallahi Ina
kokonto akan lamarin yaron nan Dan jiya da dare Dana Kira malam na BANDE cewa yayi
Wai mun kuskure wani abu shi yasa har Alhajin ya iya daura mata auren Kuma yayi duk
iya yinsa ya kasa ganin komai akan mijin nata sai wani haske kawai yake gani".
Daga can taji magansr mamar ta amsa da "hakane ba damuwa sai kinzo din ta aje wayar
tana jan karamin tsaki ta tashi ta shiga toilet.

A bangaren Ammah kuwa bayan Sajida da zulai sun Gama aikin break fast din da aka
Kai gidan zahra, sajidar wanka tayi ta Shirya kafin ta fito falo su karya, bayan
sun Gama ne ta kalli Ammah tana fadin "Ammah in Sha Allah yau an tafi gida Ina son
na wuce school ne daman na jira ne saina raka Zahra gidanta tun last week muka Fara
lactures".
Ta fada a ladabce.

"To Babu laifi hakan Allah yayi Albarka, sai Magaji ko Malam Bala wani ya Kai ki
mun gode madallah, kunyi sallama da mutuniyar tun jiya kenan!" Ta tambaye ta.
Kai ta girgaiza tana fadar "A'a sai anjima zan shiga muyi sallamar".
___

Zahra Bata tashi ba sai wurin takwas da rabi tayi Mika gami da salati tana Kara
ware idanu tana kallon dakin da alama kamar ma ta manta inda take Sai a hankali ta
dawo cikin nutsuwarta "ya Salam".
Ta furta hankali tana ware sexy eyes dinta, wallahi Sam ta Manta da waifa a dakin
gidan aurenta take ba a dakin Ammah ba, tashi tayi zaune kan sallayar tana Kara
kallon Kanta har lokacin hijabin da tayi sallar ne a jikinta.
Toilet ta shiga duk jikinta ya Mata wani irin nauyi Sam Bata jin dadin jikin nata
ruwa Mai dumi ta hada ta shige ciki tayi kwance tana shakar kamshin turen wanka
data zuba ta jima sosai a cikin ruwan kafin tayi wanka ta fito sabon towel ta dauko
mai kalar purple Babba ta daura ta fito gurin mirror taje lotion ta dauko ta shafa
a jikinta, tashi tayi ta nufi gurin wata jaka kayan gyarab gashinta ta dauko, zuwa
tayi ta zubesu yanzu da a gida ne da Ammah ce zata gyara Mata tsab ta hade shi guri
daya, tana kiciniyar daureshi taji alamun bude kofa da sauri ta kalli gurin, Mahmud
ne cikin shigar kananan Kaya yayi wani irin fitinannan kyau, hannunsa ya nade a
kirji ya jingina da kofar ya zuba Mata idon dake figitata, shi be shigo ba shi be
koma ba ya kafeta da idanunsa.
Tunda suka hada ido dashi tayi saurin sunkuyar da Kanta jikinta na wata irin rawa
duk ji tayi ta rasa yanda zatayi daga ita sai towel din Nan a jikinta, gashin ta
saki ya bazu har gadon bayanta ta matse hannunta a kijinta, sun Kai kamar minti uku
a haka Yana Kare Mata kallo son ransa a cikin zuciyar sa Yana tsarkake sunayen
Allah da yayi Masa kyautar bazata da wannan kyakykyawar halittar dake gabansa a
matsayin matarsa ta sunna halaliyarsa wadda ba wani shamaki a tsakanin su.
Cikin takunsa Mai Cike da karsashi Amma a nutse, ya doso inda take tsaye Yana zuwa
ba zato ba tsammani taji ya saka hannu Yana tattaro gashin daya bazu a kafadarta
yana fadar "Bari na gyara Miki tunda Naga yana neman gagararki".
Bata iya ce Masa komai sai jikinta daya cigaba da tsuma, tsab ya hade ya saka ribom
din daya gani a kusa mayukan gashin brush comb ya saka ya Kara gyara shi sannan
yayi baya a hankali ya zauna akan sofa Yana fadar "ki shirya kizo muje ki bamu
break fast gashi can Ammah ta aiko tun wurin 7:30 su Musaddiq suka kawo".
Bata amsa ba Kuma ta dago kalle shi ba, d'an gunguni ta fara kasa kasa "kawai ka
zauna mun a daki kana kalleni kaki fita a gabanka kake son na saka kayan ko me?".
Yana kallonta gefen ido tana magana a ciki baya raba daya biyu yasan complain take
akan zamansa. Tashi yayi Yana fadin "idan kin Gama kiyi min magana Ina aiki ne".
Ya juya ya fice.
Wata ajiyar zuciya ta sauke tana fadar "innalillahi ni Fatima Naga ta kaina Wai shi
wannan waye shi? Nifa wallahi lamarinsa sun fara bani tsoro gaskiya" ta fada tana
cuno Baki, sai Kuma tayi sauri har towel din jikinta na neman faduwa key ta sawa
kofar, a gurguje ta saka doguwar rigar lace peach colour Mai touching din flowers
green Bata daura Dan kwalin kayan ba saita rufa gyale green,Sam batayi wani make up
ba powder kawai ta shafa sai lips glow turarenta ta fesa ta nufi kofa ta bude ta
fice tsaye tayi a cikin corridor din saita rasa a wane bedroom din yake.
Ta jima a tsaye tana saka yanda zata tunkari dakinsa Kai tsaye, cikin yin shahada
ta nufi inda take zaton nan ne bedroom din nasa a hankali ta murda handle din ta
tura kamar wadda za'a cewa ket ta ruga, wani sanyi da kamshin turensa Dana freshner
ya shiga hancinta dakin ba wadataccen haske duk curtains din windows a sake suke
can kan sofa ta hango shi da laptop a gefen sa yana ta faman daddanabawa tsaye tayi
ita Bata shiga ba ita Bata koma ba, yana kallonta ta gefen ido Amma sai ya basar
kamar bai ganta ba.
"Assalamu Alaikum".
Ta fada a darare, Bai kalleta ba Amma ya amsa sallamar.
Dan Jim tayi kafin tayi karfin halin cewa "na gama shiryawar".
Kansa ya dago ya kafeta da idanunsa da yake razanata dasu kafin yace "idan bazaki
shigo kije kawai an fada min Ina cinye mutane ne da Kika tsaye a nan".
Dan cuno Baki tayi ta saki handle din ta shigo a nutse Amma fa Babu nutsuwa Kota
sisin kwabo a zuciyarta ta ayyana "waya sani ko mayen ne tunda abune a duhu".
A tsakiyar dakin ta zauna an carpet Kanta na kallon tace Masa "barka da Asuba".
Shiru yayi kamar Bai jiba Saida ya Mula dan kansa yace "Lafiya ya kwanan bakunta I
hope ba wani damuwa ko?".
Kai ta gyada masa alamar eh.
Yace "good Bari na karasa wani dan aiki muje muyi break ko?"
Ya fada Yana kallonta.
Ganin tayi shiru yasa yaci gaba da aikinsa ita Kuma tana zaune duk sanyin dakinsa
ya Mata yawa, tana son sanyi amma sai taji na dakin yana neman ya sakata rawar
jiki.
Baifi minti biyar ba ya rufe laptop din ya Miki, gurin da take zaune ya nufo yana
zuwa ya Dan tsuguna kusa da ita Yana fadin "taso muje kada nabar 'yar amanata da
yunwa na amsa query a gurin su bestie ko?"
Ya fada Yana murmushi.
Hannunta ya kama ya dagota tsaye suna shakar numfashin juna Amma ita kanta yana
duban kasa, dayan Hannun yasa ya dago fuskarta as usual yanda ya saba.
Ajiyar zuciya ta sauke a hankali Amma bata rufe idon ba kamar yanda ya hanata a
jiya Bata manta ba amma ta kauda Kai gefe dan da gaske Bata iya had a ido dashi.
Dan kwanto da ita yayi jikinsa Yana juyo da fuskarta yana fadin.
"Wallahi kada ki rusa min budget dina kisa na kwashe kunyar nan daga idanunki tun
banyi niyya ba matukar zakici gaba da irin wannan dabi'ar".
Das das girjinta ya kara bugawa akan wadda yake, tana fadin "oh ni Zahra tawa ta
sameni shi Wai wane iri ne haka? sai yayi ta sakin magana ko kunya babu".
Saida ya matsa mata taci abincin kirki bayan sun Gama ne suka dawo parlor suka
zauna Sam Babu sabo ko kalilan a tsakaninsu kallo ya kunna a Nile sat ya kamo super
support suna kwallo live.
Ganin ita ba wani gane kan ball din take ba yasa ta Mike zata koma daki ta kira
Sajida taji ya maganar tafiyar Dan tun jiya da Abba yace a jiya zata tafi gidanta
sajidar tace itama sai gida ta.
Takunta biyu taji ya janyo ta ta fada jikinsa ba Shiri ta zaro ido waje hura kata
iskar bakinsa yayi a fuskarta dalilin yasa ta rufe idonta kenan a hankali yace
"Ina Zaki ki barni a zaune alhalin saboda na tayaki Zama yasa naki fita ko ina".
✨✨
✨✨

AUREN HUCE HAUSHI

✨✨
✨✨

💎 PAGE TWENTY 💎(20)

_______"ya Salam". Zahra ta fada a hankali jin yanda yake hura mata iskar bakinsa a
fuskarta, yasa hannuwansa duka biyun ya tallabo fuskarta yana kallon face din very
cute da ita, shifa baya gajiya da kallonta komai nata burgeshi yake yi Dan bakinta
ya kalli 'yan kyawawan lips din ta pink, gdy yake yiwa buwayi Gagara misali daya
mallaka masa ita a lokacin da bai taba zato ba, tunda ya kafeta da ido Bata yarda
sun hada ido ba, ba Kuma tayi gigin dogowa ba.
Qaran da door bell din tayi shiya kawo karshen 'yar tutsiyen da yayi Mata wani soft
kiss ya yiwa gefen wuyanta Wanda har Sai da ta zabura tana fadin "wayyo Allah!".
A shagwabe ta janye jikinta daga rikon da yayi mata, shi Kuma ya tashi ya nufi
kofa, Bata jira taga waye ba tayi wuf ta nufi ciki jikinta kamar mazari.
Tana shiga ta zube a gado tana fitar da numfashi da sauri da sauri kamar wadda
tasha gudu, jin alamun bude kofar yasa tayi saurin duba gurin Sajida ta gani tsaye
ta tsura Mata ido tana Mata wani kallo cikin mutukar tsantsar farin ciki zahrar ta
taso tana fadin "haba bestie kin wani tsareni da ido kina min kallon qurillah irin
wannan ko Kinga wani abu a jikina ne?".
Ta qarasa fada tana karasowa kusa da ita 'yar madaidaiciyar ledar hannunta tana
fadar "Wai meye Kika wani yi shiru kina kallona ne Dan Allah talk to me Mana pls".
Biyo bayan zahrar tayi har gefen gadon kafin ta samu kuzarin fadin "Bestie Kinganki
kuwa just one day Amma har kin Fara canzawa, Fadi min meye sirrin gaskiya, na tafi
jiya da zulumin ki a Raina yau kuma nazo na sameki haka kin wani Kara Zama fresh
dake".
"Bestie tsakanin mu harda 'yar zolaya zakice Wai na Kara zama fresh?"
Zama tayi gefen zahrar tana fadin "wallahi I am serious kin canza a idona gaskiya
Kinga ai dole na fada ko?".
"To shikenan kin fada bazan hanaki ba, wai da gasken yau Zaki wuce?"
Kai ta gyada Mana kafin tace "In Sha Allah meya rage kuma ai gara naje na fuskanci
karatun ko tunda na samu nutsuwa kin shigo gidan ki. Alhamdulillahi, ga sauran
abubuwanki na wajen Baffan rimi kici baga da amfani dasu dazuma munyi waya da safe
yace na bawa Ammah abinda ya Aiko dai ya Kara jardada Mata na a fada Miki kada wani
ya kawo Miki abu kici Kuma yace a tura a karbo Miki sako Nan da sati daya".
Dan langabar da Kai tayi tana Kara ganin kimar Sajida ta dauki matsalar nan tata
bada wasa ba.
Godiya sosai Zahra ta yiwa Sajida akan abinda suke mata, sun Dade sajidar na yiwa
Zahra nasiha akan ta rike aurenta da kyau ita bataga wani abun ashsha ba gurin
Mahmud idan. Nan da Nan idon Zahra ya kawo ruwa ta shiga sharewa da hannunta tana
fadar "wallahi bestie na rasa dalilin da yasa nake jin wani abu a tare dashi tun
ranar Dana Fara ganin shi naji abun ko kallonsa fa nayi sai naji gabana Yana faduwa
heart beat Dina Yana karuwa, kinsan ma inda matsalar take?"
Kai sajidar ta girgaiza tana fadar "sai kin fada".
"Kinsan haduwar mu ta farko rungumeni fa yayi a cikin jirjinsa tsam kamar.wata
baby amman Kamar an dinke min Baki na kasa ko fada Masa magana ne saima wani
azababben kwarjini da yayi min harda fadar na ringa kula kada nayi musu asara'.
Ai Sajida Bata San lokacin da wata dariya ta kubce Mata ba tana fadar.
"Babbar magana kice da wata tsumammiya a tsakani ku tun tuni har kika dauki
alhakina gurin hanani kwanciyar hankali tun jiya Allah barci ma ban samu na kirki
ba Ina zulumin abinda kaje yazo, Dan ba kowa bane za'a aje masa mace kamar ke ya
iya kauda Kai gaskiya"
Wani duba zahrar tayi Mata tana fadin "ban Gane ba me kike nufi da maganganunki?.

Wata dariyar tayi tana fadin "A'a ba mefa nake nufi kawai dai...... "
Sai tayi shiru.
Wani zancen ta dauko Tana fadin "Zahra ki tsaya ki nutsu a gidan aurenki ki gyale
kowa duk wanda ze raina Miki miji kada ki amince ko waye kuwa Koda ni da nake Miki
wannan maganar, Kuma game da Hameeda ki kula sosai Dan a jiya ta nuna Miki jiya ba
yau bace, jini kuma yafi ruwa kauri, Koda ta dawo tana neman Kara shiga jikin ki da
wata manufar tazo, Dan Allah kiba marada kunya duk yanda ake son ganin lapses dinki
kada ki bada damar hakan".
In Sha Allah zan kula nagode Bestie Allah yabar zumunci. Zahra ta fada
"Ameen" sajidar na ta fada, suna cikin hira akayi knocking din kofar ba'a bude ba
Zahra ce Mike tana fadin "ina zuwa, tana kokarin yafa gyale ta rufe gashinta Sajida
ta warce ta aje gefen ta tana fadin "haba ke kamar matar liman a daki na da Bata
ja ba tayi gaba saboda an Kara buga kofar, budewa tayi Mahmud ta gani Yana tsaye ya
canza kaya ya saka Riga da wando na wani yadi light brown dinkin buda yana baza
kanshi sa na ibada.
Matsawa tayi daga jikin kyauren ganin alamar shigowa zeyi Amma fa Saida yadan shafi
fuskarta kadan sannan ya ida ahigewa ciki, tsaye tayi tana binsa da ido tana ayyana
"Wai meye ne yake faman shafa mata fuska har a gaban mutane ko kunya bayaji tasan
wlh sarai Sajida ta gani sai dai ta basar kawai gashi ta wani rike mata gyale ta
wani barta tsurarta".
Direct gurin mirror ya nufa ya zauna a Kan stool, Yana fadin "Bestien mu zuwa
nayi muyi sallama naji Abdul Hakeem yana maganar Zaki wuce yau ko".
Ya fada Yana murmushi, itama murmushin tayi masa tana fadar.
",In Sha Allah yau sai kano tunda Allah ya cika min burina Zahra ta shigo gidanta
fine".
"To mun gode kwarai Allah ya saka da Alkhairi sai munzo visiting idan madam zata
dauki nauyin zuwan mu Kinga Nima sai Naga duniya ko madam?" Ya zubawa Zahra
narkakkun idanunsa Yana Mata wani kallon qasa qasa.
Shiru Zahra tayi tana yafa gyaren a kanta, Sajida ce tace "gaskiya Kam haka
za'ayi".
Tashi yayi ya Dan tako kadan zuwa gaban Zahra kamar ze hadeta da jikinsa da sauri
tayi baya tana turo Baki yi yayi kamar Bai gani ba, envelope ya Mika mata Yana
fadin ki Bata sskonta ne na jiya data Bari nayi niyya bazan canza ba sai dai idan
bataso ta bayar, nizan shiga gurin su malam".
A hankali tace "an gode madallah a dawo lfy".

"Amin to bestie sai munzo ko".


Bai jira abinda zata ce ba yayi ficewarsa.
Ajiyar zuciya Zahra ta sauke tana Zama kusa da Sajida Mika Mata envelope din tayi
tana fadin "yaushe ya Baki kikace bakya so?".

"Jiya Mana lokacin da zamu tafi sanda wannan jikar marokan ta zubar da darajarta ta
rokeshi, yanzu Dan Allah me Hameeda ke nema? wane irin rufin asiri ne Allah Bai
mata ba. Amma ta lalace gurin roko? shi yasa na aje masa kudin sa nayi gaba kayan
ma nace bana so su rike".
Dan murmushi Zahra tayi tana fadin "Saji danger wato halin na Nan ko? To nidai
gashi nan tunda a gaban ki ya bayar saiki karba".
"Bude mu gani to"
Sajidar ta fada.
Stalling founds ne na ingila musu yawa a ciki kallon kallo sukayiwa juna kafin
Sajida tace wallahi bestie akwai kukus a shinkafa zakice na fada Miki, Wai kuwa kin
tsaya kin Kare guyn nan kallo kuwa?". Kinga ya Miki Kama da Wanda baida abinyi ko
wanda ya tashi a cikin rashin wadataccen ilimi da mugu? Dubi muhallin daya ajeki,
ance malam ya bashi gidan sai kungiyar da yakewa aiki sukayi renovation din gidan
ki kiyasta nawa yaci gurin aikin kinsan da an kashe abinda yafi kudin ginin duk yi
Masa akayi? Ki tuna Nan fa ba garinsu bane ance bako ne kuma yaki fadin garinsu
anyi magana ance yace ya manta komai sai a hankali idan ya tuna hankali ze yarda da
hakan? Kuma kina tunanin Abba ze daukeki ya bashi ba tare da yasan wani Abu a tare
dashi ba? Kiyi nazarin abin Mana ni dai ina fada Miki kibi komai a hankali kuma
yanda na fashimci wani Abu a maganar da Kika fada min kinfa kamu da son guyn Nan
tun sanda kuka hadu ba tare da kin sani ba, Kuma Shima Naga yanda yake shige Miki
ko kunya ta Bai jiba kinsan sai a hankali kawai kwanan Nan labarin ze sauya irinsu
basayi da wasa fa".
Ta garasa fada tana dariya kasa-kasa.
Suna cikin tattaunawa Kira ya shigo wayar sajida "Ya Abdul Hakeem ne" ta fadawa
Zahra kafin ta daga.
"To"
Kawai tace ta kashe Kiran tana fadin.

"To bestie ya Abdul Hakeem Yana jirana Wai a she shine ze Kaini nifa daya fada na
dauka da Wasa yake lokacin da Ammah tace Magaji ko Malam Bala dureba zasu kaini sai
kawai yace su Bari Shima Yana son yaje kanon Sai ya tafi Dani".
Dariya Zahra tayi tana fadin "idan tayi wari munji batun, yanzu ba fa Naga Ya
Abdul Hakeem Yana dama dama dake ba bai fada min ba Amma zakice na fada Miki Ina ga
target dinsa kenan yau yake son ya yad'a manufarsa shi yasa yayi Riga malam
masallaci yace Wai daman kanon zaya".
Kin magana sajidar tayi sai murmushi kawai. Zahra tace "bestie ko dai komai ma ya
kankama ne ban sani ba Ina shirme?".
Kafin sajidar ta Bata amsa wani Kiran ya shigo da sauri ta dauki jakarta tana fadin
"To bestie sai gani na gaba Allah ya bada zaman lafiya ya kade fitina, sai anyi ta
hakuri kafin komai ya dai daita ki kwantar da hankalin ki zakiji dadin Zama dashi
in Sha Allah".
Har gate ta rakata babbar ledar dake hannunta ta Mika mata tana Mata addu'ar sauka
lfy. Amsa tayi tana Mata godiya ta bude gate din ta fita, ya Abdul Hakeem Zahra ta
gani a mota a zaune cikin mamaki tace.
"Ya Abdul Hakeem daman kana Nan waje Amma baka shigo ba?".
Fitowa yayi ya karaso gurinsu Zahrar ta gaishe shi, sannan ta juya ta koma ciki duk
zuciyarta ba Dadi Kamar ta Hana sajidar tafiya amma ba hali.

*********
Mahmud Yana fitowa direct Famfon shanu ya nufa tunda lifan din Habib a gurinsa ya
kwana, tun jiya daya karba da yamma Bai koma unguwar ba.
Lokacin daya karasa yayi arba da motar Sameer wani murmushi yayi Yana fadin.
"magulmaci kawai".
Kafin ya shiga Saida suka dinga gaisawa da jama'a anata Allah sanya Alkhairi, Binya
ya tambaya Ina Habib yace yaje Kai wani sako da malam ya tura shi ya Kai gidan
sarki.
Gurin Malam din ya shiga shi dasu Sameer ya samu suna magana da malam din Yana
shigowa da sallama mlm din yace.
"Yauwa Dan halak yanzu nake cewa bazaka jima ba zaka shigo, mutanen ku ne sukazo da
wasu ayyuka gasu nan dai zasuyi maka bayani. Ya wajen iyalin naka!?"

Dan sosa kansa yayi Yana Dan sadda shi qasa yace "Lafiya kalau tace a gaisheka" .
"Masha Allah. Allah yayi Albarka"
Gurin su Sameer ya juya suka gaisa, kafin suka fita zuwa inda suke meeting.
Stepdown training zasuyi da school base management committee Basu tunda tsarinsu ya
koma sun bin tsarin makarantun government ne sai kuma officially da suka gayyaci
Mahmud zuwa gurin taron da zasuyi a Lagos nan da kwanaki biyar masu zuwa. Bayan
Gama taron Sameer ya dauki Mahmud a mota suka fita hotel din suka nufa a hanya
Sameer ya kalli Mahmud Yana fadin "yallabai meye labari naga text dinka komai an
sawo zuwa anjima motar zata karaso amma sai nake ganin kamar kayi tafiyar nan da
ita tunda zaka jima a can Kuma kaga duka kwanan ta nawa zaka tafin baka ganin abin
ze iya Zama na surutu ko ace ma guduwa kayi amma dai ya kake gani?".
Dan Jim yayi kafin yace.
Tafiya da ita ba shine solution ba na dauketa na kaita Ina ko Kuma nace Mata wanene
ni Nan nace Lagos zani can Kuma taga sabanin hakan ya kake tunani ka tuna fa she's
educated, zatayi saurin gane komai ni kuma nafi son na Gina soyayya ta a zuciyarta
ba tare da tasan who I am ba, I hope you understand?".
Kai ya gyada Masa alamar eh.
Sun Dade suna tsaya yanda program din ze kasance da abinda za'a batar da abinda
za'a kashe a makarantar zuwa lokacin da zasu dawo suna cikin aikin direban daya
dauko kayan ya Kira Sameer ya fada Masa ya shigo Azaren ya fada Masa inda yake
tattara komai sukayi suka wuce gurin da direban yake, Sameer din ne ya shiga gaba
direban na binsa a baya har zuwa gidan Mahmud din.
Mai gadi ya taya direban sauke kayan, kayan abinci ne da sauran tarkacen girki
hatta nama da kifi daga can aka kawo kayane masu matukar yawa.
Ciki Mahmud din ya shiga tararwa ya yi tayi Baki har su zulai da sahura, a
tsaitsaye suka gaisa yayi gaba zuwa bedroom dinsa.
Ganin idon su zilan yasa zahra mikewa tabi bayansa dai dai lokacin Kuma Yara suka
Fara shigon kayan masarufin da aka kawo, ganin zahrar Bata Nan yasa su sahura shiga
dasu store din kayan abincin suka hada da wanda Abba yasa suka kawo dazu da kayan
gara su gireba dasu dublan da alkaki.
Sunyi mamakin yanda yara ke shigo da kayan abincin basu Kara Shan mamaki ba Saida
aka Fara shigo dasu Nama da kifi ga drinks Nan ko ba'a fada ba Wai ance ido ba mudu
ba amma yasan kima sun San kayan na manyan kudi ne, ko wacce da magana a bakinta
Amma bata furta ba.
Zahrar na shiga corridorn ta waske zuwa nata dakin.

✨✨
✨✨

AUREN HUCE HAUSHI

✨✨
✨✨

💎 PAGE TWENTY ONE 💎 (21)


...............…... Sai da su zulai suka gyara Mata komai yanda ya kamata sannan
suka gyara parlourn,lokacin da Mahmud ya fito bedroom dinta ya nufa baiyi wani
knocking ba ya tura kofar a gaban gado ya ganta ta cire bedsheet din ta zubo da
pillows din da alama wani Abu take nema sallama yayi mata cikin muryarsa Mai
nutsuwa yana kallon ta, cikin takunsa na cikakken namiji ya karaso Yana tambayarta
"lfy me kike nema ne haka Kika birkita gurin haka?".
Jiki sanyaye tace Masa "wayata nake nema tun safe banganta".
Dan matsowa yayi kamar ze tayata dubawar Yana fadin "Kuma tun safe Baki ganta ba
Kuma Baki nema ba sai yanzu, to su waye suka shigo dakin ne?".
"Shiru tayi kawai tunda tasan daga ita sai sajida ne a dakin Kuma tun bayan tafiyar
ta ko Baki ne 'yan ganin daki Bata ahigo dasu Nan Dan gani take yaushe za'a dinga
shigo da jama'a har dakin barcin mutum su dai dayan tunda ba a ciki take ba.
Dagowa tayi ta Dan kalli gefen shi da gani wanka yayi ya canza kananun Kaya tana
mamakin sa ita tunda take ganinsa Bata taba ganinsa da shiga irin wannan ba Kullum
manyan kaya ne Amma daga jiya zuwa yau ya zamar Mata wani daban, Sam ba wancen bane
take gani.
Kamar ze wuce ta bayanta sai Jin Hannun Mutum tayi ya zagayo ta cikinta ya manna
bayanta a kirjinsa ya kwanto da kansa dai dai saitin kunnenta iska yadan hura Mata
kadan tare da hucin numfashinsa kafin yace.
"Ki daina wahalar da kanki tana gurina tun safe na dauka, nayi mamakin da baki
nemeta ba sai yanzu? Na cire sim din saboda Naga wani sakarai ya kiraki da number
din to nasan ze iya bibiyarki tunda naga bashi da taushidi ko kankani Bai hakura ba
da hukuncin Allah so yake da karfi saiya kwato abinda ya kubce masa".
Kasa ko kwakwkwaran motsi tayi sanda yake jero Mata maganganun. Amma jin ya Kira
Musbahu da sakarai marar taushidi yasa taji Zuciyarta ta wani baci, idan beji
tausayinsa na abinda ya faru ba ai baze Masa bita da kullin irin wannan maganar ba,
shida ya tsunci dami a kala har ya samu bakin magana irin haka. Nan da Nan taji ta
samu wani courage wanda Bata San tana da shi ba, cikin muna bacin rai ta fara
kokowar raba jikinta da nasa tana fadin.
"Wallahi Musbahu ba sakarai bane, ba Kuma marar tauhidi bane,dan ya biyo abinda
yake halalinsa amma kasan dai Banda qaddara ba abinda ze rabani dashi, dashi muka
tsara planning na rayuwarmu Amma lokaci daya ka rusa Mana budget din mu ka yarda da
aurena da aka baka Kuma wallahi tunda nake dashi bai ko taba rike ko hannuna ba,
amma Kai kuwa fa ranar Dana fara ganinka a duniya dame ka Fara min bada rugumata
ba?" Kai kenan baka da aikin yi sai tabawa mutane jiki ......
Bata karasa fadar abinda tayi niyya ba taji ya hade bakinsa da nata cikin zafin
nama Yana ladabtar da bakin nata da harshensa, dayan hannun Kuma yayi Mata wani
irin riko bana Wasa ba dayan Kuma yana yawo dashi a ilahirin jikinta cikin wani
irin sarrafawa Mai zafi.
Wata irin tsuma jikinta ya kama ga hawaye kamar na lalataccen famfo sai zuba suke
ba bakin kuka sai mutsu mutsu take Amma ko a jikinsa wajen sau uku ana Kiran
wayarsa tana tsinkewa, yayi biris da Kiran Kumar baya ji, sai da ya tabbatar da ya
ladabtar da ita yanda yake so ya saketa, kan bed ta fada tana shashhshekar kuka
hannunta daya yana Kan lebenta dake Mata zafi haka ma kirjinta zafi yake Mata ga
gaban rigar ya farke Mata ita.

Kafarsa daya ya doro Kan gadon dayar tana kasa ya Fara fadar maganarsa hankali
kwance kamar bashi bane ya Gama yamutsa Mata jam'iyya yanzu ba cikin mugunta.
"Wallahi na Kara Jin wannan sunan a bakinki ko magana makamanciyar irinta saina
shayar dake ruwan mamakina, an fada Miki ni lusari ne da har Zaki tasani gaba kina
fada min rubbish ne? an rusa muku budget din sai kuyi duk abinda zakuyi, an fada
Miki Nima son abin nakeyi ne? da har Zaki tsaya kina min rashin kunya akan wannan
lusarin Mai karairaya kamar mace,ke yanzu wannan har wani namijin arziki ne da ze
iya dake? wallahi da kinyi tsautsayin aurensa da kin Gane Baki da wayo, idan Kika
Kara gigin fada min magana makamanciyar irinta zan Baki mamaki wallahi, , har kike
wani zakewa kina fadawa mutane magana, kice tak akansa billahil Azeem sai kin Raina
kanki a dakin Nan saina banbance Miki tsakanin namiji da muna maza".
Yayi tsaki ya juya abinsa cikin takunsa na ingarman namiji ya fice daga dakin
zuciyarsa kamar zatayi bombing.
A yanda su zulai sukaga ya fito Saida abin ya Basu tsoro kallon kallo suka shiga
yiwa juna, sahura ce tace.
"Zulai bakiga yanda Mai gidan nan ya fito bane? Allah yasa ba mutuniyar taki bace
ta taboshi Kinga ai ba haka ya shiga ba".
Zama zilan tayi tana fadin "waya sani sahura muna Nan tare dake, nifa shi yasa nace
ba zanzo ba yau amman Ammah ta matsa akan sai nazo na Gane mata lafiyar ta,tun
safe wayarta idan an Kira Bata shiga".
"To Kinga kuwa dole ki dubota ki gani ko Lafiya ya fito a haka kofa a dawo lfyr mu
bai amsa Mana ba".
Jiki ba kwari zulai ta nufi bedroom din Zahra ganin zilan ta shige cikin corridor
sahura ta Ciro wayarta Nokia ta Kira Mama. Ba bata lokaci ta dauka kamar jira
takeyi ta shiga labarta mata abinda ta gani tun daga kan kayan da suka Zuba store
har fitowar Mai gidan yayi da alamun bacin Rai a tare dashi, to kawai sahurar ke
fada alamun wani Abu mamar take fad'a Mata sannan sukayi sallama.
Sai da ya fice harabar gidan ya Ciro wayar daga aljihun wandonsa ganin Sameer ne
yasa ya Maida wayar ya nufi inda Sameer din yake zaune cikin mota, Bai Masa magana
ba, zagaya yayi ya shiga motar yana fadin "let's go"
Ganin yanayin daya fito ya hana Sameer din korafin barinsa a waje baice ya shigo
ba, dan kwantar da kujera Mahmud din yayi ya kwanta yasa hannu ya dafe kansa da
gaske Sara Masa yakeyi lokaci lokaci Yana Dan Jan tsaki, Sameer dai be tanka Masa
ba yasan a kusa yake, sai da sukayi nisa da gidan Sameer din ya Dan juyo yana
tambayar.
"Ina muka nufa yanzu nifa na gaji ga yunwa Ina ji kace muzo gida muci abinci Kuma
ka watsar dani a mota inaga ma sai da ka rage zafi ni in Nan Ina hamma ka
shanyani".
Ya fada Yana Maida hankalinsa a titi.
Tsakin ya Kara yi Yana dagowa daga kishingidar da yayi Yana duban Sameer din "Allah
ya shiryeka ka dauka kowa ma irinka ne Wanda baya iya kauda Kai a Kan Mata? Muje
can hotel din kayi order abinci kaci tunda bani na gayyato ka ba cewa nayi ka
dorowa mota kayan Kai Kuma sai gurin jibi kazo, to bansan wane kinibibin ya kawo ka
ba ka bar yarinyar mutane da ciki kana gantali".
Ya karasa maganar Yana hararar Sameer din.
Dariya yayi Yana "fad'in easy man bani na kar zomon ba rataya aka bani, waya fada
maka lamarin su da sauki? bakaji abinda Abbanta ya fada maka ba? ai da yace sai
ana hakurin da gaske ne Zama dasu Saida hakuri".
Wani sakaran kallo Mahmud din ya aikawa Sameer da shi.
"Ka wani zaqe kana ta zuba wani Abu nace maka tayi min ne? da kaketa faman fadin
maganganu haka tsabar saka ido kawai, gobe ka tattara ka koma inda ka fito tunda
ba gayyato ka nayi ba da zaka dameni da kananun maganganu zan shigo da kaina kanon
ba ai ba bakuwa ta bace ba".
Ya fad'a da gaske Yana Bata rai.
Shiru Sameer din yayi ganin da gasken koma Nene yayi touching dinsa sosai.
Suna shiga harabar hotel din kafin Sameer ya Gama parking a parking lot Mahmud ya
bude ya fice abinsa Yana picking din wayarsa da aka Kira.

******Tunda zulai ta doshi kofar bedroom din Zahra take jiyo Kamar shashhshekar
kuka, hannunta har rawa yake gurin bude kofar Dan ba maganar knocking, rubda ciki
ta sameta tana faman shashhshekar da sauri ta mayar da kofar ta rufe ta karasa
gurin zahrar da sauri tana Fadin.
"Subhanallahi uwar dakina me zan gani haka me kikayi masa? Dukanki yayi? Dan Allah
kiyi magana Kona Kira Aunty Hasana ne sai ki fad'a mata ko na Kira Miki Ammah".
Kai ta girgaiza mata alamun a'a, "to ki fad'a min ko zan iya yi Miki wani abun
Mana".
Saida kukan ya lafa Mata sannan ta yunkura ta tashi zaune ido zulai ta zuba Mata
ita ba yarinya bace kallo daya tayi Mata tasan da wata a kasa ganin yanda take a
yamutsa ga labbanta sunyi jajir abinka ga farin Mutum ga gashin kanta duk gyaran ya
turje. Zama tayi kusa da ita sai a lokacin taga gaban rigarta a yage Hannun bra
dinta guda a tsinke.
Kai kawai zulai ta dafa tana Fadin "mezan gani haka ni zulaihatu! Haba Zahra'u me
yayi zafi haka ai sai kisa ya illataki a banza, gardama kika yi Masa yayi Miki
haka?"
Cikin shashhshekar kuka tace "A'a maganar Musbahu yake min shine ya Fadi Abu marar
Dadi a kansa shine kawai Dan na mayar Masa da amsa Nima yayi min haka". Ta karasa
fad'a tana kuka.

Kasake zilai tayi tana duban zahrar kafin tace


"Haba Zahra'u da wayonki da hankalin ki Zaki rinka irin wannan abun har yaushe Zaki
ringa maganar wani namiji a gaban mijinki har kiyi ikirarin fad'a Masa magana marar
Dadi akan shi ai yayi Miki kadan wallahi idan wani ne yau basai gobe ba saiyayi
Miki kaca-kaca yanda ko sunansa ba Zaki Kara fad'a a gabansa ba, kada ki kuskura ki
Kara irin haka Zaki ragewa kanki kima da daraja a idonsa, duka yaushe akayi daren
da shashshawa zata Bata,Ina cewa jiya aka kawo ki amma ace an Fara da haka kinga
abin baiyi kyau ba ko kadan, yanzu ki tashi ki shiga kiyi wanka da ruwan dumi zanje
na cewa sahura kina wanka ne, mu tafi kawai tunda nasan halinta Abu kadan zata fara
yaya tashi tunda nasan badan Allah ta biyoni ba dan Saida na fito harabar gidan ta
biyoni.
Sallam zulan tayi Mata Tana Kara tausarta akan ta ringa tauna irin maganar da zata
ringa fada masa.

Cikin karfin Hali ta Mike ta nufi toilet da gaske ya tsumama mata jiki ta jima a
toilet din tana kuka maganganunsa sun Mata ciwo matuka har wani gori yake Mata
Shima ba sonta yake ba, to an fada masa ita son nasa take har yake wani Mata
wulakanci, ita ta rasa a Ina ta kuskuro ne take haduwa da fitintinu daga wannan sai
wancan? "Astagafirullah".
Ta fada a zuciyarta, alwala ta dauro ta fito ba wani kwalliyar azo a gani tayi ba
duk ranta a cunkushe ga 'yar wayar da zata debe mata kewa ma ya dauke, a ranta tace
"mugu kawai wani sumumu kasam dashi Kamar na Allah Nan kuwa dan duniya ne Mai
lasisi".
Tana cikin saka kaya taji karan bell alamun Baki a gurguje ta ida yafe gyalen rigar
ta dan fesa turare tayi gaba.

*****
Sai Bayan sallar magriba su zilai suka karasa gida dai dai lokacin Magaji ya fito
da manya warmers a hannunsa sai Autan Ammah da basket a hannunsa Shima, zasu kaiwa
zahra abincin dare.
Suna shiga zilai ta wuce part din Ammah ta fada Mata sun dawo ita Kuma sahura ta
nufi nasu bangaren sai da zulan ta shige part din sannan sahura tayi wuf ta shige
sashen Mama.
Salma kawai ta samu a falon tana kallon series na India ko arzikin amsa sallamar
sahurar Bata samu ba sai wani kallon banza tayi mata tana Fadin "lafiya Kika wani
shigo afujajun haka?".
Kafin sahura ta samu zarafin Bata amsa Mama ta fito daga bedroom din ta tana Fadin
Kamar maganar sahura nakeji?"
Cikin azarbabi tace "nice Mama mun dawo".
Ta fada tana Zama a kasa kan carpet.
Cikin kwarewa da munafurci ta shiga korawa mamar bayanin abinda ta gani harta Kara
da cewa.
"Anya Mama yaron Nan kuwa Babu abinda yake boyewa kin ganshi kuwa? Gaskiya wallahi
baiyi kama da fakiri Mai neman abincin yau da gobe ba, kayan abincin da muka zuba a
store din wallahi ni wani abin ma ban taba gani ba hatta madara wannan manyan
gwangwwnaye sunfi ashirin Nama kuwa na kaji kawai sun Kai hamsin Banda na rago
Banda na shanu Banda kifi Allah Mama Saida muka cika freezer din cikin kitchen din
ga lemuka da ruwa Kamar banza ga......
Bata Bari ta garasa ba ta daga mata hannu "bar shi kawai jeki zan nemeki".
Mikewa tayi tana Fadin "a huta lafiya Bari naje nayi sallah naji ana Kiran
insha'i". Ta fice.
Tunda ta fita Mama ke jijjiga Kai tana kwafa, Sam hankalin salma na can gurin
kallon ta Bata damu da abinda su mamar suke ba, Saida mamar ta Kira sunanta sannan
hankalinta ya dawo Kan mamar tasowa bayi ta dawo kusa da ita tana fadin.
"Mana menene Naga kamar ranki a bace,?".
Tsaki tayi tana fadin.
"Anya Abbanku da Asma'u ba ninkeni sukayi a baibai ba kan auren yarinyar Nan? ni
daman tunda naga daga b'angaren Asma'u da 'ya'yan ta da 'yan uwa ba wata turjiya
nasan da abinda suka taka bakiji labarin da sahura tazo min Rashi ba?".
Kai salmar ta girgaiza alamar bataji ba, Nan Mamar ta shiga fad'a mata abinda
sahurar ta fada Mata, Nan da Nan hankalin salma ya tashi ta shiga fadar "ai
laifinki ne Mama Nan nazo na fada Miki naga wani inaso a gurin Baba Malam Kika
dinga zagina duk yanda naso ki fashimceni shi ba irin wanda kike tunani bane ni
naga abinda na gani Amma Kika shafawa idanunki toka kikaki saurarena ai gashi nan
duk fafutukar ki ta tashi a banza ko yanda kika fada min gidan yake ai kinsan da
wata a kasa".
Ta fad'a tana share hawaye, Nan da nan hankalin Mamar ya Kara tashi idanunta sukayi
jajur, cikin kaushin murya ta Fara fadar.
"Ni za'a yiwa haka wallahi sai dai kowa ya rasa Dan wannan auren sunansa matacce
dole ya saketa ko baya kaunar Allah ai indai Ina raye yarinyar Nan sai dai kyanta
ya Kare a banza ba dai tayi aure inda zata huta ba ita da hutu sai dai tayi nata
gaji da aiki, duk wani haske na rayuwarta saina dusashe shi Bari ma ki gani".
Ta yunkura ta Miki ta nufi bed room dinta tana lalubar wayarta.
Ayi hakuri ba editing Naga kwanaki wata na fadar kada a karanta rubutun ba kyau.



AUREN HUCE HAUSHI



Story
&
Written
By

Maman Fatimah.

Godiya da yabo sun tabbata ga Allah s.w.a, salati da daukaka da Amincin su tabbata
ga shugaban mu Annabi MUHAMMAD s.a.w.w.

Page twenty two. ( 22)

________Mahmud Bai bar cikin hotel din ba Saida yayi sallar insha'i, cikin gari ya
koma gurin malam lokacin sun Fara karatun dare da maza manya Kamar Yanda suka Saba,
shima littafin ya dauko na Riyadussalihinp ya zauna daukar karatun sai gurin
takwas, bayan jama'ar sun watse ya rage daga malam din sai Mahmud da Habib.
Ganin Mahmud din ya zauna malam yasan da magana, Saida Habib ya gama gyara
littatafan kusan aikinsa ne shida Abubakar, bayan fitar Habib din kusa da malam
din Mahmud ya matso Yana Fadin Baba barka da dare".
Cikin sakin fuska malam ya amsa Masa Yana Fadin.
"Ya akayi ka zauna har wannan lokacin baka koma ba kasan ba sabawa tayu ba itama ya
kamata a ringa kula". Kai yadan Sosa Yana Fadin in Sha Allah yanzu zan tafi daman
na tsaya ne Ina son muyi magana".
"To Babu laifi ina saurarenka".
Qara sadda Kansa yayi Yana Fadin.
"Daman game da maganar tafiyar da zamuyi ne nace ko za'a samu wadda zata zauna da
yarinyar Nan ne?".
Gyaran murya malam din yayi kafin yace

"Eh hakan yayi dai dai saidai ka tuntubeta kaji nata ra'ayin tunda Naga gidan nasu
da wadatar juma'a ko wata zata tayata zaman tunda kasan sha'anin yau sai a hankali
kada a Kai Mata wadda za'a samu matsala".
Tunda baba malam ya fara Kora bayani Mahmud ke gyada Kai sai da ya Kai Aya sannan
Mahmud din yace. "haka ne in Sha Allah zan nemi shawarar tata duk yanda mukayi zan
fad'a maka, na gode" Ya fada kafin su fad'a wata hirar akan wani sabon project da
suka samu daga usaid karshi gwamnatin jihar Bauchi da sukazo musu aikin plane na
shekara bakwai. Bashi ya bar gurin malam ba sai wurin Tara da rabi, daya fito ma
majalissar su ya nufa gurin su salisu Nan suka dunga yi masa chari akan ya zagaye
ya tafi gidansa bai nemi rakiyar kowa ba ko rowar ganin Amarya yake musu, shi kuma
ya Kare kansa da hujjar Shima be San da zuwenta ba kawai da yamma Baba malam yace
yaje can gidan ya jira Alhaji Jafar Yana son ganinsa, Yana zuwa kuma ya ganshi da
zahrar ya kawota da kansa, to wa zaya Kira Kuma ihu bayan hari.
Sunyi masa Allah Sanya Alkhairi da Alkawarin zuwa su gaida amarya sai goma ya karbi
lifan din Habib ya nufi hayin banki.

Lokacin daya shiga falon shiru ba motsin komai sai ni'imtaccen kamshin turarukan
wuta 'yan asali da kuma na roomfreshner masu dadin kamshi lumshe ido yayi Yana
shakar kamshin.Nan da Nan yaji wata irin kasala ta rufe shi ga wani mahaukacin
feeling yana bijiro masa tun bayan barinsa gidan yake fama da wani irin tunanin ta
duk motsin da zeyi sai ta fado Masa,moment din yake tunawa duk da ba cikin dadin
Rai yayi ba Amma ya tsaya Masa a zuciya sosai Kamar magnet haka ya d'afe Masa.
A hankali ya taka zuwa tsakiyar falon komai tsab Kamar wani mahaluki Bai shiga
falon ba, harya Fara Hawa steps din da zasu sada shi da bedrooms nasu hankalin sa
ya Kai wurin dining din manyan warmers ya gani a hankali ya sauko ya nufi gurin
abinci ne mai rai da lafiya sai Kuma pepper soup na cow tail da hadin salad da
alama na ba'a taba ba yasan aikin Ammarta ne kada kai yayi Yana fadin "wato
abincin ne bazataci ba ko me take nufi? baiwar Allah ta Bata lokacinta ta bada a
kawo Amma ba za'aci ba"
Dakinta ya nufa Yana zuwa ya kama handle din yaji ta a rufe, shiru yayi wata
zuciyar na cewa yayi knocking wata Kuma na kwabarsa, juyawa yayi ya koma gurin
dining din shi dai baze iya cin abinci Mai nauyi ba, abincin ya dauka yabar pepper
soup da hadin salad din tinda bashi da yawa.
Gurin Mai gadi ya nufa yana Fadin "Ga abincin nan a samu ayi amfani dashi yayi
yawa".
Da hanzari ya taso Yana fadin "To yallabai ai dazu ma Mai gidan ta Aiko dashi har
Saida na bawa wasu Yara ma sauran, wannan kuma Bari na kira Mustapha yazo ya kai
musu can gida madallah dai an gode da dawainya".
"Haba ba komai gashi idan yazo sai ya biya mashin dasu". Ya aje Masa 5k akan warmer
din ya juya yabar Mai gadin Yana sheka Masa addu'a da fatan Alkhairi.
Saida yayi wanka sannan ya dawo dining din yaci iya Yanda yake ganin ya isheshi
sauran ya Kara kaiwa Mai gadin sannan ya koma daki.
Kan kujerar desktop computer ya zauna Yana kunnawa da ita akayi masa connecting din
CCTV din dake gidan, a hankali ya fara watching Yana kallon duk wani abinda ya
faru a gidan wani irin murmushi yakeyi lokacin daya ke kallon dabin su da ita da
yadda tasha kukanta, wani Abu daya ja hankalinsa shine yadda yaga su zilai da yadda
yaga sahura tayiwa zilai dabara ta turata ciki gurin zahra, ita Kuma tana waya
bayan ta gama Kuma yaga ta shiga store ta fito tana kudundune Abu a cikin hijabinta
wanda be San ko menene ba, take a Nan ya Dora mata question mark.
Saida ya Gama ganin komai Dan yanzu ma littafi ne take karantawa har lokacin daya
murda handle din kofar da Yanda ta wani zaro sexy eyes din ta Kamar zasu Fado kasa
saboda razana, murmushi yayi Yana fadin "matsoraciya kawai wannan za'a Sha drama da
ita Dan Naga alama shagwaba tabi jikinta Bata San wahala".

Zahra kuwa tunda ta shige ta rufe kofarta tayi duk abinda zatayi na al'adun
kwanciyar ta, sai ta dauko littafin ta du'aul mustajaba tana karanta addu'ar barci,
bayan ta Gama ta shafa shiru kawai tayi tana tunane tunanen zuci ba, memories na
abinda ya faru tsakanin ta da Mahmud ya shiga dawo Mata, Dan guntun tsaki tayi tasa
hannu a kirjinta data wuni suna Mata zugi, a hankali ta Fara magana Kamar Mai gudun
kada wani yaji ta.
"Jarababbe kamar maye duk ya cinye min labba da harshe ya shafeni tas yana wani
gurnani kamar na zaki, da wasu idanunsa da gani na fitinannu ne! Ni Zahra na gamu
da gamona na shiga Tara bama uku ba, shikenan na Zama nama sai Yanda hali yayi".
Hawaye ne sharrr suka zubo Mata duk lamarin ya cud'e Mata ta rasa mafita, alwala ta
shige ta dauro tana ayyana gara ta kaiwa Wanda baya barci wani abu Kuma Bai taba
boyuwa ba a gurinsa kukanta tasan shine sami'uddu'a.
Sallah tayi raka'a hudu ta zauna tayi istigifari da hailala da salati ga fiyayyan
halitta Annabin Rahama Muhammad s.a.w.w har Saida taji zuciyarta ta samu nutsuwa
kafin daga karshen ta daga hannuwanta sama tana Fadi cikin raunin murya da
Qasqantar da Kai ga Allah s.w.a
"Ya Ubangiji Kaine mafi sani ga abinda yake faruwa Dani, wani Abu Bai sameni ba sai
da izininka na gode maka a duk halin dana samu kaina a ciki, ka zama gata na,ka
lullubeni da bargon Rahamarka, ka suturtani da suturarka, ka rufa min asiri da
rufin asirinka, kada ka barni da iyawata ka iya min da iyawarka, Ubangijina ga
wannan bawan naka Nan kasan ko waye shi lamarinsa Ubangiji ka sani ba boyayye bane
a gurina Idan Yana da wani kaidi kada ka Bari yayi tasiri a kaina Dan isar Annabi
MUHAMMAD a gurinka. Ubangiji kajikaina ka duba raunina ka tausaya min kada ka Bari
makiya suga wallena ka bani rinjaye a kan dukkan al'amurana".
Duka hannuwanta tasa ta rufe fuskarta kamar me shafa addu'a Amma kuka ta saki Mai
tsuma zuciya tana ayyana "Wai fa ita Amarya ce wadda ya kamata ace a irin wannan
time din ana can ana riritata kamar a hadiyeta dan so da kauna da tarairaya da
kulawa. Amman nata da haka yazo Mata, Astagafirullah Ubangiji ka yafe min zunubina
daya janyo min irin wannan gararin rayuwar".
Ta dauki dogon lokaci tana shashhsheka a haka barci yaci karfinta ta sulale a gurin
yayi awon Gaga da ita.

Bata farka ba sai kusan biyar da rabi cikin sauri ta tashi tana fadin
"subahanallahi!"
Da sauri ta nufi toilet tana addu'ar tashi daga barci, a gurguje tayi uzurinta tayi
alwala ta fito sallah tayi ta zauna yin Azkar da karatun qur'ani har gurin takwas
na safe.
Mahmud Bai dawo gida ba daga sallar asuba gurin Sameer ya wuce, so yake yi suyi duk
abinda ya kamata a Nan tunda kwaso jiki ya taho, shi yasa jiya yaqi yin komai yayi
kwanciyarsa kawai.
Ba karamin mamaki Sameer yayi ba ganinsa da yayi a irin wannan lokacin to ai ko
lokacin da taye single baya Masa sakko haka. Amma sai gashi shida yake expecting
dinsa gurin one-two haka shine ya ganshi haka kamar an koroshi.
Cikin zolaya yace "My man ya naga haka ka duba time kuwa? Ka fito kabar 'yar
mutane ko dai da matsala ne na fadawa Babanka manya su shiga ciki, sun baka yarinya
girma -girma kana neman ka bada musu yaji a ido duk Wanda ya ganka a irin wannan
lokacin daya Kamata ace kana can kana Shan kafi tea, ai sai mutane su dauka fanko
aka kawo maka, gaskiya ka yiwa Allah ka koma ni zan shigo mu karasa aikin a gidanka
daman meke kawo mu Nan? ba bukatar privacy ba? to yanzu muna dashi kaga no need sai
munzo Nan Kuma kasan yanzu ba da bane ".
Ya fada ba alamar zolayar yanzu, ikon Allah Mahmud ya tsaya yana kallo kafin yace
"ka Gama Alhaji muhammadu tunda Naga alamar roll din tsohona kake playing, to Wai
Ina ruwanka da harkar Nan Ina cewa Mata dai tawa ce yanda nayi ra'ayi haka zan
tafiyar da abina, ai dalilin daya kawoni kenan kazo mu ida duk Wani aikin da zamuyi
kaje kayi sallama da malam ka kama gabanka".
Ya zauna Yana dauko laptop din Sameer Yana operatin dinta.
Kusa dashi Sameer din ya zauna Yana fadin "Allah ya huci zuciyarka angon Zahra da
Safnah....." wani kallo Mahmud ya watsa Masa wanda yasa Sameer yayi shiru ba
Shiri, shi kansa baisan sanda bakinsa ya furta sunan safna ba ko alama.✨✨
✨✨
AUREN HUCE HAUSHI

✨✨
✨✨

Story
&
Written by

Maman Fatimah.

💎 Page twenty three 💎 (2 3)

________Zahra ba ita ta farka b sai gurin bakwai da rabi, sai lokacin ta tuna ta
cewa Musaddiq ya fadawa Ammah ta bar kawo abinci zata dafa tunda ba komai take ba,
toilet ta fad'a ta Dan sakarwa kanta ruwa Bata jima ba ta fito Riga da Wanda na
Pakistan ta saka tayi rolling da gyalen ta saka plat shoes na daki ta nufi falo
Amma zuciyar ta tana ta dar- dar kada suyi arangama da Dodon nata, falon ta shigo
shiru sai sanyin A/C da daddad'an kamshin da yake ga curtains din duk a sake ga
fitilu masu qarancin haske a kunne saiya bada wani irin yanayi Mai saka nutsuwa.
Dan waige-waige ta Fara Kamar tana neman wani Abu gurin sai Kuma ta nufi gurin tv
ta tsuguna tana hada socket din adapter din tv ta kunna ta kamo tashar Almajid,
kokacin sun saka Qira'ar Muhammad Saddiqul minshawi a cikin suratul ISRA'I sai da
ta dai daita volume din sannan ta nufi kitchen din a nutse da takunta Wanda da yawa
suke ganin yangace da jiji da Kai alhalin ba haka bane naturally haka Allah yayi
ta.
Kitchen din ta shiga Kusan shigowarta ta uku Kennan, lokar da taga kayayyakin aikin
ta bude ta dauko roba mai Dan Fadi ta nufi store ta debo Irish ta fito wanke shi
tayi ta fere ta zuba a tukunya ta kunna gas, sai kuma ta dauko kaza guda ta yanka
ta wanke ta zuba seasoning da spices ta rufe, ta jona egg boiler ta zuba kwai hudu
a ciki.
A gefe kuma ta dauko attarugu da Albasa ta yanka kananu ta aje a gefe Irish din ta
Fara dubawa taga yayi ta sauke ta zuba a container Mai zurfi tasa fork ta murje ta
dora frying pan ta zuba Mai kadan ta saya attarugu da albasar ta zuba a Kan irish
din ta zuba magi da curry ta fasa ta yanka dafaffen kwan a ciki sannan ta fasa
danye ta zuga ta juya ta aje ta duba kazar itama tayi Nan da Nan ta hada pepper
chicken sannan ta jona tanda electric ta Fara zuba hadin Irish din Nan tana soyawa
Kamar masa, tana gamawa tayi pepper chicken. Dora ruwa tayi a karamar tunya kafin
ya tafasa ta dauko madara ta bude ta diba a wani bowl ta dama sannan ta dama corn
flour a cup, jikin kitchen cabinets din ta tsaya tana bin karatun da yake shigowa
daga parlour har sun kai suratul D'AHA.
Madarar ta zuba taci gaba da tafasa sannan ta zuba corn flour din ta daure da yayi
dai dai yanda takeso ta sauke ta Kara Masa condensed milk a cikin ta juye, hadesu
tayi a babban tray tayi ta nufi falon, Nan akan dining table ta jero komai sannan
ta koma ta dauko sauran tarkacen su cups.
Kitchen din ta koma ta gyara gurin tas, sannan ta koma daki wanka ta shiga, tana
fitowa ta shafa lotion dinta tayi simple makeup ta saka saka turarikanta na jiki
dasu humra Nan da Nan jikinta ya shiga fitar da wani fitinan Nan kanshi, doguwar
rigar Dubai Mai kananun stones pink mai duhu ta saka rolling tayi dan Vail din
rigar milk colour sai ta fito balarabiyarta sak Dan idan ba kaji tayi maka Hausa ba
bazaka taba cewa tasan ko zo da Hausa ba, tayi kyau matuka yarintarta ta fito sosai
idan ka kalli fuskarta very cute sai wani annuri take fitarwa.
Parlour ta fito gurin dining din ta nufa cikin takunta das das. Tana mamakin Ina
ya shiga Dan ko motsinsa babu har yanzu ita kuma bazataje bedroom dinsa ba, idan ya
gaji da zaman dakin ya tunda ba yaro bane yunwar cikinsa ta fito dashi. Kunun
madarar ta zuba da masar Irish din kwara biyu kawai ta dawo main parlourn ta zauna
tana ci tana sauraren karatun, sai da ta gama ta Kai kayan kitchen ta wanke sannan
ta dauko Wanda ta zubawa baba Mai gadi ta nufi kofa a hankali take tafiya a cikin
harabar gidan iskar bishiyoyin da sauran shuke shuken suna kadawa gwanin sanyi can
gurin gate taga baba Mai gadin ya nufa da sauri da alama budewa zeyi.Dan tsayawa
tayi daga gefe idonta Yana kan gate din Dan taji dirin mota zata shigo cikin
kankanin lokaci motar ta shigo ido cikin ido sukayi da shi shine yake driving din
gabanta ne ya bada ras ras Kuma ya kafeta da fitinannun idanunsa cikin gwaninta ya
nufi parking lot, Sameer kuwa Kamar wani sakarai haka yake kallon zahrar Yana
tsarkake suna Allah a zuciyarsa ya ganta har kusan hudu Amma da alama ganin tsoro
yake Mata sai yau yaga zahirin zahrar, da sauri baba Mai gadin ya karaso yana
gaisheta ta Mika Masa Dan Karamin basket din ta juya da sauri ta nufi kofar falon
har Kamar tana dan sassarfa ta shige ciki, harta wuce idanun Mahmud suna binta Nan
da Nan yayi kicin-kicin da fuska daman ga Sameer ya tabo shi ga itama da kalar nata
shirmen, cikin zafin nama ya kashe motar ya Kama kofar ze bude Sameer ya kamo
hannunsa ya rike Yana girgiza masa Kai kafin ya dungule dayan hannunsa irin na roko
din nan yace.
"Pls Dan Allah cool your temper kada kaje mata a haka kayi Mata uzuri Batasan Kai
ko waye ba, Kuma infact ma laifinka ne ka tafi ka barta a gida har zuwa wannan
lokacin Kuma tana ganin hakan da tayi shine dai dai koni nayi supporting dinta
hakan shine dai dai ta nuna maka tasan haqqin abinda ka bar mata amana" .
A Dan fusace ya kalli Sameer.
"Nine na Bata amanarsa da izuninwa ta fito nan wato. ya kalleta yanda yakeso ko?
Matata take kaiwa Mai gadi abinci wannan wane irin zubewar aji ne a gurina? Dubi fa
yanda ta fito? Ko baka gani ba?"
Ya fada yana kallon Sameer.
"Ni banga wani Abu na rashin kyautatawa ba a shigarta, kawai dai idonka wani Abu ya
nuna maka na daban gaskiya".
Hannunsa ya zare daga cikin na Sameer din ya bude kofar a hankali ba Kamar dazu ba
zagayowa Sameer yayi ya rufe motar yabi bayansa Dan Idan ya Bari ya shige irin na
jiya ze masa ya ajeshi a waje, kofar ya bude wani sanyi da kanshin girki Dana
turarikan daki sukayiwa Sameer sallama Bata Nan sai tv a kunne ana karatun har
lokacin.
Direct gurin dining Sameer ya wuce yana fadin Bari na Fara da Nan Idan na gama ma
gaisa tunda ba bako nake ba ya Fara budewa Yana kallon Mahmud Yana fadin.
"Tab da alama Allah ya tarfawa garinki nono irin wannan delicious".
Gaba Mahmud yayi Bai tanka Masa ba ya shige ciki.
Kofar bedroom dinta ya kalla har dariya take bashi bilhaqqi da gaske tsoransa
takeji bare Kuma da jiya ya Dan motsa mata Jamiyya.
Ta Dan Dade a bedroom din nata daga baya ta bawa kanta kwarin Gwiwar ta fita ko
banza bazata bada kofar da wani na waje ze gane da 'yar tsama a tsakaninsu ba Kar a
Raina Mata wayo, fuskarta ta Dan Kara shafawa powder kadan ta Dan Kara fesa mouth
freshner Mai kamshi apricot ta nufi kofa tana budewa saura kadan yau ma suyi karon,
da sauri taja Baya. Shigar kananun Kaya yayi as usual dan zaman da sukayi ta
fashimci kamat ya samu wani freedom ne na sakewa, trouser black da milk T-shirt ne
a jikinsa hannunsa daure da agogo sai waya a hannunsa. Baya tayi da sauri tana Dan
zare idanu Dan ba Karamin tsoro taji ba, Shima kallon ta yake Kamar ya rungumota ko
yaji relief na abinda yakeji a zuciyarsa, amma sai ya share ya Mika hannunsa ya
kamo nata ya natso da ita kusa dashi Sosai Yana Fadin "kin tashi lfy?".
Ya shafi gefen fuskantar, cikin siririyar murya tace masa
"Ina kwana? Shiru yayi Kamar beji ta ba, ya janyo ta suka Fara tafiya a cikin
corridorn, sai da suka Fara gangara steps din taji yace waya Baki izinin fita gurin
watchman din can?"
Ya Dan matse hannunta dake cikin nasa.
"Wash!!! Allah ta fad'a ba tare data shirya ba. Dan da gaske matsewar ta shigeta
dago Kai tayi cikin narke fuska Kamar zatayi kuka dai dai lokacin Sameer ya dago
Kansa daga daddana wayar da yakeyi Jin maganarta Sam beji tahowarsu ba wani irin
perfect match couples ya gani sun masifar dacewa da juna ya Dade bega ma'auratan
da suka burge shi kamar su ba, a zuciyarsa yake Fadin.
"Masha Allah".
Zahrar Tace masa.
"Ba kowa, Dan Allah ka sakar min hannu wlh zafi...."
Ta fada cikin shagwabar da Bata San tayi ba.
Murmushi Sameer yake ta saki daga inda yake Dan ba karya yasan muhmud yayi dacen da
Basu zata ba abun kamar a film yake ganinsa. Dan lokacin da suka Fara ganinta da
Kuma furucin da shi Mahmud din yayi ashe Allah ya karbi addu'ar.
Dan gyaran murya Sameer yayi Yana kallon Mahmud din tare da fadar.
"Yallabai a bar madam ta karaso mu gaisa Mana ni ba mazauni babe gaba nayi daga
Nan"
Ya fada da sigar zolaya duk yaga har yanzu kamar Yana Jin zafinsa tun maganar da
yayi masa na Safnah.

Sassauta rikon hannaun yayi suka ida gangarowa directly dining area ya nufa yana
zuwa ya ja Mata kujera ya zaunar da ita sannan Shima ya janyo ya zauna.
Gurinsu Sameer ya karaso daga inda yake zaune Yana fadin.
"Madam barka da Asuba kingan ni sai yau ki?".
Ya fad'a yana Zama kusa da Mahmud.
A kunyace ta amsa da "lfy kalau Ya Sameer ya kaje gida? Ina madam?"
"Komai lfy ya hakuri damu?".
'yar dariya tayi kafin ta Mike ta Fara bude abincin Wani daddad'an kamshin ne ya
doki hancin Mahmud har Saida ya lumshe idonsa, Dan kallonsa tayi sannan ta kalli
Sameer tace "me za'a zuba?".
Kai Sameer ya girgaiza Yana fadin "ai ni na riga ku ci tun shigowarmu naji bazan
iya jiran masu gidan ba saina shide Ina jin kamshin delicious Amma ace saina jira".
Ya fad'a Yana dariya.Dan murmushi Mahmud din yayi.
"Wato ko Ina saika nuna halinka ko?".
"Pls zuba min kawai".
Kallonsa tayi kasa-kasa, tace "Toh"
Masar dankwalin turawan ta zuba sannan ta zuba pepper chicken din ta tura Masa
sannan ta zuba kunun Madarar sannan ta koma ta zauna a darare.
Wani cup din ya zuba kunun Madarar ya dauko da fork ya matso kusa da ita da plates
din abincin yace.
"Oya saka hannu muci".
Ya wani hade gabas da yamma alamun ba wargi Kai ta shiga girgaizawa alamar ta koshi
Shima ture abincin yayi Yana duban Sameer.
"Muje kawai"
Ya fad'a yan Jan kujerar baya.
"Zanci".
Ta fada a gajarce.
Komawa yayi ya zauna Yana fadin "fine tunda zakiçi gara Idan mutuwar zamuyi mu mutu
tare Dan naga abinda Mata suke yayi kenan Idan aka Basu Wanda ba shine zabinsu ba
su kashe shi su auri wanda sukeso".
Tunda ya Fara Kora bayani Zahra tayi masa kur da ido tana Mai maita.
Kai Sameer ya shiga girgaizawa Yana mamakin wani sabon hali da Mahmud din ya tsira,
yaga alama nema yake ta Hana yarinyar Nan sakat.
Ita Kuma tunda ta furta zanci Bata Kara tofa ko kalma daya ba, sai kawai ta dauki
fork ta cako Irish din ta Kai bakinta ta tauna ta hadiye, pepper chicken din ta
dauka taci ta dauki kunun Madarar ma ta Sha duk Yana kallon ta shi kuwa Sameer Yi
yayi Kamar Allah Bai halicce shi a gurina ba.
Tana gamawa ta tura kujerar da take Kai baya sannan ta dubi shi ido cikin ido tace.
"Gashi naci idan kana tunanin zan zuba maka poison a abinci kayi kuskure lalacewar
tawa Bata Kai haka ba, Idan na kasheka wace riba zanci? wato ka tafi lahira free
ko? duk lodin zunuban daka dauka niga sakarai na lodawa kaina, to Bari na fad'a
maka ba saina aikata zunubi irin haka zan rabu da Kai ba A'a salin alin kowa ze
kama gabansa ni da Kai tunda daman masu iya magana na cewa tsintacciyar magen Bata
mage nasan komai Daren dadewa zaka koma inda ka fito".
Ta fad'a Tana wurga masa harara ta wuce ta kyalesu batabi ko takan Sameer da yake
fadin "Allah ya huci zuciyar amaryarmu".
Da ido Mahmud yabi Zahra har ta bacewa ganinsa "Wai shi yarinya kamar wannan zata
saka shi gaba ta fada Masa son ranta amma yayi shiru Yana kallon ta".
Sameer ne ya katse Masa tunanin da yake.
"Dan Allah kada ka koya matsa tsiwa wlh da gani Bata Saba ba, bakaga jikinta har
rawa-rawa yake ba".
Ya fad'a Yana kallonsa.
"Jikinta na rawa kenan Kare mata kallo kayi har kaga jikinta na rawa ni ban gani
ba?".
"Subhanallahi! Wace irin magana ce haka wlh ba haka nake nufi ba, Bari naje kawai
sai munyi waya".
Ya Mike Yana aje rafar dari biyar guda biyu Yana fadin "A bawa madam ace Mata na
wuce tunda ka Hana muyi sallama".
Ya biya Kan center table ya dauki keys dinsa yayi gaba tunda yasan ba magana Mahmud
ze Masa ba Dan da gaske yazo wuya yanda yanayin fuskarsa ta nuna.

Bayan fitar Sameer, Mahmud kasa ko motsin kirki yayi wai shine tsintacciyar magen?
Da gasken gaske maganar ta dokeshi kwafa yayi Yana fadin zakiga tsintacciyar mage
iya ganinki sai kin gane bakin rijiya ba gurin wasan makaho babe".
Ji yayi kwata kwata abincin ya fice masa raga Rai duk yanda yake jin yunwa ture
abincin yayi ya Mike ya nufi bedroom dinsa Bai jima ba ya fito cikin shigar yari
filtex fari dinkin boda da farar hula a Kansa Yana baza qamshinsa na Ibada, yayi
waje.

Tunda Zahra ta Fadi maganar dake ranta taji zuciyarta wasai, gefen bed dinta ta
zauna tana mita.
"Haka kawai saika wani ringa sakarmin magana ba control duk abinda yazo bakinka
saika fad'a mini, Wai na saka wani Abu girkinma ba saina Kara yo da Kai ba sannan
na Zama suspect daman saboda A kashedin Ammah ne yasa nayi, kwana biyu amma kamar
na shekara duk ka matsa min ka karbe min waya nayi Shiru na Zuba maka ido Naga
gudun ruwanka, na fita mikawa bawan Allan Nan abinci kace da izininwa? Haka kawai
ka zamar min karfen kafa".
Ta fad'a Tana kwafa.

Tunda gari ya waye Ammah Bata zauna ba shirye-shiryen tafiyar Inna maimuna take
wadda zata tafi yau, cikin Shirin fita unguwa Mama ta shigo lokacin Ammar na zubawa
innar kilishin da Abba yasa akayi Mata zaunawa tayi tana Fadin "Inna yau zakiyi
Mana ta Baki wlh ba dadi".
"Kayya Hajiya Rabi banda abun yazo da sammazi Aida na jima da tafiya gida daga zuwa
biki na share our na zauna kinsan da Ardo Yana Raye hakan ba zata faru ba yaushe ze
Bari".
"Haka ne Kam Allah yayi musu Rahama".
"Amin" su Inna suka amsa.
Leda mamar ta aje kusa da innar tana Fadin.
"Gashi Inna ba yawa Allah ya kiyaye hanya ni fita zanyi unguwa nasan kafin na dawo
kin tafi".
Gdy innar da Ammah sukayi Mata ta tashi tana yiwa innar fatan sauka lafiya.
Sai bayan ta wuce ne innar ke tambayar Ammah ina Hameeda ne Naga tun she jiya da
safe bata qara ganinta ba.
"Jiya kina barci tazo Nan Wai ta tafi Jos gurin yayar mamansu larai".
"To ba laifi hakan ba laifi daman shekaranjiya ne da dare na fita zanje can inda na
baza ganyen yandi Dana shanya naji uwar tana surfa Mata zagi ban dai San dalili ba
Amma naji ita yayar tata tana Fadin sai kije kiba Zahra hakuri Mana tunda kanwar
uwarta ce ni dai Nan na barsu Dana dauko shanya ta".
"Allah ya rufa asiri kowa yayi nagari Kansa ya yiwa kuma sharri Dan aike ne duk
inda ka tura shi ze dawo, bansan abinda yarinyar Nan ta tsare musu ba, bana raba
day biyu da abinda sukasa Hameedar tayi inaga daga baya ta gane Bata kyauta ba
shine tayi magana uwar ke zaginta".
Sun Dade suna tattaunawa.
Gurin Sha Sha daya da rabi magaji yazo ya dauki Inna maimunar zuwa gidan Zahra.
Zahra na barci Dan batasan lokacin da barci yayi awon gaba da ita ba, cikin barcin
taji alamar bell din kofa ta yunkura ta tashi ta yafa Veil din rigar saman
gashinta.
Tana budewa taga Inna maimuna da magaji, jikin innar ta fada kawai sai ta saki kuka
Wanda ita kanta bata San kona menene ba.
" Ke matsa can da Baki rabuwa da shiririta saboda Allah menene abin kuka
magidanciya dake, Dan Allah duba min Nan Mai sunan malam wannan ai rashin wayo ne
koba haka ba?"
Ta fad'a Tana kallon magaji, duriya yayi Yana fadin "kumfi kusa Inna na bankwana ne
tunda Idan Kika shige wannan lungun Sai baba ta gani, ni Naga ma kinyi Rana gaskiya
har yanzu Baki tafi ba".

"Ai a Gombe zanyi kwana biyu gidan Dan aminiyata da nayi rainonsa to nayi Masa
Alkawarin zuwa idan zan tafi".
Ita dai Zahra tunda ta kwantar da kanta a cinyar Inna maimuna Bata Kara dagowa ba,
jinta a jikin innar sai takejin wani sauki da nutsuwa suna saukar mata.
Gashin Kanta innar ta Dan shafa inda gashin ya fito tana Fadin shi dai wannan
gashin baisan kitso ba Kullum Yana Nan a nannade kamar gammo".
Dan turo Baki tayi tana Fadin
"Ya zanyi kinsan ba kitsuwa yake ba ko anyi idan ya Dade kwana biyu ne kawai ga
zafi".
"Allah ya kyauta kawai dai 'ya'yan zamani Amma har yaushe za'a yita Zama da Kai
haka? Yau Wai uwar taku tace meya samu wayarki ko an Kira Bata shiga? tasan ba
rashin caji bane tunda ance Kuna da wannan abar Mai amfani da hasken Rana"
Dan Jim Zahra tayi tace ya karbe wayar ai hakan be dace ba, Sai kawai tace.
"Nima bansan meye matsalar ba kawai rufewa tayi taqi kunnuwa".
Magaji ne Wanda yaketa faman cakular waya dago Yana fadin dauko mugani ko abun
minor ne".
"Bata gurina tana gurinsa ban sani ba ko dubawa ze bada ayi".
"Shu wa?"
Ya fad'a da sigar zolaya, banza tayi masa kamar bataji ba.
Tashi daga jikin innar Zahra tayi tana Fadin Bari na dawo wlh murnar ganinki ta
mantar Dani ko ruwa ban kawo Miki ba". Tayi gaba innar na Fadin "dawo Zahra'u nida
ba bakuwa ba".
Gaba tayi abunta.
Saida ta ciko tray babba da dangin Zaki da sanyi har sauran pepper chicken din ta
zubo musu, tunda ta aje innar ke binta da kallo tana jinjina abin wannan cimakar
bata mai Karamin kafin bace ko ance gida tallafin qungiya ya samu har abinci ci
susuka dauki nauyin bashi?"
Ita dai shiru tayi Bata tofa ba Amma a kasan zuciyarta da maganganu fal Wanda zasu
tattaunawa da 'yarta.
Ware ciki magaji yayi ya kwashi gara har Inna na Masa Dan biki.
Wayarsa Zahra ta barba ta Kira Ammah ta gaisheta itama abinda ta fadawa innar ta
fada Mata game da wayar lokacin data sauke wayar harda share 'yan hawayenta, magaji
Yana Mata tsiyar shatwabarta tayi yawa ita Batasan ta kusa Zama uwa ba,Inna na Taya
shi.
Sai da Innar ta Gama sannan ta tambayi Zahra.
"Wai Ina Mai gidan nawa ne banji motsinsa ba tunda nazo?"
Kafin Zahra ta lalubo abin fad'a magaji ya rigata Yana fadin.
"Ai kin baroshi can a unguwar mu gashi nan suna magana da Ya Abdul Hakeem a kusa da
masallaci har suka daga Mana hannu".
"Awoh to ai kasan ban waye dashi ba sai a hankali".
Nasiha Sosai da ban baki Inna maimuna ta Kara yiwa Zahra tare da kara jaddada Mata
mashinmancin biyayya ga miji.
Kaya Zahra ta zubawa inna a wata babbar leda harda atamfa dasu turaruka taba
Magajin ya rike mata.

******
Tafiya ce miqqqqiya daga Azare zuwa Babban mutum ta Babura jihar jigawa, direban
daya dauko Mama da Asabe ya Dan juyo yana kallon Asabe wadda ta maida hankali gurin
cin doyarta da kwai da suka saya a kanya babba yace ",munzo Babban mutum fa Ina
zamuyi kinyi shiru alhalin kece idona tunda wannan ba yanyata bace".
"To na manta wallahi kasan da Dan Habu muke zuwa na zata shine ita dai Mama Bata
cewa komai Dan niqab nema a fuskarta badan ta matsu da son ganin malam na bande din
ba da ba yanda za'ayi tayi wannan kasadar Dan yanda ta fadawa Abban Itas/gadau zasu
wata dubiya Alhajin yaso Bala direba ya Kaita ta nuna Masa da kawarta matar tshon
Ambassador zasuyi tafiyar abinda ya Hana Bala direba kaita kenan, hanyar tinkin ta
nuna Masa alamar Niger zasu shiga.
"Yanzu ke Asabe a she Niger zamu shiga shi ne kikace min kauyen Babban mutum wlh da
bani da takardar ecowas da Saida na zubeku ku nemi wadda zata karasa daku kinsan
kuwa yanda suke da doka da order?".
Tafiya ce miqqqqiya daga Babban mutum zuwa bande, sun Sami tarba Mai kyau daga
yaran malam na ciki suna fitowa su Asabe suka shiga malam din yana zaune akan buzu
da wani zabgegen carbi a hannunsa ya amsa musu sallamar su suka zauna suna gaishe
shi.
Asabe ya dago kai kalla.
"Baki fad'awa Hajiya sakona ba?"
"Allah ya taimaki malam na fad'a Mata cewa tayi na kawota gurinka tazo taji Koda
yanda za'ayi lamuran ne suke neman canza fasali".
Carbinsa ya Fara ja yana girgiza Kai yayi hakan kusan say uku kafi ya sauke wani
dogon numfashi yana Kara girgiza Kai.
Mama cikin kidimewa ta furta.
"Da matsala ko malam?".
"To da matsalar Amma Abu mafi ban mamaki shi yaron har yanzu bana ganin komai akan
Lamarinsa kwata-kwata sai yau Naga wasu mutane a Kan lamarinsa da Kuma itama
yarinyar an tasa ta gaba da dafa'i shiri Kuma na gasken gaske sai dai naga wata
tafiya a gaban mijin nata da alama Kuma tafiyar da Alkhairi q a cikinta sai dai
idan dauke hankalinsa za'ayi daga garin kwata kwata, idan ya tafi ya kasa ko
tunanin garin bare ya dawo, idan ba haka akayi musu ba ba makawa sai kin Zama 'yar
kallo a gidan dan duk yaran gidan Mata ba wadda tauraruwarta ta kama kafar tata da
gaske haka Allah ya yita da madaukakin Alkhairi".
Zuru Mana tayi ta kasa magana, maganar dai ita kenan Zahra tafi nata 'ya'yan.
"Malam ayi duk abinda ya Kanata inda hali ma ya rattaba Mata saki kafin yabar
garin".
""Abinda ban gani ba kenan a cikin auren nasu Dan Idan shi ne ze saketa to inaga
sai dai ta mutu da auren Dan Banga hakan ba a tare dashi,ni a yanda na gani a
istiharata ma ya Santa batun a Nan garin naku ba Kuma da soyayyar ta Mai karfi a
zuciyarsa wadda har abada baze iya rabuwa da ita ba, ayi dai hakan yanda Idan
iyayenta suka gaji da jiran dawowarsa Bai dawo ba su raba auren da Kansu". Bayanin
ya kwantawa da Mama hankali, ya kawo abubuwa ya bata har Wanda za'a hada da tuaren
wuta a bawa zahrar Idan harta turara Mahmud ya shaqa shida Azare har abada.
Kudi masu kauri Mama t✨✨
✨✨

💎 AUREN HUCE HAUSHI 💎

✨✨
✨✨

MAMAN FATEEMAH

PAGE TWENTY FOUR (24)

_____ Tun bayan tafiyarsu Inna da magaji sai gidan ya zamar Mata shiru Bata
Dade a parlourn ba ta koma ciki, da taga tunani yana neman ya dameta saita dauko
qur'an dinta ta Fara karatu Saida taji Kiran sallah ta aje taje tayo alwala.
Bayan ta gama sallar ta Haye gado ta Kara A/C tayi kwanciyar ta ba tafi minti
talatin da kewnciya ba taji alamar Baki ana Danna bell, tashi tayi ta nufi kofar da
gaske dai bazata samu barcin na kirki ba,Kofar ta bude a hankali su Amatu ita da
Aunty safiyya ne guri daya suka zauna a Dr sulaimanu Adamu model school of Hygiene
inda tayi service, su Kuma permanent lecturers, rabon ta da Amatu tun ranar daurin
aurenta dan lokacin da zata wuce jama'are garinsu Bata biyo ta gidan Ammah ba daga
gidan Aunty Hasana ta wuce kawai. Cikin nuna tsantsar farin ciki Zahra ta rike
hannun Amatu tana fadin "wlh nayi fushi Amah Ina nan Ina jama'are? Amma kikaqi
dawowa ni Aunty safiyya zanyi welcoming kawai Amma ke kam dai sai a hankali kawai,
Aunty sannu da zuwa". Ta fad'a Tana Basu hanya tare da karbar yaron Aunty safiyya
dake hannun Amatun.

"Hakan ma na gode tunda an karbi Auntyn ai shike nan tunda ita ta gari batayi laifi
ba saini da nake can kauyen mu".
Ta fad'a Tana Zama a cikin one seat dake kusa da ita.
"Eh wlh Aunty tana da excuse a gurina tunda nasan Bata Nan taje gida sokoto Amma ke
kuwa ko waya fa Baki Kira kinji ya ake ciki ba".
"Kice dai ban Kira ba. Amma tambayi Sajida kiji na kirata yafi sau ashirin ma ke
dince lokacin Kiran baze yuwu ba Sai ki qara narkewa".
Dariya suka saka su duka harda Aunty safiyyar.
"Wlh Amah saina rama kinci bashi, Wai na narke kamar wani danyan tuwo".
"To da mecece? mutuniyar dake somewa Kikayi fa dif kika dauke wuta".
Kyale Amatu Zahra tayi ta karasa kusa da Aunty safiyya ta zauna ta Dora Shureem a
Kan cinyarta tana Fadin.
"Aunty sannu da zuwa Ina yini?"

"Lafiya kalau Amarya ya Amarcin Naga ya barbeki kanwata Masha Allah".


Dan sinne Kai tayi tana Fadin "Kai Aunty Ina wani Amarci a Nan kawai dai".
"Gulmammiya Kinga yanda kikayi wani mahaukacin kyau kuwa? Ai da gani Amarci ya
tabbata a gare ki,wa Zaki kife a baibai yarinya Kar nake kallonki fa".
"Allah ya shiryeki tunda haka Kika zama, Bari ki gani".
Ta Mike da Shureem a hannunta ta nufi kitchen, saida ta Zuba musu kayan garar a
plate ta dauko musu ruwa da drinks ta dauko plate ta fito tana Fadin "Amah shiga ki
dauko dayan Dan Allah".
Sai da suka Gama sannan Zahra tace su shiga suga gidan, ko Ina suka shiga Fadi suke
Masha Allah! a gurin fridge din dake cikin Dan Arc din dake tsakanin kitchen da
dining area ne Aunty safiyya ta kasa hakuri Saida ta magantu lokacin data Kai hannu
ta bude tana fadar.
"Yau ne ganina na biyu da fridge din nan naso shi kamar qaddara Amma da aka fad'a
Mana kudinsa Saida na Raina kaina"

"Kai haba Aunty bakiyi niyyar saye bane".


Zahra ta fada.
'yar dariya Auntyn tayi. "Bazaki gane ba Idan ci baizo daya ba ai koshi ma baya
zuwa daya".
"Haka ne kam Aunty".
Amatu ta fada, suka nufi bedrooms dinta ko Ina dai maganar daya ce Masha.
Amatu ce ke fadar "Allah ya mayar damu danshinki".
"Amin. Amma Banda kalubale irin nawa, ba Dadi Amah har gobe abun Yana damuna bani
da nutsuwa ko Kankani wlh duk lamurana sun tsaya cak bani da wani karsashi irin na
amarya a gidanta, komai ganinsa nake Wai banbarakwai kamar a mafarki haka".
Sai Kuma idanunta ya ciko da hawayen da taketa kokarin kada su zubo.
"Ayya haba Zahra kiyi hakuri Mana, ai zuwa yanzu yaci ace kin hakura da koke-koken
Nan tunda Mai abkuwa ta abku ai sai hakuri ki rungumi abinda Allah ya Baki ki
dangana wata Rana sai labari".
Aunty safiyya ta fad'a.
Parlour suka dawo sukaci gaba da Hira, rabi duk ban Baki ne Aunty safiyyar kewa
Zahra da nuna Mata ribar hakuri a cikin hirar ne Amatu take fadawa Zahra sakon
Sajida na tana kiran wayata Amma Koda yaushe switch off.
Dan lumshe ido tayi sannan ta bude tana kallon Amatun.
"Matsala wayar ta samu shi yasa ba'a samuna Amma in Sha Allah soon zan sayi wata,
yanzu bani taki na kirata".
Wayar Amah ta Mika Mata tana dialing din number ta.
Tana dauka ta Fara mata tsugudidi.
"Yau wacce Rana Amatu ta kirani".
"Assalamu Alaikum ayi sallama Mana bestie".
Ta fad'a tana murmushi.
"Kai!!! wa nakeji haka bestie, haba Dan Allah kin kyauta kenan ba waya ba wasika
kin barni a tunani kala-kala Sam na kasa samun nutsuwa". Tashi Zahra tayi ta shige
ciki tana Fadin "Bari kawai bestie guy din nan ya fa karbe wayar tun ranar da Kika
tafi ya dauketa da safe daya shigo, shine fa daya shigo ya tarar duk na hargitse
gado ina neman ta yace tana gurinsa, ya kama min wasu zantika akan Kiran da Musbahu
yayi ranar ni kuma na kasa hakuri shine yayi min Rashin mutunci Kuma ya hanani
wayar".
Ta fada kamar zata fashe Mata da kuka, tambayar ta tayi yanda abun ya faru Bata
rufe Mata komai ba ta fada Mata. Bata katse Mata hanzari ba har ta gama.
"Amma ban taba sanin Baki da wayo ba sai yau, Gaskiya Baki kyauta ba ko alama Ina
hankalinki ya tafi kada ki Kara Koda Wasa saboda wani ki ciwa mijin aurenki fuska
ai wallahi jarimi ne daya iya hadiye fushinsa bakiji a jikinki ba".
Ta fada a kufule, kit ta kashe Kiran.
Ajiyar zuciya Zahra ta sauke tana kallon wayar a zuciyarta tana fadin ji a jiki na
nawa Kuma ba ze fadu bane shi yasa.
Lokacin da zahrar ta fito wasu bakin ta tarar sun shigo su biyu har Amatu ta kawo
musu ruwa da drinks suna hira dasu Aunty safiyya, sallama tayi musu sannan suka
gaisa Nan Amatu tace musu "ga matar gidan nan".
"Masha Allah"

Suka fada a tare sannan babbar wadda zatayi kamar sa'ar Aunty safiyya tace "mune
makotanki da hannun dama sunana Hafsat Amma ana kirana maman junior, wannan Kuma
kanwata ce Nuratu da take karatu a Nan Abubakar Tatari Ali polytechnic (ATAP) aiki
ne ya kawo Mai gidana mu 'yan Taraba ne".
"Masha Allah! Allah ya taimaka ya bada sa'a".
Suka fada.
Sun Dan jima ana hira dasu sannan suka tafi har gate Amatu ta rakasu da ledar kayan
garar biki.
Suma mikewa Aunty safiyya tana goya Shureem da yayi barci, Dan langabar da Kai
Zahra.
"Wai har zaku wuce ne Kuma Aunty?".
"Eh mana zan shiga gidan fachalata data haihu bana Nan".
"Amman Banda ke dai Amah gaskiya tunda nasan kina garin Nan sai karshen wata keda
jama'are".
Aunty safiyya ce ta tari numfashin zahra
"Ai ita ke driving dinmu ya zan barta a Nan ta dawo Miki special ko weekend ne".
Alamar bude kofar da akayi ne yaja hankalinsu, Mahmud ne ya shigo Yana musu sallama
da katuwar leda a hannunsa, tunda ya shigo Aunty safiyya ke kallonsa ita dai tasan
wannan fuskar amma ta Yaya za'ayi haka ko Kuma kama ce kawai.
A cikin takunsa na cikakken namiji ya shigo, da sauri Zahra ta nufo gurinsa tana
Fadin.
"Sannu da zuwa". Tana Mika hannu zata karbi ledar.
"Da nauyi bazaki iya dauka ba".
Ya fada Yana kallon ta.
Har cikin kitchen ya shiga da ita sannan ya wuce bedroom.
Amatu ce ta zunguri zahra.
"Ke! meye hakan Kuma? Kika wani sharesa Kada dai kice min sokoncin da kike bazawa a
gidan kenan ko Kuma Dan kin gammu ne kikayi wani biris dashi".
"Gaskiya Kam ki dage ki Kama mijinki irinsu tsada suke".
Aunty safiyya ta fada tana nunawa Zahra hanyar daya bi.
"Kai! Aunty Kuma ......"
Bata karasa ba Amatu ta Kama hannunta ta nufi steps din tana Fadin "kije kawai
tunda daman tafiya zamuyi saina shigo Saturday in Sha Allah".
Dan raurau tayi tana kallon Aunty safiyyar.
"Na gode Aunty ku gaida gida saina zo har gida ban gajiya".
Dariya Auntyn tayi.
'Haba dai sai dai mun dawo, wannan turaren kada kiyi Wasa dashi tun daga besse na
taho Miki dashi kakata ta wurin Babana take haduwa da Kanta Yana da matukar kyau
sosai ba sai fada Miki ba da kanki Zaki nema".
Dawowa tayi Saida ta rakasu har gurin mota duk da mitar da Amatu ke mata, ta
hadasu da kayan garar fal ledoji biyu dasu bokitan roba da mug masu kyau da plates
Wanda Aunty Hasana ta bada aka kawo mata saboda Baki masu zuwa.
Saida suka fice daga gidan sannan ta dawo ciki.
Bata shiga ciki ba a parlourn ta zauna tana mitar. "Idan na shiga me zan Masa
wanda yake ganina a wata Mai neman rayuwarsa".

***
Saida Amatu ta dai daita a titi sannan da Dan dubi gurin da Aunty safiyyar ke zaune
tana rungume da Shureem.
"Aunty nifa wani Abu ya bani mamaki da daure Kai"
"Kamar me fa?".
"Duk gari ya dauka an aurawa zahra Almajiri k'olo saboda ita ba 'yar Alhajin bace,
surutu dai gashi nan, ni Kuma yanzu Naga sabanin abinda ake fada, yaushe Zaki kalli
wannan kice Yana Qasqantacciyar rayuwa irin wadda ake fada?".

"Ni Nama fiki mamaki Dan ni dai Idan ba gizo idona yayi min ba ko Kuma kama ce ta
halitta tunda ance kowa Yana da Mai Kama dashi a wani gurin, da sai nace Miki M.M
DANGE na gani".
"Waye hakan?".
Amatu ta tambaya.
"Bazaki gane ba Amatu wasu Family ne a sokoto masu mahaukanta kudi Nima fa sau daya
na taba ganin M.M DANGEN a bikin wata cussing Dina zainab data auri Dan Family din,
Kai gaskiya bashi bane inaga Kama ce kawai, amma Kuma kamar harta baci sai dai ba
yanda za'ayi DANGE ya iya rayuwa a nan".
"Kamar Yaya Aunty?"

"Tab kinsan kuwa waye shi? ai inaga kaf ba Wanda ya mallaki abunda ya mallaka a
duk Family din, gashi yaro matashi Kinga gidansa na sokoto ma kuwa? Banda na Abuja
da sauran garuruwa, to in kuwa shine me zeyi da Dan wannan gidan ai ji zeyi kamar
Yana rayuwa a kurkuku ne, bama shi bane shifa ko bodyguard dinsa abin kallon ne
Suma sun Zama done fa"
Ido Amatu ta zaro.
"Kikace wannan gidan kamar kurkuku? Duk yanda na ganshi Aljannar duniya".
"Naki wasane Amatu. Allah ya kawo dalilin da Zaki shiga ko gidan daya daga cikin
families din DANGE ne kiyo kallon duniya me Kika gani a Nan kedai Allah ya Kai damo
ga garawa kawai, Dan dai a wannan zuwan da nayi sokoto naje yiwa zainab din barka
naji wasu a cikin family din sunata hirar MM DANGEN Wai ko ya bar kasar ya koma
turai tun bayan samun wata matsala Mai zafi a cikin family din wadda ta tada kura
har rayuka suka baci".
Da ire-iren hirarrakin suka karasa gidan barkar.
...
Tana zaune a Nan parlourn ya fito cikin kananun kaya da karamar leda a hannunsa
direct inda take ya nufo ji tayi gabanta ya Fadi.
"Ya Ilahiy" ta fada a zuciyarta.
Gefenta ya zauna Yana Fadin
"Wash!! I am tired wlh samo min ruwa Mai dan sanyi".
Yayi maganar yana dan matsowa jikinta. Da sauri ta tashi yabi ta da kallo Yana
kissima abubuwa da yawa a kanta kunyar ta tayi yawa yasan sai yasha fama kafin ya
rabata da ita yanzu dai most important thing ya samu shakuwa da ita sosai.
Ruwan da farm fresh yogurt da snacks ta bawo Masa, idonsa a limshe Kamar me barci
Amma Yana kallon ta yanda take tafiya kamar me counting steps sai rausaya take.
Table coffee ta janyo ta Dora tare da bude Masa ruwan ta Zuba duk Yana kallonta.
Ajewa tayi ta juya zata wuce taji hannuwan mutum duka biyun ya zagaye k'ugunta ya
mannata a jikinsa ta baya, yayi Mata bazata Dan ko motsin mikewarsa bataji ba ko
alama, a tare suka sauke ajiyar zuciya juyota yayi gabadayan ta suna facing din
juna Yana Mata wani duban kasa-kasa.
Narke fuska tayi Kamar zatayi kuka tace Masa.
"Menene Kuma? gafa ruwan Nan na kawo maka".
Fuskarsa ya matso da ita dai-dai tata yace.
"Haka ake tarbar miji? Ki bani abincin yunwa nakeji fa, tun safe banci komai ba
tunda kika tada min hankali abincin ya fice min daga Rai, waini Kika kalli kwayar
idona Kika gasa min maganganu son ranki ko?".
"Ni me nace, cewa fa kayi zanyi poison dinka ni banji haushi ba sai kai, kisa fa?
To me kayi min, ni na daina abincin ma ba shike nan ba ban dafa ba bare na zuba
maka guba".
Ta fada tana kokarin zame jikinta, Kara gyara rikon da yayi Mata yayi ya nufi two
seat da ita a jikinsa kan cinyarsa yayi Mata masauki, ya Kai hannunsa daya ya zame
veil din da tayi rolling gashin ya shiga shafawa yana fadin.
"Nifa da Wasa nake Miki dazun bada niyyar na bata Miki rai ba na fada, so I am very
sorry Baby in Sha Allah bazan Kara fada ba, na Saba haka nake yiwa kakata Hajiya
Inna a irin wannan lokacin na break shine na tunata da ita na fada Miki kema Ashe
lefi zanyi, yanzu muje na tayaki ki Samar Mana light Abu muci bana son cin Abu Mai
nauyi sosai da dare nasan kafin mu Gama anyi magariba ko"
Ita dai tayi tsumu tsumu duk ta takura fatan ta ya saketa ta fece tunda Allah yasa
yanzu ba 'yan tabe taben bane a Kansa a iya gashi kawai aka tsaya.
Dagota yayi daga jikinsa ya rike hannunta kamar wata 'yar baby suka nufi kitchen,
ledar daya shigo da ita ya dauko ya Dora a Kan cabinet din kitchen din Yana Fadin
"zo ki cire wadan Nan daga ciki.
Kayayyakin amfanin gida ne masu yawa harda su biscuits su chocolate, sai da ta saka
komai a muhallinsa sannan ta Fara hada abinda zatayi, kujerar kitchen ya samu ya
zauna Yana kallon movement dinta friend spaghetti Mai vegetables tayi sai tayi
gasmeat.
Lokacin data Gama komai an Fara Kiran sallah.
Tare suka fito ya mannata da jikinsa a haka ya nufi bedroom dinsa da ita suna shiga
ya zaunar da ita Kan sofa ya wuce toilet.
Sai daya rufe kofar sannan ta tashi ta wuce nata dakin wanka take sonyi.
Koda ya fito Bai ganta ba beyi mamaki ba yasan za'ayi haka, lokacin daya leka ya
fada Mata ya wuce masallaci tana toilet.
Saida yayi insha'i sannan ya shigo gidan abincin Mai gadi ya dauko ya futa ya Mika
masa, daya dawo be nemeta ba,sport news ya kamo yana kallon labarun wasannin da
akayi Bai gani ba.
Zahra Kuma da tayi sallah saita zauna tayi Azkar na yamma da Bata samu tayi ba,
data Gama tayi shafa ta saka riga da siket English waars combination din milk da
maroon tayi rolling da milk veil tayi kyau kamar ka dauke ka boye body mist kawai
tayi amfani dasu kusan kala uku cikin Wanda ta gani a cikin locker din mirror dinta
sai kamshin ya Bata wani irin Dadi Mai kwantar da zuciyar me shaqarsa.
Plat shoes tasaka a kafarta ta nufi falon,jin gidan shiru batayi tunanin Yana Nan
ba Saida ta shigo sosai ta ganshi a kishingide da remote a hannunsa Yana kokarin
canza tasha.
Tashi yayi daga kishingidar ya zauna sosai Yana binta da wani mayen kallon, tunda
suka hada ido sau daya Bata Kara yarda ta kalleshi ba.
"Zo ga wayar ki Nan tunda Naga itama kinyi zuciya da ita kin bar min".
Ya fada yana Mika Mata hannunsa alamar tazo ba musu ta nufo shi cikin takunta na
nutsuwa, shi komai yarinyar Nan tayi burgeshi takeyi ga uwa uba Kuma ya fuskanci
tana da tarbiyya da biyayya sabanin yanda yake kallonta, Bai zaci zata kwantar da
hankalinta haka ba sai yaga ta tattara komai ta aje gefe abinda ya fuskanta kawai
dai Bata daukar raini.
Tana karasowa saita zauna kusa da kafafunsa a kasa taki zuwa gurin hannunsa da yake
Miko Mata. Dan murmushi yayi Shima ya sauku Yana facing dinta da karamar ledar dake
hannunsa, Mika mata yayi."Gata Nan ayi hakuri ki hada ta batirin ma yana da full
charge da sim a ciki, duk numbers dinki important suna ciki.
Wayar ta bude sabuwa ce Kar jujjuyata ta Fara tafi wadda ya Fara Bata tsada nesa ba
kusa ba kallon tuhuma ta Farayi Masa tana girgiza Kai tare da Mika masa wayar tana
Fadin.
"A Ina kake samun irin wadan Nan wayoyin na mahaukatan kudi wlh ba ruwa na ka rike
kayanka bana so ka maido min tawa ta asali kawai".

✨✨
✨✨

✨💎AUREN HUCE HAUSHI💎✨

Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu.


Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah s.w.a, salati da daukaka da Aminci
su tabbata ga Annabin Rahama Muhammad s.a w.w.

Page 25

________Dariya ya kama harda hawaye abinda bata taba gani ba.


Sororo tayi tana kallonsa, ita bataga wani abin dariya ba a maganarta, hannu ya
Mika ya karbi wayar kunnawa yayi ya Mika mata Yana kashe Mata ido tare da d'age
gira.
"Kina son kisan inda nake samun mahaukanta kudaden Nan ne?".
Kai ta gyada Masa.
"Good ki Bari sai ranar da Kika Zama ni na zama ke na mallaki kayana, a ranar nayi
Miki Alkawarin sanin komai nawa na duniyar Nan, Idan Kuma yanzu you are ready za'a
taimaki Dan Malam a lullubeshi da bargon ni'ima to? yanzu kuwa kisha labari har
wanda Baki nema bama zan fad'a Miki, tunda ke inda nake samun kudi kawai Kika
bukata baki son sanin waye ni?daga Ina nake?meya kawoni garinku? Gasu nan rab'ab'a
da yawa, to ki rubuta ki aje har abada ni Mahmud bazan tab'a ciyar dake ko shayar
dake ko wani Abu na jindadin rayuwa da haramun ba, duk abinda na Baki ki tabbata da
gumin halalina na nema, kinga wannan wayar da kudina na saka na saya Miki,wato kina
tsoron kada na Sato kayan mutane na kawo Miki ko?"
Kai shiga gigizawa.
"Ni ba cewa nayi kayi sata ba, gani nayi kana ta abubuwan da sai Mai wadata ne ze
iya yinsu Kai Kuma Naga...." Sai kuma tayi shiru tana kallonsa.
"Oya continue Mana,kinyi shiru wato Kinga bana aikin komai ko?".
Shirun tayi Bata Kara cewa komai ba.
"Tashi ni ki bani abinda zanci idan na biye Miki da wannan yarintar taki sai yunwa
tayi min illah kisa a Fara gulmarki ace kina barina da yunwa, ganshi kin sani
azumin da Babu lada".
"Ba Kaine kayi zuciya ba ka tafi kabar abincin"

Ta fada a shagwabe.
"Ki tashi ki bani kada lissafin ya canza fa"
Ya fada yana matsowa jikinta sosai, da sauri ta Mike ta nufi dining inda ta jera
abinci.
Table mat ta shimfida a Kan carpet din sannan ta dauko abincin ta aje.
Plate biyu ta dauko dayan ya janye.
"Ki Zuba Mana a plate daya ya Isa ai Kuma indai Ina gida plate din mu daya tunda
Kika yimin horon yunwa yau daga Wasa Dan kawai kewar Hajiya ta ta kamani shine Kika
horani duk ranar dana kaiki gabanta saina fada Mata tasan irin zaman da zatayi
dake, ni Dan gata ne a gurinta bana laifi zakiga yanda take sona".
"Ko?" Ta fada tana zuba abincin a plate, Dan tura Masa plate din tayi kusa dashi
"Gashi Nan ni bana Jin yunwa".

"Ashe zan Miki dura wlh, sai kinci kuji min yarinya da kinibibi Wai so kike da
karfi sai kin koya min surutu ne? Kin iya kalato abin magana da wani bakinki chut".
Ya fada yana shafo pink din lips dinta.
Taci Amman ba wani na kirki ba da gaske abinci Bai dameta ba barta dai da 'yan
ciye-ciye.
Bayan sun gama ne ta kwshe kayan ta gyara gurin duk Yana kallonta komai tayi kyau
yake mata gata ba wata babba ba sai dai akwai Sama da kasa masha Allah.
Lokacin data gama ne ya yafito ta da hannu,a hankali ta nufo shi kamar me counting
steps sai rausaya take, wani yawu ya hadiye, Dan risinawa tayi a gabansa duka
hannuwanta ya kamo ya zaunar da it kusa dashi.
"Zaki rakani unguwa?"
Ya fada Yana zame Mata veil din da tayi rolling gashinta ne ya bayyana biki sidik
dashi sai walqiya yake yasha gyara ga kamshin hair spray Yana tashi.
"Eh zani Bari naje na shirya".
ta fada Tana kokarin zare jikinta daga nasa. Duka hannuwansa yasa ya riko kugunta
ya hade ta da jikinsa.
"Ina zaki?wane irin Shiri zakiyi kinsan inda zamu ne kike sauri?".
Lakwas tayi a jikinsa da karfi da yaji so yake ya Saba mata da Zama a jikinsa gashi
baya ko Jin jauyin taba Mata jikin sai dai idan Bai soba.
"Bazaki tambayi inda zamu ba, kina Neman sake canza Kaya".
"Nasan gida zamuje Mana".
"Ai kece gidan, kinaji da so nake muje gidan da gaske mu roki alfarmar a bamu aron
me aiki daya Wadda zata zauna min dake kafin na dawo".
"Kafin ka dawo? Ina zakuje?".
"Au Ashe ban fada Miki ba, aikin NGOS din Nan ne ya taso suka gayyace mu zuwa
meeting da zasuyi a UK Kinga ai bazan zauna ba da dollars ko stalling founds suke
biyan mu, idan Allah yasa na samu da Dan auki Kinga na Kara jarina tunda Naga Nima
Ina sha'awar siyar da materials har munyi magana da Abba yace ze bani rumfa daya a
Muda lawal market na gwada ko ina da nasibi a cikin sana'ar, sannan Habib ma munyi
magana zamu Fara siyar da spare parts na motoci a nan Muda lawal market din dai".
"Allah ya bada sa'a, Kuma idan ka tafi sai yaushe zaka dawo? Ko kaima shike Nan
abinda yake faruwa Dani ze faru a kanka kaima, kada ka tafi ka barni Dan Allah
tunda nasan ba Sona kake ba baka ni akayi sadaka, Dan Allah ka taimaka ka kaini
Jordan tunda Ina kudin flight kawai ka taimaka ka fitar Dani daga kasar da sunan
Kai zaka tafi dani, bana son Ammah ta qara shiga cikin damuwa a kaina wlh Batasan
tashin hankali ba Sai Dana isa aure Kullum idan kaga Ammah a cikin tashin hankali
to a kan lamarina ne ni Kuma yanzu bana fatan na qara ganinta cikin bacin rai ta
dalilina, kaje ka fada musu zaka tafi Dani ko Kano ne ka Kaini na zauna gidan su
bestie kafin na samu visa, nagaji da Kasar nan wlh Ina da gata Amma sai walagigi
rayuwa ta takeyi anan Dan Allah kayi min wannan alfarmar Koda ita kadai zakayi min
ta karshe a zamana da Kai".
Ta kifa kanta a jikin kafad'arsa ta saki wani kuka Mai tsuma zuciya.
Bai hanata ba ya dai Kara matseta a jikinsa Yana shafa bayanta yasan abin Yana cin
zuciyarta ne bata rasa komai ba amma an dabaibaye Mata Jin dadin rayuwa kamar yanda
Baba malam ya fada masa. Sai da tayi Mai isarta ya dago kanta daga jikin kafadar
tasa.
"Kiyi hakuri kowa da irin tasa jarabawar ke taki a haka tazo, Kuma waya fad'a Miki
zan tafi na barki bazan dawo ba? Waye kuma yace Miki bana sonki? Kinsan tun tsawon
lokacin da nake dakon soyayyarki kuwa? Tun Baki san meye son bama yarinya share
hawayen ki Mahmud naki ne har abada, dole kije Jordan ke me gida sukutum a can.Amma
yanzu kiyi hakuri nema zani idan Kuma na zauna bakya son tafiyar saina fasa Sameer
yayi komai kawai nace madam ta Hana".
"Kaje kawai idan baka dawo ba nasan abinda zanyi".
"Keh! kina da hankali kuwa me zakiyi wlh zan turaki gurin Hajiya Inna duk da ban
shirya zuwa yanzu ba kawai ki Kira min ruwa, zaman Allah nakeyi zamanki nakeyi
badan ke ba Dana Dade da barin garin Nan".
" Ni Kuma?"
"Off course"
Ya fada da karfin gwiwa.
"As how?"
Share ta yayi kamar bai jita ba.
"Tashi ki rakani kada dare yayi, dauko Mana key din motarki na dana kada na tafi
ban Sanya albarka ba, ki canza shiga kada a kalle min kayana" fada Yana mikar da
ita daga jikinsa.
Duk kin haye min cinya kinsa sai ciwo take min".
Ya fada Yana Mata wani smile.
Bata kula shi ba tayi gaba abinta duk zuciyarta ba Dadi sannan tana jujjuya
maganganunsa a zuciyarta, kinsan tun lokacin da nake sonki? Danke nake zaune a
garin Nan gasu Nan dai da yawa.
Saida ta sakarwa Kanta ruwa sannan ta shirya agurguje ta saka wata Riga da siket na
atamfa super dinkin ya zauna das a jikinta ta saka mayafin da yayi matching da
atamfar ba tayi amfani da turaren kaya ba body mist kawai tayi amfani dasu a
jikinta kusan kala uku, sai ya bada wani sansanyan kanshi Mai dadi. Tana gyara
gyalen ya shigo dakin tsayawa tayi tana kallonsa shida yace unguwa zata raka shi
sai gashi da Riga armless da wandon ta farare tas na kamfanin Adidas sai taga kwata
kwata ya canza Mata ya koma irin 'ya'yan hutu din Nan na gaske wadanda Jin Dadi ya
gama ratsa su yayi wani irin fresh da shi.
Matsowa yayi kusa da ita Yana Dan watsa hannu irin dai na isassun yaran. Mayafin ya
kama ya ida rufa Mata a kanta.
"Kallon fa na menene? Kona canza Miki ne?".
Kai ta girgiza Masa.
"Baba son body language fa ki bude Baki kiyi min magana".
Yana janyo ta jikinsa.
"A'a kawai dai da naji kace unguwa zan rakaka kuma na ganka da......"
Sai tayi shiru.
"Karasa Mana sai Kika ganni da shigar nigas ko?"
Shirun dai tayi.
"Idan Ina tare da iyalin dole na sake, kema da nace ki canza ai na Shan iska nake
nufi ba Wai irin wannan ba, zo muje ki canza yawon Shan iska zamu ki min hira ki
bani labarin ki tunda ke bakya bukatar nawa ki bani happiness a wannan Daren yanda
duk inda nake na rinqa Tino da abubuwan su zamar min kamar kina kusa Dani".
"Ni dai Dan Allah ka barni haka muje kawai"
"Dauko key din to muje dare nayi Kuma Ina son ganin Baba malam da Abban mu, ko ba
namu bane?"
Ya fada Yana kallon ta, an samu cigaba, tunda ko banza tunda ya mamnatse ta take
iya kallon idanunsa ba kamar da ba da Bata yarda ta kalleshi.
"Namu ne". Ta fada a hankali, badan Yana very closer to her ba da ba lallai yaji me
take fada ba.
"Oya let's go".
Ya fada Yana nufar kofa, saida ya kashe electronics na gidan sannan suka fito Yana
time da karamar luggage a hannunsa,Kati ya curo daga cikin wallet dinsa ya saka a
kofar ya rufe, daga nesa Mai gadi ya hangesu sun nufi parking lot din gidan inda
motar daya take ajiye, a ransa yake fadar "duk inda wannan Dan ya fito Dan mafita
ne ba irin yaran Nan bane lalatattu kamar yanda aketa surutun abun masu kushe da
ganin rashin kyautatawar su Alhaji nayi masu gani kyautatawar nayi".
Yana can Yana tunani Bai ankara ba yaji Karan Horn alamun har sun karaso Yana can
Yana nashi zarafin.
Da gudu ya tashi Yana fadin Ayi hakuri nayi zurfi gurin tunani ne, a dawo lfy
Allah ya tsare".
Horn ya yi Masa suka fice daga gidan.
Suna barin gidan sun hau babban titi sosai motar su mama ta doso kofar gidan. Dan
saida suka hada turaren wutar ya kammala aka zabga Masa turarika masu mahaukatan
kanshi da mazubai Wanda dole yayi attracting mutum.
Daga Dan besa direban ya tsaya Mama da Asabe suka fito Asabe na rike da ledar Mai
tambarin gurin Saida turarukan wutar dasu humra suka nufi gate din gidan, Asabe CE
tayi knocking ta 'yar karamar kofar jikin gate din ya leko ya gane Mama tunda ya
jima a unguwar sai dai ita ba lallai yasan shi ba.
Da sauri ya bude kofar Yana fadin. "Hajiya kune haka barka da zuwa ina wuninku".
Ta rusuna ya gaishe su.
'yar dariya Mamar tayi tare da amsawa kafin tace masa.
"Munzo Kara duba Zahra ne tunda tazo ban samu mun shigo ba sai yau"
Cikin nuna girmamawa malam Sani yace. "wallahi kuma anyi sabani yanzu ba dadewa
suka fita da Mai gidan da kun lura ma inaga kunyi kiliya dasu a lokacin da zaku
shigo su Kuma sun fita".
Turus sukayi wannan ta kalli wannan.
"Ina suka fita daga kawo yarinya ko sati Bata rufa ba?" Ta fada da alamun bacin
rain a maganar ta ta.
"Wlh nima ban Sani ba tunda ba hurumina bane sanin hakan ba, sai dai ko Zaki Kira
ta a waya idan basuyi nisa ba sai su dawo".
Mama Bata taba danasanin rashin karbar number zahrar ba irin yau.
"Ba komai ga sako Nan ka aje mata idan Allah ya kaimu gobe Asabe zata dawo tayi
Mata bayaninsa"

Ta fada tana kallon Asaben, Wadda ledar ke Hannunta, da sauri ta mikawa Mai gadin
tana fadar "in Sha Allah zan shigo Amma a fada Mata".
"In Sha Allah za'ayi fada kin gaida gida".
Ya juya da ledar a hannunsa, want abu Asabe ta radawa Mama a kunne tayi saurin
tsayawa tana duban kofar da Mai gadin ke kokarin turowa.
"Malam Bismillah".
Ta fada Tana komawa tare da dauko Abu a cikin Jakarta.
Dawowa yayi Yana Dan sadda kai, kudin da Bata San ko nawa bane Mika masa.
"Ga wannan ba yawa Dan Allah a tabbata sakon ya shiga Hannunta komai dare"
"In Sha Allah Hajiya da shi zata shiga ciki, Allah ya Kara sutura na gode
madallah".
Ya fada Yana qara gyara rikon ledar da kyau.
"Hajiya ta haka akeyi Nan gaba ko wani aikin kike bukata da gudu zeyi Miki kinsan
su bugun Abuja ba bayanin da basa ganewa in dai kina ungo to zance ya Kare Abu sai
dai in Baki nema ba, ai Nima goben da sako zan taho Masa Naga alamar kamar zeyi son
abin duniya jifa yanda yayi caraf ya karbe kudin daman kamar jira yake.
Dariya sukayi gaba daya harda tab'awa, suka nufi motar data kawo su.

******

Tafiya suke yi Yana rike da Hannunta da nasa dayan, dayan Kuma Yana tuki cikin
kwarewa lokaci lokaci Yana Dan matse hannun, ganin sun dauki hanyar barin garin
yasa Zahra ta Dan dube shi.
"Wai Ina zamu ne?".
"Siyar dake zanyi, kinji yanda nake samun makudan kudina cikin sauki, duk garin da
naje haka nakeyi na duba kyakykyawar mace na aura idan an sake Dani sai nabi dare
na gudu nabar garin daman ba Wanda yasan daga inda na fito, bare ke yanda Allah ya
surantaki da sura ai ke sai nafi samun alheri a jikinki".
Ya fada Yana wani daure fuska.
Zuruzuru Zahra tayi ganin fuskarsa ba annuri ko misqala zarratin Nan da Nan jikinta
ya dauki rawa, duk sanyin ACn dake motar Saida gumi ya rufeta, kallonsa ta Karayi
still dai fuskar kamar bai taba fara'a ba a duniya.
Jikinta tsumar ya karayi kamar ana kada Mata gangi, cikin sarkewar murya ta Fara
magana bakinta Yana rawa.
Me nayi maka zaka cutar Dani?".
Rage gudun motar yayi cikin duhu, a hankali ya tssyar da motar, Zahra rufe idonta
tayi take hawaye suka wanke mata kumatu.
✨✨

AUREN HUCE HAUSHI

Maman Fateemah

Page 26.

________Sai da ya gangare sosai sannan ya kashe motar, chak ya daukota kamar 'yar
Baby ya rungumeta, dai dai kunnenta ya kai bakinsa ya hura Mata iska duka tsikar
jikinta ta tashi duk da tana cikin halin rudu bai Hana sakon zuwa ba.
"Ki rufa min asiri ada ace satoki nayi Nan da Nan kin rikice nayi Miki Kama da masu
irin wannan d'abi'ar? Wlh zolsyarki nakeyi haka Zaki shide min ki Kira min ruwa
daga fita unguwa mu bige da kwanan Asibiti cool down idan na sayar ai Nina kashe
kaina".
Ba zato taji ya saka harshensa Yana lashe hawayen Yana Wasa da harshensa a saman
idanunta, qanqameshi tayi, "Dan Allah ka bari".
"Na bar me?"
"Hakan ba Dadi".
"To da cewa nayi kiji Dadi? Ni nasaka kukan Kinga ai shanye hawayen ya kamani kada
muje inda zamu a juya min baya".
Ya fada yana shinshinar gefen wuyanta.
" Kiyi hakuri bazan Kara ba tunda wannan idon naki Mai arahar kuka ne Ni zanga
yanda za'ayi idan abin kukan ya samu".
"Cewa fa kayi ka Saba halinka ne ka Saba yin hakan Kuma fa fuskar ka ba Rahama a
ciki kamar Mai tsaron gidan wuta".
"Kai innalillahi! Mai tsaron wuta ni din?" ya fada yana fiddo idanu waje
"A'a ba Kai nace ba kamar nace".
"Ba cinya ba kafar baya"
" Nifa nayi ne Dan Naga idonki, idan kina cikin halin tsorata yana sakani nishadi".
Wayar sa ce ta Fara vibration a jikinsa, Dan zameta yayi daga jikinsa ya dauko
wayar ya duba tsaki ya d'an Yi.
"Dan matsala kawai".
Ya fad'a yana saka wayar a handsfree.
"Ya akayi Hayatu".
Dariya ce ta kwacewa Sameer Wadda Bai shirya Mata ba.
"Wlh zan kashe, wato abin dariyarka na Zama ko?".
"Sorry sir wlh ji nayi gaba daya tazo min, Kuma ko sallamar da nayi baka amsa min
ba".

"Ka Fadi abinda zaka Fadi Kona kashe da gaske Kuma sallama na amsa Kaine dai bakaji
ba, duk safiyar Allah baka tashi kirana ba sai yanzu da tsohon dare salon ka Hana
mutum rawar gaban hantsi, na fada maka idan Ina bukatar Abu ni zan nemeka Amma
tsabar saka ido sai ka kirani ni, to fad'i meya faru? Ina jinka".
Ya fada Yana maido ta jikinsa.
"Game da maganar tafiyar Nan ce anya zanje kuwa wlh jiya danaje sokoto daukar
wadannan hardcopy din na shiga gurin Hajiya Inna muna cikin magana saiga uncle
Mustapha ya shigo a sukwane bansan wane minafikin bane ya fada Masa nazo garin ba
tunda bana zuwa lokacin da suke gida, ya tasani gaba da sababin nasan inda kake ina
kallon su suna walaqiqin nemanka Amma nayi mirsisi naki fad'a musu komai, Ni Ina ta
faman lallaba mutuniyar taka amma Saida Uncle mustapha ya Bata lamarin Dan wlh kuka
take da hawayen ta bibiyu tana fadin Dan Allah na fada Mata idan mutuwa kayi saita
hakurw tasan ita kadai zata nesanta ka da ita, wlh yanda ta bani tausayi da bude
aiki kawai zanyi sai Kuma na tuna da warning dinka kawai na fasa, Kuma wlh yanda
uncle yayi ba abinda ze Hana shi bibiyata ta karkashin kasa ban sani ba a gida da
waje amma ya kake ganin za'ayi? Numfashi ya sauke me karfi yana Kare matse zahrar a
jikinsa har Saida tayi 'yar karar Jin zafi.

"Karar me nakeji a kusa da Kai ne?".

"Ina ruwanka tsabar saka ido, to madam ce a kusa Kona baka ita kaji for
confirmation, a'a Barta a gaisheta".
Tana jinka a speaker wayar take, ka Bari kawai Zancen baze yuwu ta waya ba idan
Allah yasa na shigo sai mu tattaunawa Kuma ka tabbata komai ya kammala kafin na
shigo goben in Sha Allah"
"Noted, in Sha Allah a gashe min da ita sosai a fada mata Batool tayi ta kiranta
dazu ba'a dauka ba".
"Ina ga a gida ta baro wayar ka ganta Nan sai rigima take zabga min irin tasu ta
shagwababbun 'ya'yan larabawan" ya fada yana dan matse dantsen Hannunta kadan.
"Wash Allah na da zafi fa".
Ta fada tana Masa wani kallo Mai ma'anoni kala kala.
"Allah ya bamu Alkhairi"
Sameer ya fada Yana kashe wayar Bai jira yaji abinda Mahmud din ze fada ba.
"Kinga kinja ya katse Kiran bamu gama bayani ba irin wannan Abu haka ai sai ayi
zaton muna hanyar shuga wata nahiyar ne".

Sunne Kai tayi a jikin kirjinsa, "Dan Allah ka Bari ni me nayi,".


"Ba komai".
"Bayani zakiyi da yaren garinku yarinya".
Gurin zamanta ya maida ta sannan ta tada motar suka koma kan titi, tunda zahra ta
koma gurin zamanta take Masa kallon tukuma da neman Karin bayani.
Amma saiya fuske abunsa kamar be gane ba, Yana ta faman tukinsa ko a jikinsa.
Zaranda hotel taga sun shigo, kallon mamaki tayi Masa a kasan zuciyarta tana
tunanin me kuma za'ayi a Nan shida yace unguwa zata raka shi to Wai mema ya hada
shi da hotel ne? Gurin da aka tanada don parking ya nufa ya kashe motar.
Fitowa yayi ya zagayo kofar da tare zaune ya bude ya Mika Mata hannunsa ta Kama ta
fito.
Kulke motar yayi ya jata suka nufi ciki, a Hanya suka hadu da wani security da gani
akwai sabo sosai a tsakaninsu.
"Ranka ya Dade an shigo lfy?
Ya fad'a Yana kallon Zahra a kaikaice.
"Lafiya kalau Ibrahim ya aikin?"
"Lafiya kalau yallabai".
Ya fada Yana niyyar wucewa yana Kara kallon Hannunsu dake sarke Dana juna.
" Ibrahim gafa madam Dina Yau na kawota taga mafakata".
Ya fada Yana Dan murmushi.
Dawowa yayi Yana fadin.
"Masha Allah yallabai Allah ya bada zaman lfy, ai Dani aka daura Auren babban
masallacin juma'a, madam sannu da zuwa gurin namu".
Ta amsa ta gaishe shi ya amsa yana Mata Allah Sanya Alkhairi sannan sukayi gaba,
dakin da yake kusan mallakinsa ya bude musu suka shiga lumshe ido Zahra tayi Dan
wani special kamshi da sanyi A/c ne ya bugeta, yanayin ba Karamin Dadi yayi Mata
ba, direct kan sofa ya nufa da ita tare suka zauna har lokacin Bai sakar Mata hannu
ba. Falon tabi da kallo ba karya komai yaji Dan an kawata shi sosai.
"Wai me zakayi a nan?"
Ta fada tana masa kallon ido cikin ido.
"Me kikeci na baka na Zuba? ai dai muna tare dake ko! zakiga abinda zanyi yanzu ki
zauna ki dan tayani aiki kafin naje unguwar ku gurin iyayena sallama".

"Dan Allah kaje Dani "


"Kai ! Naje dake Ina? Lallai kina so na amsa tambayoyi kenan kwanan ki nawa rabonki
da gidan? Kawai na kawoki Nan ne kisan dakin yana cikin abubuwan da suka zamar min
abin tunawa a zamana na garin Nan kinsan saboda ke na kama shi ya Zama permanent
dakina tsawon shekara kusan biyu da nayi a garin nan?".
Galala take kallonsa.
"Saboda Ni kamar Yaya?".
Wani kallo yayi Mata Yana Dan taune gefen lips dinsa na kasa.
"Naki Wasa ne yarinya,Wai kin zata daga cewa an bani Mata saina karba kawai? Niga
sarkin tausayi ko to Daman Nima Ina son kayana kawai dai kinfi karfina ne na mikawa
Allah kukana Ina zaune Kuma ya juya lamarin gareni tunda shiya hadani dake a inda
ban zata ba ya cusa min soyayarki lokaci daya nasan baze Bari na shiga gararin
rayuwa ba, duk rintsi ze kawo min mafita sai gashi ya kawo min lokacin da har nayi
given up Ina kokarin barin garin idan na shaida dauri Aurenku, amma fa da Allah
kadai yasan meya faru yanzu to Sai ya taqaita cikin shikimarsa".
Agogon hannunsa ya duba, Zahra tana kokarin magana ya katseta.
"Adana tambayar saina dawo Kinga idan na biye Miki ba inda zan fita, a 'yan
kwanakin nan kin mayar Dani wani parrot sai magana nakeyi ba comma ba full stop,
wlh kin canzani kwata-kwata da Hajiya Inna zata ganni Ina zuba haka hum..".
Ya fada Yana daukar luggage din daya shigo da ita da dayan hannun dayan Kuma ya
mikar da ita tsaye.
"Zo muje ki tayani shiryawa".
Nokewa tayi tana Dan ware idanunta. Shiryawa kuma? Kaje kawai Ni ina nan".
Gaba yayi yaga alama da gasken ze iya shashancewa a gurinta.
Komawa tayi ta zauna tana jujjuya lamarin bawan Allahn nan sai wasu maganganu yake
fada Mata ba tare da fashin baqinsu ba.
Kamshinsa shiya fada Mata wanzuwarsa a falon, a hankali ta dago Kai ta kalleshi
"Masha Allah" ta fada a hankali Dan ba lallai yaji ba.
Gurin da take zaune ya Dan tsuguna a gabanta ya Dora Mata laptop din dake hannunsa
da wasu takardu da list na sunan mutane kusan dari da ashirin da biyar daga local
government hudu Alkakeri, Jama'are, Zaki da Dass, karkashin makarantun Allo zasuyi
step down training a Nan Azaren schedule ne na aikin da payment dinsu.
Ta dago zatayi magana ya Dora Mata yatsa a biki "kiyi kawai idan na dawo kin
tambayeni duk abinda kike bukatar sani bana son nabar garin Nan aikin Nan Bai
kammala ba".
Ya Mike fuskarsa ya kawo dad da tata ya Bata light kiss a gefen kumatunta, saina
dawo take care". Ya nufi kofar da sauri da key din motar a hannunsa.

Harya rufe kofar Bata dauke idonta daga gurin ba, ita fa mutumin Nan ya Fara Bata
tsoro mutane suna daukarsa wani Abu daban ita Kuma tana ganinsa wani Abu daban.
Ta Dan jima Tana sakawa da kwancewa daga karshe ta watsar da komai ta dauki laptop
din ta shige cikinki bedroom din ta Haye lafiyayyan gadon ta bude ta shiga aikin
inda Allah ya taimaketa yaci karfin aikin karasa Masa zatayi.

*******
Lokacin da Mahmud ya fito Ibrahim da wani sulaiman ya Kira ya Basu aikin kula da
dakin da Zahra ke ciki duk da yasan suna da matakan tsaro sosai Amma hankalinsa Bai
kwanta ba sai da ya Kara Mata da nasa, gurin motar ya nufa bayan ya zauna ne ya
Ciro wayarsa ya bude ta haka Nan ya shiga CCTV da akayi connecting da wayarsa.
Hotunan ne suka fito rababa na dakinta yayi zooming qura Mata Ido yayi lokacin
data fito daga wanka tana daure da Karamin towel fararen cinyoyinta sunyi wani
sambal dasu ta Kai ta kawo Yana kallonta harta gama, tunda ya Fara kallon yake
sakin wani Nishi kadan kadan Dan da gaske ta yamutsa Masa tunani ji yake kamar ya
zubar da Alkawarin daya daukarwa kansa a kanta, komawa yayi baya na kofar gate ya
dauki hankalinsa ganin wata mota mata sun fito sun dauko wani Abu a Leda sun nufi
gate din gidan full screen yayi da gurin da suke ya waye da mama amma Asaben çe bai
ganeta ba yana kallon duk abinda sukayi har Zuwa lokacin da Asabe tayiwa Mama rad'a
a kunne ta Kira Mai gadin ta bashi kudi suka juya
da yanda suke kwasar dariya har da tabawa kamar yara sai abin ya bashi mamaki,
meya kawo su gidan su kadai ga Kuma motar da gani ta commercial ce, girgaiza Kai
kawai yana tunanin abinyi.
Da gurin malam ya fara zuwa ya Dan jima tare dashi kafin ya aje Masa Alkhairi yayi
Masa sallama, Yana Kara yi Masa addu'ar samun nasara a tafiyar da godiyar
Alkhairnin daya bashi, Habib ne ya Dan kalli Mahmud din bayan sun fito Yana
tambayarsa..
"Da gaske baka fad'awa Baba malam ba inda zakun kada fa yaji daga baya yayi fada
yace ka tsallake kasa baka fada Masa ba.
Kafadarsa ya dafa.
"Kada ka damu da kaina Zan fada Masa in sha Alllah".
Tare sukaje gidansu Zahra inda suka Dace suna kokarin yin knocking sai magaji ya
fito, daga gani wani gurin zaya yanda yayi Shar dashi.
Gaggaisawa sukayi kafin Magajin yayi musu jagora zuwan gurin Abban nasu. Anan falon
ganawa da bak'insa suka sameshi, sun gaisa Sosai a Nan Mahmud ya fada masa tafiyar
da zeyi, Abban yasa Albarka soshi.

.
✨✨
✨✨

AUREN HUCE HAUSHI.

MAMAN FATEEMAH

Page 27

_____Dan Jim Mahmud yayi kafin ya Dan muskuta kadan ya Kara sadda kansa kasa.
"Abba Dan Allah ko za'a taimaka a bamu Aron daya daga cikin masu aikin Nan Mata
su tayata Zama kafin Allah ya dawo damu". Ya fada a ladabce
Dan gyaran murya Abban yayi Yana fadin "Hakan babu laifi kayi tunani Mai kyau
baza'a bar yarinya ita kadai ba gara da babba, ba komai kome kenan da safe za'a
turo wadda zata zauna da ita, Allah yayi Albarka ya bada sa'a"
Sun jima suna Hira da Abban har suke fada Masa harkar kayan spares na kayan motocin
da zasu ringa saidawa, Albarka ya sanye musu sannan sukayi Masa sallama, har sun
Kai kofa Abban yace Bari ya fadawa Ammah ku shiga ku gaisa, a waya ya kirata ya
fada Mata sannan yace su karasa ciki.
A kofar gate na shiga ciki suka samu Musaddiq Yana jiran su, cikin ladabi ya gaishe
su Yana tambayar Mahmud Aunty Zahra, hannunsa Mahmud din ya Kama Yana bashi amsa
har suka shiga part din Ammar.
Sallama sukayi tana zaune a parlourn, sallamar ta amsa tana fadin. "Su Habib ne
sannunku Bismillah".
Ta fada tana nuna musu gurin Zama.
Basu zauna a kujerar ba sai suka zauna a Kan carpet.
"Ina yini?"
Suka fada a tare, "lafiya kalau ya wajen malam?"
"Lafiya kalau yace a gaisheku".
"Masha Allah muna amsawa, Allah yayi Albarka, yayi muku jagoranci cikin dukkan
lamuranku, ayi ta hakurin Zama da yara".
Ta fada a kunyace Dan har ga Allah tana Jin nauyin yaron da kaunarsa saboda
karamcinsa da halin fattako daya nuna lokacin da aka bashi Auren zahra da Rana
tsaka ya Kuma sa hannu biyu ya karba.
"Amin na gode ba komai, zahrar tace ma a gaisheku, kuma nazo ne nayi muku sallama
zanyi tafiya ne amma in Sha Allah bazan jima ba, na fadawa Abba a samu wadda zasu
zauna tare kafin Allah yasa na dawo".
"Masha Allah. Allah yayi taimako hakan baze gagara ba ko can gida Mubi Sai a samu
wadda zatazo su zauna tunda akwai yaran sosai ba sai an dauko bare ba tunda yau din
ta Zama wata iri Amma kafin tazo sai su Fara Zama da zulai tunda Bata da matsala"
"Godiya muke Allah ya kara sutura" Habib ya fada, suna mikewa har lokacin Autan
Ammah Yana jikin Mahmud a zaune. Addu'a Ammah take musu har suka fito Nan da nan
wani rauni ya shigi Mahmud haka tasa Umman take Masa a duk lokacin da ze shiga
wurinta bakinta baya gajiyawa da Yi Masa addu'a, duk kewarta sai ta rufe shi,
"kaimu gurin Mama mu gaisa".
Mahmud ya cewa autan Ammah.
Part din Mamar suka nufa, Musaddiq ne yayi knocking har sau biyu ba'a bude ba Kuma
suna jiyo maganganu da sound din tv.
Habib ne yace "mu tafi Dan Allah yaushe zamu tsaya kamar wasu 'yan maula". Har sun
sauka daga steps din balcony din sannan aka bude kofar, Asabe ce ganin Autan Ammah
da mutane yasa ta fito tana fadin ku shigo Dan Allah wlh bamuji ba sai daga baya
Salma ke fadin Kamar taji bugun kofa".
Habib ne yayi farat yayi magana "ai ba komai a gaishe da Hajiyar Daman mujin Zahra
ne ya shigo ya gaishe ta".
Sukayi gaba suka barta a tsaye.
Ciki ta koma jiki ba kwari.
Mama ce ta kalleta.
"Wai su waye Naga kin fita Kuna magana dasu ne Kuma Basu shigo ba?"
Zama tayi kusa da mamar, "sirikin ku ne inda mukaje basa Nan yazo gaishe ki da
alama Kuma sauri suke tunda sun jima a tsaye ba'a bude ba".
"Wai kina nufin Mahmud mijin Zahra?"
"Shifa sunce a gaishe ki, da alama sauri suke Dan har sun fice.
Baki Salma ta tab'e tana fadin. "saura kiris dai uban kowa ma ya rasa, ba dai kunce
kun Kai turaren wutar ba, yanda aka wayi gari aka ganshi da hakoransa talatin da
shida haka za'a wayi gari yayi layar zana inga ta qafafar da ake anyi aure, auren
ma Dan jeka nayi ka da ba wani armashi yayi ba, Shima Abba Dan ya ganshi handsome
ne ya bashi ai ko banza ance mijin agolar gidansa ne".
Dakuwa Mama tayo Mata "Abban naki kike fadawa haka? Nima da farko nayi tunanin ko
wani lashi yaga yaron Yana dashi sai da na saka akayi min bincike aka tabbatar min
da gidan da kayan da yake sakawa duk Wanda yakewa aiki ne suka kawo Masa Dan wasu
ma ance min wannan yaron shugaban aikin nasu ne ya kawo Masa kwancensu Dan ya rinka
fita kunya tunda matar tasa 'yar boko ce, shi Kuma almajiran soro ance min ma
iyakarsa secondary ya Dan iya rubutu da karatu ne yasa suka dauke shi aikin nasu,
har kike wani zaqewa kina sonsa ai da naji haka saina fad'i ba nauyi yo Dan kyau me
ake da kyau bako sisi Allah Banda nayi Alkawarin saina Maida Zahra karamar bazawara
ba, da barinsa zanyi a garin to idan nayi wannan saken kakanninta zasu iya bashi
mahaukatan kudi ya nemi sana'ar da ze rike musu jika gara dai yayi gaba tazo ta
zauna na Dora daga inda na tsaya".
Dariya Salma da Asabe suka kwasa Asaben ce ke fadar "Aikinki Yana kyau uwar dakina
ba Wanda ze taba hasaso hakan daga bangaren ki kin kasa kin tsare duk wata kafa da
wani ze fahimci da saka hannunki a lamarin yarinyar nan".
Dariya mamar tayi itama "Au da sokike na ringa nuna adawata a fill ai Ni duk ranar
da tazo gidan Nan da bayanin mijin ya gudu sai nafi kowa kuka da tsine masa".
"Sai Maman mu". Salma ta fada tana kyalkyalewa da dariyar mugunta.

*********

A harabar gidan suka samu Abba Yana yiwa malam Bala direba magana, gurin suka nufa
Abban na ganinsu ya nufo inda suke.
"Har kun fito"
"Eh Abba zamu koma"
Suka fada tare, takarda Abban ya mikowa Mahmud.
Hannu yasa ya karba.
"Gashi Nan ka Kara guzuri Allah ya kaiku lfy ya bada sa'a".
Godiya sukayi Masa sosai har Saida yayi fada.
Tare suka fita da Auta har gurin mota ledoji biyu Mahmud ya dauko daga seat din
baya ya mikawa Musaddiq.
"Gashi naka daya na Faruq daya tukwaicin ku ne na kawo abinci".
Da murna Auta ya nufi gida Yana fadin "mun gode Uncle".
Cheque din kudi ne masu nauyi Abban ya bawa Mahmud saida abun ya Basu matukar
mamaki.
Habib ya mikawa cheque din Yana fadin.
"Ka rike a gurinka kawai a sawo kayan shagon Nan dasu a Fara kasuwar tunda Allah ya
kawo kawai".
"A'a baza'a yi haka ba ka tafi dasu kayi guzurin Kamar yanda yace idan Allah yasa
kun dawo sai asan yanda za'ayin".

"Kayi yanda nace ba wata damuwa acan komai Yi Mana za'ayi to me zanyi dasu? ga Kuma
abun bukata a gida ba gara ayi ba watakila kafin mu dawo ka koma sari na biyu".
Ya fada Yana murmushi.
Majalissar su sukaje Mahmud yayi musu sallama har salisu Yana zolayarsa akan barin
Zahra da zeyi Yana tsakiyar angwancewa. Bai Dade ba ya tafi duk hanlalinsa Yana
kanta yasan har ta gaji da jiransa watakila ma tayi barci.
Saida ya biya ya saya musu kaza da apple ya dauki hanya.
Lokacin Sha daya da minti ashirin da bakwai.
A hankali ya bude dakin abin mamaki Zahrar ya gani gurin fridge da glass cup a
Hannunta tana Shan wani abu, Sam bataji bude kofar ba saboda tv a kunne take sannan
ta bawa kofar baya, Jin kamshin turarensa yasa tayi saurin juyowa lokacin yazo daf
da bayanta, juyowar da tayi sai a cikin kirjinsa.
Ledar ya saki qasa yayi Mata kyakykyawan masauki ya saka hannunsa ya talkafo bayan
ta, yasa Bakinsa a dai-dai kunnanta.
"Na dauka kin wuce Kano a barcinki Ashe dai jaruma na aura wadda take iya jiran
mijinta komai dare". Ya karasa fada Yana Dan hura Mata iskar Bakinsa a kunnen.
"Dan Allah ka Bari".
Ta fada tana niyyar janye jikinta shi Kuma ya Hana hakan. Dan kwabe fuska tayi, "ka
sakeni toilet zani".
"Ba wani toilet idan Kuma da gaske ne muje na rakaki".
Kai ta gigiza, shafa gefen ribs dinta yayi yaji yanda rigar ta matseta komai yayi
tsan-tsan. Dan sakinta yayi Yana Kare mata kallo daga sama har kasa, Dan sunan
dinkin a tsokano fitina kawai, shi a dazu ai be karewa dinkin kallo ba sai yanzu a
kausashe ya jefa Mata tambayar.
"Waye telan da yake Miki dinki".
Hannu yasa ba zato ya shafo gaban rigar da sauri ta saka duka hannuwanta ta tsuguna
sai Kuma kasan ya baje. "Ya Salam" ya fada a hankali.
"Kinyi shiru Ina tambayarki".
"Makociyar Aunty Hasana ce take Mana dinki".
Ajiyar zuciya yayi yayi zaton namiji ne yaji ance sune ke gwada Mata idan hakan ta
kasance ai an gama dashi wani ya taba Masa wannan jikin. Tsugunawa yayi ya kamota
ya dago jikinsa ya maidata "ki barni naji duminki gobe ya wannan bana kusa dake Ina
can na rungumi pillow, so muje muyi hirar yaushe gamo, ko Kuma ban sani ba murna
kike kina Jin dadin Zan tafi na Baki space ki sake ko?"
Ya fada Yana Wasa da Dan Karamin zoben dake 'yar karamar yatsarta.
"Oya talk kinyi shiru koba haka bane daman ba kince min me naci Kamar maye na
tsotseki waya sani ko maye ne ni ko Baki fada ba? Kawai Dan na koyawa bakinki
ladabin magana da miji akan wannan yaron shine na samu lambar maita daga gurinki".
Sexy eyes dinta ta zaro Masa, abinda yake burgeshi yake matukar so kenan yaga ta
tsorata.
"Ni nace maka maye? Yaushe akayi hakan Wana fadawa?"
"Abar maganar kawai sai ranar Dana cinyeki danya Zaki gane Ni maye ne".
"Wlh Ni ban fada ba, Toni Wana na gani da Zan Fadi haka har a Gaya maka, a kwanakin
Nan ko waya ban rike ba fa".
"Naji shike Nan zo muje Naga aikin Allah yasa dai yayi kada aiki ya Koma baya"
Ledar tsarabarsa ya dauka ya jata suka nufi ciki. Gefen gadon ya zauna Yana janyo
laptop din gefensa Zahrar na tsaye a dayan gefen.
"Hayo ta Nan ki bude ki nuna min aikin in gani". Ba musu tayi yanda yace Kan
cinyarta ya Dora laptop din ya Dan kwanto jikinta yana ganin aikin har ta Gama nuna
Masa, tab'a hannu yayi Yana fadin "inye kice idan Allah ya hure mun na samu
sakatariya ta a gida basai na nema a waje ba, yanzu jeki saman fridge akwai plate
biyu ki dauko kizo ki Zuba wannan" ya nuna Mata ledar daya shigo da ita.
Laptop din ta aje kusa dashi ta janyo gyalen da ta yafo zata yafa ya karbe Yana
Mata wani kallo.
"Me zakiyi da shi ko akwai Wanda ba muharraminki ba a Nan da Zaki Kama rufe jiki,
ok da bana Nan kin aje har Dan kwalin kina watayawa yanzu Kuma na dawo Zaki wani
saka gyale tunda idan na ganki kin dauki zunubi ko?"
Shiru tayi Masa tasan idan ta magantu sai ta Kara laifi, juyawa tayi ta nufi kofa
ya bita da idon Yana kistima abubuwa da yawa a zuciyarsa.
Plates din ta dauko ta kawo ta koma ta dauko ruwa roba daya da fresh milk tunda
taga Kamar yafi son Shanta akan lemo.
"Dauki ki zuba" Nan ma ba musu ta bude kedar Naman wani kanshi ne ya doki hancinta
har lokacin Kuma da zafinta, daya ledar ta bude apple din ta Zuba a kai, gyara zama
yayi Yana nuna Mata gefen shi, Kaita girgaiza.
" Na koshi bana Jin yunwa".
"Naji ai ba abinci bane kizo kici ko nayi Miki dura da gaske nakeyi fa".
Narai narai tayi da ido, Allah bana cin Abu Mai yaji ko maiko da yawa da dare ulcer
yake tada min".
Ture plate din yayi gefe ya janyota ya zaunar da ita a cinyarsa.
"Me Kika ce? Ulcer as how Kika kamu da ulcer, since when?"
"Bafa wani Abu bane tun Ina secondary ne Amma tunda aka fada min na rage cin
wadannan abubuwan more especially da dare idan Zan kwanta saina daina ciwon cikin".
Plate din ya ture gefe, "tashi ki Kai fridge ki dawo".
Kallonsa tayi da alamar tambya "to Kai bazakaci ba"

"Ni saboda ke na sawo coffee ko fruit kawai nake Sha a irin wannan time din, ki
wanko Mana Apple kawai ya Isa".
Saida ta wanko ta kawo sannan ta dauki kazar ta Kai fridge din ta dawo.
A Dan nesa dashi ta zauna taga alamar 'ya abun nasa Yau suna kusa.
Matsowa yayi jikinta da plate din Apple din Yana Danna waya da alama kamar Kira
yakeyi Apple din ya Mika Mata Yana ci gaba da trying Kiran, sau biyu Yana Kira
ba'a daga ba ya hakura ya aje wayar.
"Labarin ki Zaki bani tun daga primary, secondary Zuwa Yau din Nan da muke tare
Kuma ki fada min dalilin da yasa ake fasa aurenki da dukkan Wanda sukaso aurenki
laifin na waye? Ok kafin Nan Bari na tambaye ki wani abu"
Wata wayar ya Ciro daga aljihun gefen hagu na rigarsa.
Jikinta ya matso sosai Kusan Rabin jikinsa Yana cikin nata ya kanainaye ta CCTV ya
kunna ya Mika Mata ya saka fullscreen gurin gate din gidansu ne Mama da Asabe ta
gani tun tsayuwar motarsu har zuwa gurin Mai gadi Saida ta gama ganin komai yace
"Daman Kuna abin kirki da Mama ne? Kuma wacece wannan Dan yanzu da Daren Nan da
naje yiwa su Ammah sallama naganta a dakin mamar kenan daga Nan can sukayi"
Ya fada Yana tsareta da idanunsa masu razana ta.
"A'a ni bana wani good term da Mama ko kadan Dan da sam ita da Aunty salma basa
yina Daman Hameeda ce tawa idan tana gurin ba Wanda ya Isa ya Fadi marar Dadi a
kaina, to ita dinma bansan meya canzata ba lokaci daya tayi min cin fuska ba ko
Kara gani a tsaye, ita Kuma wannan Asabe ce aminiyar Mama ce komai tare sukeyi".
"Ok ba damuwa".
Wayarsa ce ta dauki wani slow music alamar shine ringtone din wayar, dauka yayi
tare da sallama.
Magana ya Fara Bai jira Wanda yayiwa sallamar ya amsa ba.
"Kazo Azare katagum local government a cikin local government ne na Bauchi state ne
a duba map zakaga inda location din yake amma kada ka biyo ta jos Nissan yayi
yawa ka shigo ta Kano kawai karfe bakwan safe tayi maka a garin".
Abinda ya fada kenan ya katse Kiran.
Wani Kiran ya Karayi ringing daya aka dauka.
"Bilya a canzawa Mai gadin gidana gurin aiki ya Koma Sharar compound din makarantar
yaran Nan kawai" kit ya kashe Kiran duk tana binsa da ido.
Agogon jikin wayarsa ta kalla Sha biyu da Rabi.
A marairaice ta dube shi "yaushe zamu tafi nifa Ina Jin tsoron dare fa".
Kansa ya kwantar a cinyarta Yana facing din face dinta.
"A Nan zamu kwana bakiga harda jakar matafiya ba? jiranki nake ki bani labarin naki
kinyi shiru kin shareni".
Dan turo Baki tayi "Toni me zance maka ai kasan komai"
"Kamar Yaya nasan komai, harda labarin da aka turo min ta msm na duk Wanda kikayi
tare dashi Saida ya sanki 'ya mace yaji test din Bai Masa ba tunda kyawun iya jiki
da fuska kawai ya tsaya" shima Hakan ne tunda anfada min?"

"Cikin razana ta nuna kanta da hannu.


"Ni Kuma Zina? Waye yayi min irin wannan tozarcin? Me nayi musu haka da zafi da har
za'a yi min bita da kulli irin wannan?" Sai hawaye.
"Ya Ilahiy!! Ken wace iri ce daga tambaya sai kuka kewai kuka baya da wahala a
gurinki Kamar wata 'yar film, tab kice na iya bakina, idan na karanto Miki sauran
yau ma a Asibiti zamu waye kinga the chapter is closed labarin ma a bar shi Gama
Shan apple din ki kwanta Naga alamun barci a idonki Ni aiki Zan karasa".
Cikin shashhsheka tace "basai nayi komai ba tunda banzo da kaya ba haka ma zan iya
kwantawa".
Luggage din ya nuna Mata da Hannun. "Ki bude akwai komai a ciki ya janyo laptop
dinsa ya Fara aiki bai Kara bi ta Kanta ba, yayi biris da ita Kamar besan Allah
yayi ruwan tsirarta a dakin ba.
Nuku nukunta ta Gama sannan taje ta bude jakar kamar yanda ya fada kayansu ne ita
harda sleeping dress Kusan uku Saida ta duba sosai sannan ta samu wata doguwar Riga
Mai Dan dama dama ta dauka ta nufi toilet duk abinda take Yana kallonta ta gefen
ido har ta shige.

Ruwan zafi ta hada ta zuba turarikan wankan data gani a gurin ajiye, shigewa tayi
ciki tayi kwance ruwan Yana ratsata kamar zatayi barci ta jima sosai sannan tayi
wankan ta fito, sai da ta goge jikinta ta zura rigar barcin cotton ce mai laushi ta
sauko Mata har Kusan gwiwa sai da matsalar ta dayi zif akayi Mata har kasa ga saman
rigar wani net aka saka transparent komai a waje yake ba wani sirri Kai kawo da
dinga yi a toilet din daga karshe towel na wanka babba ta rufo a jikinta ta fito.
Dago ido yayi yana kallon ta sai Kuma ya janyesu yaci gaba da aikinsa cikin kware,
idan yaci gaba da kallonta wlh wata dariya zata kubce Masa, shi dai yasan duk wayon
Amarya sai an Sha manta.
A darare tazo ta zauna a nesa dashi.
" Ki tashi ki kwanta ya nuna Mata tsakiyar gadon. Jinjina Masa Kai tayi ta Haye
tana Jan blanket din tana rufe jikinta. Kusan Rabin hankalinsa Yana Kanta Yana
kallonta tayi Addu'ointa shafa a jiki, tun Tana Dan Jin dar a jikinta har barci
yayi awon gaba da ita.
Sai gurin daya ya kammala duk abinda ya kamata ace ya gama.
Wanka yayo tare da alwala pyjamas ya saka masu kalar off-white sannan ya tada
nafila raka'a hudu yayi ya sallame ya jima Yana addu'a kafin ya nufi gado dariya ta
bashi blanket din daban ita daban sai barcinta takeyi cikin nutsuwa face dinta ya
kurawa ido "yes she's beautiful" ya fada a hankali kamar Mai tsoron kada taji.
Kusa da ita ya kwanta kamshi turarensa Dana turaren wanka sai suka bada wani
kamshin Mai dadin shaka, madaurin jikin rigarsa ya since ya zare rigar daga jikinsa
ya kwanta a jikinta Bata ko motsa ba a hankali ya saka hannunsa ya zuge zif din
jikin rigarta yayi mamakin nauyin barcinta blanket din ya janyo ya lullubesu da shi
sannan a hankali ya mannata da jikinsa yana sakin ajiyar zuciya, a cikin barci taji
Kamar hannu na yawo a jikinta a Dan tsorace ta bude idonta ga dakin ba haske so
sai, Sam saita kasa gane takamaiamai a Ina take ga ta Kuma a jikin mutum ko Riga
Babu.
"Wayyo Allah na!!!" ta fada jikinta ya dauki rawa..
"Shittt, cool down nine kiyi barcinki Nima barcin nakeji..
.✨✨
✨✨

AUREN HUCE HAUSHI

Page 28

____Hankalin Zahra be kwanta ba sai da taji Yana maida numfashi a hankali


alamun barcin ya dauke shi ajiyar zuciya ta sauke da farko Bata yarda ba da yace
barci zasuyi Saida ta gani da gasken yayi barcin.
Kokarin zame kanta da yayi Mata pillow da gefen kafadarsa tayi, a cikin barcin
ya kara janyo ta jikinsa yana gyara Mata kwanciyar amman idonsa dai a rufe, shiru
tayi lif a jikinsa Dan Bata son ya farka su hada ido ai da kunya amma taga alama
shi bashi da ita misqalazarratin idan wani ne ai zuwa yanzu Basu wani sababa yanda
abun yazo musu a hagunce, ko dan shifa yana ikirarin ya santa batun yanzu ba to a
Ina?Kuma waye shi?daga Ina yake? Waye sameer a zahiri shi yaron sameer ne ita Kuma
a bad'ini shi yake bashi directive abin da daure Kai Kuma yace ya manta garinsu da
komai nasa Amma a gurinta yana fada Mata ya tuno kakarsa har da 'yar tsamar da
sukeyi.
Tunani barkatai ta dunga yi har barci yayi awon gaba da ita, karfe hudu da rabi
na Asuba alarm din daya saita ya tashe su kusan lokaci daya suka farka har lokacin
tana jikin shi, shiru tayi Bata nuna ta tashi ba, so take ya wuce toilet.
Addu'ar tashi daga barci yayi a hankali ya zare ta daga jikinsa kura Mata Ido
yayi a cikin dimligh din dakin face dinta sai glowing takeyi ko Ina a jikin fresh
sai wani sansanyan kanshi ke fita daga jikinta wanda har ya zauna a jikinta Dan duk
jikinsa kamshin yakeyi, light kiss ya Bata a kumatu ya gyara Mata rufar saboda
sanyin AC ga sanyin Asuba. Duk abinda yake tana jinsa bakam tayi Dan ji tayi wani
irin nauyinsa ya rufeta Wai wane irin barci ne tayi har yayi sabgar rabata da
rigarta amman Wai Bata sani ba, Jin karar ruwa yasa tayi saurin tashi ta janyo
rigarta tana cuno Baki.
"Haka kawai duk a kalleka waya sani ma ko Abu ya saka a cikin Apple din Dana
Sha shike Nan na Kama barcin asara sai yanda yayi Dani" da sauri ta ida janye
blanket din tana duba jikinta Jin ba wani bakon Abu yasa taji sanyi a cikin ranta,
sai Kuma abun ya Bata dariya, Jin ze fito yasa ta koma ta kwanta jallabiya ya zura
ya saka tashi ka fiye naci, ya dauki tasbasha (counter( ya matso kusa da ita Dan
guntun ruwan alwala na fuskarsa ya yarfa Mata kadan a fuskar ta.
"Ki tashi kiyi alwala an kusa tada sallah nasan idonki biyu tun lokacin Dana
tashi".
Ya fada Yana nufar kofa zuwa masallacin cikin hotel din.
Tashi tayi ta nufi toilet din a gurguje tayi wanka ta daro alwala lokacin data
fito har an idar da sallar, lotion din data gani ta shafa ta bude jakar duk wani
abun da zata bukata ya sako a ciki ita mamaki take to a Ina ya Sami kayan ita dai
ba nata ya dauka ba, hatta bra ma size dinta ce doguwar Riga ta cire daga leda ta
saka baka Mai aikin stone, hijab ta saka ta tada sallah.
Har ta gama azkar Bai shigo ba sai gurin shida da rabi ya shigo directly inda take
ya nufa.
"Barka da Asuba".
Zahra ta fada tana sadda Kai kasa, shiru yayi kamar Bai jita ba sake maiamaitawa
tayi.
"Taso kiga yanda ake gaida Dear ba irin wannan local gaisuwar ba"
Sunne Kai tayi tana Dan murmushi, tsugunawa yayin daf da ita yana kallon 'yan
yatsun Hannunta sumul sumul dasu kamar Bata aikin komai da Hannun, dagota yayi gaba
dayan ta ya mannata a jikinsa "ji nakeyi kamar kada nayi tafiyar nan ko Kuma na
daukeki mu tafi, idan na tuna zanyi nesa dake wlh wani irin rauni ne yake kamani
naji kamar idan bana Nan wani Abu ze faru".
Ya fada cikin muryar karaya da gaske a 'yan kwanakin Nan Yana Jin wani Abu daya
fi na da a tare dashi.
Cikin 'yar siririyar muryarta tace "ba komai kaje kawai Allah Yana tare damu ba
abun da ze faru sai abinda ya hukunta a kaina, Allah ya bada nasara yasa a Dace,
kawai dai Dan Allah kayi min wata alfarma kafin ka tafi".
Hijabin ya zare a hankali daga kanta ya Dora a Kan bed side kafin ya zaunar da ita
a jikinsa as usual.
"Fadi wace bukata gareki".
Dan shiru tayi kamar bazatayi magana ba.
Oya fell free with me, kiyi magana Mana kinsan eight thirty nake so na wuce".
"Daman so nake na ringa zuwa Dr.sulaimanu Adamu college of Hygiene inda nayi
service na ringa yin lectures ko sau biyu ne a sati".
Wani kallo yayi Mata na Amma Baki da lissafi.
"Ni matata da yawon aiki? Gaskiya A'a! Wannan bukatar Bata karbu ba, me kikeci na
baka na Zuba indai aiki ne wlh sai kin gaji da yinsa, tashi daga jikina kin wani
samu cinya kin dane,kada na makara nayi missing flight mu tsuguna duk dan burin
bawa ya rushe".
"Yanzu Allah bazaka Bari na rinka Zuwa ba".
Ta fada a marairaice.
"Kinsan Allah wlh Zan hadaki da zayyan Dan nasan Yana daf da shigowa garin Nan ya
juya min dake can kauye gurin Hajiya Inna ko banza kin tuka mata tuwon dawa kin
mata shara, kinga ita gaba ta kaita balarabiya na mata aikatau ita kuwa bakar fata
Kinga sai mu Dora a media muma 9ja munci gaba ana zuwa daga middle East ana Mana
aikatau".
Ya karasa fada Yana Jan Dan tsinin Karan hancinta.
Tana kokarin magana wayarsa dake Kan bedside ta dauki wani kidan larabawa Mai dadi.
"Dauko min wayata Dan tsabar na Zama mijin ......, Gashi Nan ringtone din ma kidan
kune na saka". Wayar ta dauko, Zayyan ta gani kwalalo idanu tayi Ashe da gaske yake
da yace Shi wannan din zezo yanzu ko waye shi kuma "oho" ta fada a zuciyarta.
Wayar ta Mika masa.
"Ka karaso?" Abinda taji ya fada kenan Bata San me yace Masa ba taji yace "ok, ka
shigo ciki akwai securities a kofa zasu zasu rakoka gurin da Zan ganka".
Ya kashe Kiran Yana nufar kofa, ki shirya kafin na dawo yanzu zamu wuce".
Yayi Gaga abinsa ya barta da Baki a sake "ikon Allah shi Kuma ko waye yake bada
umarni cikin dare ya wayi gari da abinda ya bukata tasan ko waye daga nesa yake Dan
jiya tanaji Yana fadin kada a biyo ta jos a biyo ta kano, ita duk ya Gama Dame Mata
lissafi wlh.
******
A hankali yake tafiyar cikin nutsuwa Amma da gani kasan tafiyar ta ingarman namiji
ce, tunda ya doso gurin Zayyan ya kafe shi da ido, take ya shiga jinjina lamarin
ogan nasa wato ana zaton wuta a maqera said gata a masaqa, waze tab'a tunanin sa a
irin nan yayi masifar bada kafa.
Bai Farga ya kureshi da ido ba Saida yazo daf dashi, "sorry sir" ya fada Yana sadda
kai, baiyi magana ba ya mika Masa hannu wannan d'abi'ar sa ce baka Masa irin
gaisawar Nan sai dai kuyi musabihwa. "Barka da Asuba ya Hanya?".
"Alhamdulillahi."
Ya fada sai da Mahmud ya zauna kafin Zayyan Shima ya koma ya zauna.
Kamar bazece komai ba gurin ya dauki shiru.
Saida yaja fasali sannan yace. "I hope ba Wanda ka fadawa munyi waya ga Kuma inda
zaka sameni?"
Kai ya girgaiza "ko daya oga ba Wanda yasan inda na tafi kawai nace musu zanje gida
ne na samu Kiran gaggawa".
"Good, na kiraka ne zaka zauna gidan da wife Dina take zanyi tafiya, Wanda na saka
gadin Naga alamar gaskiya Bata isheshi ba, ko Kuma ze iya komai saboda kudi, zan
turo maka pictures na wasu Mata koda Wasa kada kabar kafarsu ta shigar min gida
shi yasa na taso ka da tsohon dare ".
Zayyan jin magwnar yayi wani banbarakwai "wife Kuma? To ta ina Hakan ta faru?
mutumin da ake tunanin baya kasa sai Kuma ya ganshi a nan Yana wata irin rayuwa
hankalinsa kwance, ga abubuwan tambaya Amma ba Halin yinta.
"To in Sha Allah baza'a samu matsala ba".
"Yanzu zaka shiga cikin Ibrahim ze nuna maka dakin da zaka huta daga Nan zuwa sha
daya Binyaminu ze shigo kuje gidan".
Ya fada Yana mikewa.
Da kallo zayyan ya bishi har ya b'acewa ganinsa, ajiyar zuciya ya sauke Yana
jinjina Lamarin ogan nasu wato duk yanda kasan Shi idan yayi wata bada Qafar saika
rasa gane wace alkiblar ya kalla. "Wife Dina". Yanda yayi maganar kasan ba wasa
cikin Yana wannan tunanin Ibrahim ya karaso Bai sani ba.
Da azama ya shiga falon a zaune ya sameta da luggage dinsa a kusa da ita tayi
rolling da Veil din rigar sai tayi masa wani irin kyau, a slow ya karasa inda take
zaune ya saka hannu ya dagota tsaye ya sumbaci saman goshinta.
"Nayi Miki irin gaisawar ku, Ina key din lokaci Yana ja kada da gaske nayi sakaci
kija Mana, muna lallabawa, kin hakura da Zuwa makarantar naji Baki ce komai ba?"
"Bani da say, sai yanda kace haka za'ayi".

"Nace A'a! in dai Ina raye da lafiya ta bazaki nemi komai ki rasa ba Koda kuwa
faskare zanyi to zanyi na samu abinda zankula dake".ya fada Yana daukar luggage din
ita Kuma ta nufi kan fridge inda ya ajiye key din jiya.
A jere suke tafiya sunyi wani irin dacewa wadda dole idan ka kallesu ka qara suna
kokarin fita daga reception su Zayyan suna kokarin shiga, Mahmud ya kalla da jakar
matafiya a hannu Yana rike da Hannun Zahra,.
"Kam bala'i"
Yaji Bakinsa ya subuce ya fada Yana matsawa baya Kamar yanda Ibrahim yayi.
"A sauka lfy" Ibrahim din ya fada shi kuwa Zayyan kamar an saka makulli an datse
Masa baki.
"Ka bashi key din dakin ka biyoni mota Zan baka sako".
Ya fada Yana duban Ibrahim, mota Zahra ta shige ta barsu suna tattaunawa kafin ya
shigo ya tada motar ya nufi get din fita har yabar harabar hotel din, Zayyan na
lekensa ta window sai dai yasan idan yayi magqnar Nan da wani kwabarsa ce zatayi
ruwa daya fesa labari, oga da rije jikar mace uwa uba yana tukata da kansa Kai
wannan abin surprised da yawa yake"Ga bikin zuwa ne babu zani.

Tafiya yake da hanzari Dan ma safiya ce sosai titin ba yawan jama'a cikin Kan kanin
lokaci suka shigo unguwar, Horn ya danna da karfi da gudu Mai gadin yazo ya bude
yana fadin "barka da zuwa!"
Da gudu ya Koma ya dauko sakon dasu mama suka kawo jiya Yana fadin "barka da Asuba
yallabai gashi jiya bayan futarku su Hajiya Babba sukazo suka bada a ajewa Hajiya".
Ya fad'a Yana risinawa Yana mikawa Mahmud ledar.
Saida ya karewa shi da ledar kallo, sannan ya hade gabas da yamma yace ka rika idan
kana so, Kuma
Ka hade kayanka in anjima kadan binyaminu ze zo da Wanda ze canjeka aikin Nan
adalci daya nayi maka ban koreka ba zaka koma share-sharen makarantar Yara kawai".
Jiki na tsuma Mai gadi ya durgusa Yana fadin "Yallabai me nayi haka da zafi Dan
Allah kayi hakuri wlh baza'a qara ba ka rufa min asiri".
"Iya Alfarmar kenan bana korar ma'aikaci sai lefinsa ya Kai uku to Kai daya kayi ba
tare da kasan laifi bane shi yasa nayi maka uzuri bazan rabaka da rufin asirinka ba
dauki kaje yanzu Zan fito". Jiki ba kwari ya dauki ledar ya juya Yana ta faman
tunanin ta ina ya kuskuro yallabai jiya lafiya kalau suka rabu yau Kuma ya tashi da
canjin gurin aiki da Allah ma ya dube shi da Rahama daba Kora bace days shiga uku.
Suna shiga Mahmud yayi bed room dinsa ita Kuma ta nufi kitchen ta Fara hada abu
marar wahala coffee ta dafa Masa sai sandwich kawai tayi shaf-shaf a tray ta Dora
direct bedroom dinsa ta nufa ya fito daga wanka Yana goge jikinsa a ranta tace shi
baya mura any time wanka kamar dangin kwadi.
Sallamar ta ya amsa Yana aje towel din dake hannunsa.
"Ke! Me kikayi daga zuwan mu ba dai abinci bane ko? Ni bana cin komai a irin wannan
lokacin".
Langabe Kai tayi tana dubansa kasa-kasa har Zuwa lokacin wani nauyinsa takeji. Yana
ankare da ita.
"Coffee ne fa da sandwich nayi maka Dan Allah kada ka tafi da yunwa,alhalin gani a
tare da Kai ai da naji kunya daga zuwa ka nemi abinci a kanon".
"Inye ashe dai ana son mamudan?".
Ya fada yana nufar inda ya aje kayan da ze saka kananun Kaya ne na kamfanin Armani
ya saka bako kunya ya cire rigar wankan ya tsaya daga shi sai boxer short, da sauri
ta runtse idonta Dan Bata zata zeyi irin wannan abunba Yana kallonta ya basar yaci
gaba da shiryawarsa, Zama yayi Kan sofa Yana umartarta ta kawo masa coffee din nan
duka ta dauko ta aje gefensa ya dauka Yana sipping Yana kallonta tana Wasa da gefen
veil dinta da ya sauko, sandwich din daya yaci ya yaji ya isheshi Shima Dan kada ya
watsa mata kasa a ido ne, amma Sam baya iya cin komai a irin wannan lokacin.
"Zauna muyi magana" ya fada Yana dubanta,.gefen sofar tayi niyyar Zama ya tikota
"Kinga gurin zamanki Nan ya dorata inda ya Saba..
"Zan tafi Baki San cikakken asalina ba, Zan fada Miki saboda sha'anin Rai da rayuwa
kona dawo ko ba na dawo ba, Ni haifaffan garin sokoto ne iyayena duka biyun sunan
Nan ni dangatan iyayena ne da kakata Hajiya Inna, suna Sona yanda Baki zato yanayin
rayuwa ne ya kawoni nan, duk family na ba Wanda na fadawa labarinki sai kakata ta
sanki a hoto tasan wasu labaranki, kota Allah ta kasance wannan dana Kira ya zauna
yayi min gadinki sunansa zayyan na fada Masa ke matata ce ze sadaki da Family na,
Dan Allah kiyi min Alkawarin duk rintsi bazaki juya min Bata ba, ki rike min aurena
da Kima da daraja, idan Allah yasa na dawo Zan fada Miki koni waye da duk abinda ya
shafeni na rayuwata Daman taki na sani ba sai kin fada min ba,
duk abinda kike bukata ki duba waccen lokar akwai kudi a ciki bangaren abinci Kuma
nabar komai a Hannun Habib, ga Kuma kudin da Sameer ya Baki ban Baki ba". Ya aje
mata su a akan cinyar ta.
Jin tayi shiru yasa ya dago fuakarta da hannunsa,kukan Zuci take ba wani sound sai
dai hawaye"subhanallahi kuka dai? Kona fasa tafiyar nan kawai tunda Naga hankalinki
yaki kwanciya da ita"
"Ba komai kaje kawai naji Kanata nanata maganar in baka dawo ba na sani ko idan ka
tafi bazaka dawon ba".
Lakuce Mata Baki yayi "ai kece bazan dawo din ba, wannan ya shafa cikinta sai kin
ajiye Mana babies a ciki idan naki dawowa aini nayiwa kaina, ki kwantar da hankalin
ki nema zani ki min addu'ar samun nasara".

✨✨✨
✨✨✨

AUREN HUCE HAUSHI

Strory
&
Written
By
Maman Fateemah

Page 29

_____ Sun jima a haka Yana lallashinta kafin ya dagota su tashi tsaye tare " me
za'a bani nayi guzuri dashi?"
Ya tambaye ta, shiru tayi kafin ta Dan watsa hannu tana Dan kallonsa ta gefen ido.
"Ai kaga bamu kwana a gidan ba bare nayi maka wani Abu Saida idan biscuits din Nan
Zan dauko maka sai ka tafi dasu na bada a sawo min wani".
Dariya abin ya bashi ita bilhaqqi da gaske take fada Wai biscuits kamar wani yaro.
"A'a niba shi nake so ba tsarabar da zan rike Ina tunawa da ita har na dawo".
"Me Kenan?" Ta tambaye shi cikin nuna rashin sani.
Jikinta ya matso sosai ya riko ta Yana kallonta da wani yanayi mai wuyar fassarawa,
Bakinsa ya Kai Kan nata Dan bakin yasa Hannun ya talkafo kanta batayi zato ba
tsammani taji harshensa na yawo cikin bakinta ya lalubo nata harshen cikin gentle
yake tafiyar da ita ba kamar ranar nan ba, sun dauko Kusan minti biyar Yana Abu
daya ji tayi kafafunta na neman gagarar daukar ta, jin jikinta na rawa yasa ya Kara
mannata da jikinsa wani Nishi tayi ba Halin magana, kokarin yanye harshenta take
daga Bakinsa Kai ya girgaiza Mata sai da yayi mai isarsa ya saurara Mata Kan
gadonsa ta zube da gaske ya kashe Mata jiki ji take idan ta taka kafarta faduwa
zatayi.
Dan rankwafawa yayi saitin fuskar ta "Haba 'yan Mata be strong Mana me akayi da
maza inji karya, taso muje ki rakani idan na biye Miki labarin salo ze canza".
Ya kamo hannunta ya mikar da ita, jakar laptop dinsa kawai taga ya dauka, gyalenta
wanda yake yashe a kasa ya tsuguna ya dauko Mata Yana rufa Mata a kanta.
"Zaki bani Aron motar ki naje Kano da ita? amma fa saina dawo na dawo Miki da ita a
airport Zan bada ajiyarta yanda idan muka dawo saina karba kawai".
Kai ta gyada Masa alamar Eh.
*A'a magana zakiyi idan kin amince to idan Baki amince ba na nemi hanyar Tasha
kawai".
"Ka dauka kaje da itan koka dawo ma na bar maka za'a kawo min wata ba kaji Abba ya
fada ba".
"Ke! Kinsan kudin ta kuwa zakice kin barmin Dan ki hau Abba ya saya Miki, Aron ma
Ina laifi".
Yaja hannun ta suka nufi kofar a falo ya tsaya Yana wasu 'yan dube duben da Batasan
Kona menene ba sannan suka nufi harabar gidan, kasa hakuri tayi ta jefa Masa
tambayar.
"Wai haka zaka tafi ba kayan sakawa da takalma da sauran abun bukatu ne?" Dan shafa
gefen fuskar sa yayi ya Dan furzar da iska daga Bakinsa. "Bana tafiya da Kaya ai
wahala ce nasan duk inda zani akwai na sayarwa na saya kawai, aikin gane?"kallonsa
kawai batace Masa komai ba.
Saida yaje gurin Mai gadi ya bashi wata envelope sukayi maganganu sannan ya dawo
gurin da take tsaye.
"Zan tafi sai Allah ya dawo Dani, ki kula da kanki bana son yawo Amma idan gidan
Ammah ne ko Aunty Hasana idan Bata koma Jos ba kina iya Zuwa".
"To na gode, Allah ya tsare hanya ya bada sa'ar abinda akaje nema".
"Allahumma Amin. Allah ya tsare min ke daga sharrin mutum da Aljani da dukkan
abinda yake cutarwa, ya Ubangiji na bar maka amanar iyalina ka Zama gatan mu".
Ya fada yana nufar motar, a hankali ta biyo shi ya bude ze shiga ta riko hannunsa
ta Manna masa kiss a tsakiyar hannun. "Safe journey" ta fada da wata murya Mai
rauni da gudu ta juya idonta fal hawaye. Tsaye yayi Yana kallon ta har ta shige
ciki, ajiyar zuciya ya sauke kafin ya shiga ya tada motar jikin window ta tsaya har
Saida ya fice daga gidan.

________________________

Tunda Mahmud ya bar cikin gari ya saki motar, rabon da yayi tuqi irin wannan har ya
manta, kyakykyawar awa daya da minti arba'in da Tara ta kawo shi Kano, daga Hotoro
NNPC sai ya shiga ta ring road ya fita 'yan kaba haka ya dunga yayyankewa har Zuwa
round about na sani Baban kwari Sannan ya nufi Malam Aminu Kano international
airport,Yana daf da shiga gate din ya saka face mask da glass sannan ya shiga,
wayar Sameer ya Kira tana daf da katsewa ya daga.
"Kana Ina? Na shigo yanzu ina fatan komai ya dai-daita?". Dan Jim ya yi yana
sauraren sa. "Ok kazo ina parking lot inda ake bada ajiyar motoci".
Ya sauke wayar Yana kalon masu Kai da kawowa.
Yana Nan tsaye har sameer din ya karaso ya gaishe da Mahmud cikin girmamawa, jakar
laptop din Sameer ya karba da key din motar ya nufi inda suke da alhakin karbar
ajiyar, shi Kuma Mahmud ya nufi reception din.
Sameer Bai jima ba ya dawo da takarda shedar bada ajiya, sun Dan tattauna kafin
lokacin tashinsu yayi, zasu shiga screening ne Mahmud ya Kira wayar zahra, tana
kwance a gado rungume da pillow bayan tayi kukanta Mai isarta ta lallashi kanta
tunda Babu Mai lallashin gani takeyi shima kamar ya tafi kenan. Ringing din waya
taji da sauri ta tashi Dan ita Sam tama manta da wata waya tunda ya Bata Bata
karabi takanta ba, da sauri ta dauko tana duba waye ya Kira MM DANGE ta gani wani
sanyi taji ya saukar mata,
Picking tayi tare da sallama, sai kuma tayi shiru.
"Zamu tafi ne nace bari na kira na fada Miki, ko zamu sake waya ze iya kaiwa jibi
kada hankalinki ya tashi idan komai ya dai-daita Zan kiraki in Sha Allah".
"Tom Allah ya saukeku lfy".
"Allahumma Amin my precious, please take care bye".
Ya katse Kiran yasan idan yaci gaba kuka zata saka Masa ya rasa wane irin idanu
gareta masu saurin kuka.
Sha biyu da rabi jirginsu na kamfanin air Max ya daga.

Wayar tabi da kallo kafin ta aje kusa da ita, sai Kuma ta tashi kamar wadda aka
zabura. Wayar ta dauko dubawa tayi wata baguwar number ta gani batayi kasa a gwiwa
ba tabi Kiran Dan missed call ne tunna jiya. Cikin kankanin lokaci Kiran ya shiga
Bata jima Tana ringing ba aka daga muryar matashiyar macece daga ji tana ji da
ajinta sallama Zahra tayi Mata suka gaisa sannan zahrar tace Mata taga missed call
dinta ne a wayar ta.
"Missed call Dina gaskiya bani na Kira ba Amma Dan Allah wacece ke?.
Yar dariya Zahra tayi kafin tace "sunana Fatima Zahra Muhd sani Ni mazauniyar Azare
ce ta jihar Bauchi".
Kit ta kashe wayar ta yunkura ta tashi, ta nufi kofa tana daf da fita taji wayar ta
Kara daukar Kara ta dawo number dazu ce yi tayi kamar zata share sai Kuma ta dauka
taji me zata fada Mata.
Sallama tayi daga can ta amsa sannan ta Dora da fadin "Dan Allah kiyi hakuri da
farko ban ganeki bane sai da Kika fada min sunan ki wlh nice na Kira bansan yanda
akayi banyi saving number din ba matar oga Mahmud ko?"
"Eh nice ke wacece?"
"Sunana Fateeha matar Sameer Babban yaron oga jiya ne ya bani number yace na kiraki
na gaisheka nayi Miki Allah Sanya Alkhairi sai Kuma ba'a daga ba, an Sha sauga
bamuzo mukaga daki ba gashi har sun wuce China, amma in sha Allah idan suka dawo
zamuzo indai ban haihu ba har lokacin"
"Nagode kwarai da gaske,Amma naji kince China ba UK zasu Fara Zuwa ba? To can din
zasu tunda kune masu tafiyar Amma na dauka da China zasu Fara tunda canne aka samu
matsala sai Kuma Dubai, kinsan ogan naki ne kamar computer yake baya gajiya da aiki
danma yayi wannan hutun Mai yawa sai Habibi ne yake wasu ayyukan".
"Hakane kam aiya huta yanzu sai a Dora daga inda aka tsaya".
"Ai gaskiya samun kamar oga Mahmud sai an tona".
Basu jima ba sukayi sallama. Ta Dade a zaune tana jujjuya hirar su da matar Sameer,
zamewa tayi ta kwanta tana duban sama a hankali ta furta. "Ubangji ga baiwar Mai
rauni ka jibinci lamarina Kasan ko waye ka hadani dashi ka Kuma sakamin nutsu a
tare dashi ban tabaji bana sonsa ba Amma lamarinsa Yana bani tsora na rasa alkiblar
daya duba, Allah ka Zama gata na ka jibinci dukkan lamurana Dan Isar Manzon Allah s
.a.w.w.

Tashi tayi ta fita dakin nasa ta koma dauko tray din da Takai Masa break fast, duk
wani Abu daya danganci kayan electronic sai ta kashe sannan ta fito tana gangarowa
daga steps din corridor ne taji door bell din tana Kara alamar anyi Baki, a Kan
dining table ta aje kayan ta gyara gyalenta ta nufi kofar.
Budewa tayi sai sukayi arba da zilai Mai aiki da 'yar jakar kayanta.
Cikin farin ciki Zahra ta karbi jikar kayan tana fadin "sannu da zuwa anti
zilai"..
Suka shige ciki murnar Zahra taki boyuwa itama zilan ba Karamin murna tayi ba
lokacin da Ammah ta fada Mata zata zo ta Taya Zahrar Zama. Nan suka shantake suna
Hira har Kusan karfe dayan Rana kafin Zahra ta raka zilai dayan dakin da ba cikinsa
take ba ta aje kayan ta.
Tambayar Zahra zilan tayi me zata dafa musu,
"Ki dafa komai na ni harna manta wlh ashe ko break banyi ba, ga sandwich can ki
dauka kada ya lalace, Zan shiga na Dan kwanta kafin karfe biyu"

"To Allah kaimu" zahra tace "Amin"harta fara tafiya zilan Kira sunan ta tsayawa
tayi har zilan ta karaso.
"Uwar dakina Naga kamar wani mutum mun gaisa dashi ko Mai gadi kuka canza". ,"Eh
Mai gidan ne ya canza shi wlh jiya lfy muka fita Amma yau muna dawowa ya sallame
shi, wani ya Kira ya zauna Dani kafin ya dawo.
"Wani Kuma daga Ina,?. "Nima ban san daga Ina yazo ba" Tab Allah kyauta ya kamata
asan asalinsa gaskiya zamanin ne yazo da wata irin rayuwa sai godiyar Allah".
"Wannan gaskiya ne". zahrar ta fad'a. Ita nufi bed room ita kuma zilan tana nufar
kitchen.

✨✨✨
✨✨✨

AUREN HUCE HAUSHI.

Story
&

Written
By

Maman Fateemah.

This page is deducte to the Family of late Alhaji Isah Musa bakin kasuwa
kazaure.

Innalilllahi wa Inna ilaihi raji'un! Ina Mika sakon jaje da ta'aziyya ga jama'ar
garin MAJIA TAURA LG bisa ibtila'in daya samesu na gobara Mai Muni sakamakon
faduwar tankar man petrol, Wanda yayi sanadiyyar rasa daruruwan rayuka Allah ya
jikan wadanda suka rasu,wadanda Kuma suke gadajen Asibiti Allah ya tashi kafadunsu
ya Basu lafiya yasa ya zamar musu kaffara ya kiyaye faruwar haka a gaba dan
darajar manzon Allah s.a.w.w

Page 30

_______Misalin karfe daya da rabi Mai a dai daita sahu ya sauke Asabe a bakin gate
din gidan Zahra Dan yauma Saida taje can kauyen jama'are gurin wani mutum da wata
kawarta ta tab'a fada mata shi, Nan ma ta karbo abubuwa Wanda za'a binna a gidan
Wanda har abada Mahmud baze kara waiwayo garin Azare ba ko sunan jihar Bauchi ma
Sai yaji ya tsane shi.
Cikin karfin gwiwa ta karaso bayan ta sallami Mai Dan sahun tunda tasan Mai gadin
Dan hannu ne dubu biyu ta Isa tasa yayi musu kowa ne irin aiki ne, iyakar ta tace
masa na tsarin gida ne ze binna Mata saboda yau da gobe.
Knocking tayi da Dan karfi tana mazurai ita ga uwar matar gida. Cikin takunsa na
kakkarfa ya bude kofar gate Dan da hanzari tayi baya Dan ji yayi Kamar ze bangaje
ta, kallo daya yayi Mata ya gane face din Dan hoton da oga ya nuna Masa yafi bada
mahimmanci akanta Dan ita ce suspect dinsa ta farko, yasan da ita za'a yi amfani
gurin isar da ko wane irin sako ne.
Da hargagi Zayyan ya tunkaro ta.
"Wa kike nema?"
Duk daburcewa tayi nan da Nan jikinta ya dauki rawa.
A'a Daman gurin matar gidan nazo munzo jiya ne basa Nan shine na dawo yau".
Ta fada tana rawar murya.
"Kama gabanki Nan ba wata mace a ciki gidan maza ne, idan Kuma Zaki shiga Bismillah
tsuntsu daga sama gasashshe, Dan muna da kudajen da basa haram akan duk Mai
tsautsayi, idan na Kara ganin giccinki a wurin Nan saina hadaki da karena yayi min
fata-fata dake, wuceeee min daga nan" yayo kanta,da gudu ta kwasa ko waiwaye babu.
"Stupid! Da gani wannan tsohuwar kwarkwar ce wlh Banda oga ya hana da kinci na jaki
banza wato kin samu oga a araha shine kuka Neman zaku masa shegantaka akan matarsa
ni na rasa yanda akayi ma oga ya Fado garin Nan,? Kuma har ya iya Zama a haka ba
wani damuwa, ko Dan meze dameshi Yana tare da wannan danyan gold din".
Ya fada Yana komawa bakin aikinsa Amma zuciyarsa fal tunanin abinda ogan nasa ya
sani game da wannan matan daya turo Masa hutunan su ya Kuma shata musu dogon layi.
Asabe Bata samu zarafin tsayawa ba Saida ta dangana da wani gurin me suyar kifi a
bakin titi shima gani tayi gurin da jama'a ko cimmata yayi za'a ceceta, gefe ta
koma tana mayar da numfashi sai lokacin ta dubi hanyar data fito ko Mai Kama dashi
Babu. Gefen wani dutse ta zauna tana tunanin to koba gidan da sukaje jiyan bane
tunda ba wannan basamuden suka tarar ba Amma daga Daren jiya Zuwa yau har lamarin
ya canza ita damuwarta daya shin sakon da suka bayar ya sameta ko kuma na jiyan ba
shine asalin Mai gadin ba yayi musu ta 'yan duniya ya barbe kayan da kudin ya wuce
nasa gurin.
Tashi tayi Kamar wadda aka tsikara ta dauki 'yar ledar data sawowa Mai gadin Dan
abun tohiyyar Baki sai Kuma labarin ya canza salo. Harta dauko wayar ta Sai ta
mayar idan tayi gigin fadawa Mama kwabarta zatayi ruwa Dan a yauma Saida Mana ta
karo kudi masu nauyi tace a bawa Mai gadin yanda duk abinda za'a saka shi yaji baze
iya gardama ba, to idan ta koma Mata da wannan labarin amshe kudin zatayi tasan
halinta kayan ta, data Bata naira dubu gara ta bawa Dan tsubbu dubu hamsin, Sam
Bata karuwa da ita saita wadannan hanyoyin idan ta aiketa tunda itace
amintacciyarta ta Nan takeyin nata duk rintsi bazata so ta rasa wannan mafakar ba
Dan Kusan da ita ta dogara gurin kwaramniyar yau da Kullum nata.

*******

Saida Zahra tayi barci Mai isarta sannan ta farka lokacin biyu har da minti ashirin
da hudu, da sauri ta Mike tana addu'ar tashi daga barci tayi mamaki ita fa gani
tayi kamar barcin minti goma Sha biyar tayi Ashe lokacin ya ja haka, alwala tayi
tazo ta Fara sallah bayan ta idar wayar ta da dauko Ummee ta Kira cikin shauki tun
dazu ta nemeta network din na garin ba kyau sai hakura tayi, Bata jima ba tana
ringing aka daga ba Ummeen bace wata ce ta daga tana ta yi Mata larabcin gargal ita
kuwa zahrar na language yafi kwarewa a Dan daburce tayi Mata bayini ta gane Ummeen
ta fita masallacin Annabi sallah tunda har lokacin suna Madina basu tafi ba Kuma a
yanda sukayi daga Saudi Arabia Nigeria zasuyo gurinta, sallama tayi wa matar ta
kashe.
Number sajida ta lalubo ta syprus tasan zata Sha mita tun ranar da sukayi ways da
wayar Amatu tayi Mata buyagi ta kashe Basu Kara waya ba, har tayi ringing ta katse
Bata dauka ba, Bata hakura ba wani Kiran ta karayi shima Yana daf da ze katse aka
daga.
"Haba bestie Ina ta kira kin shareni ko har yanzu fishin ne?"
Mai makon taji bestien sai muryar Fatima taji tana kwallawa Sajidar kira tana fadin
"ku taho ga Amarya Zahra! Zahra" ta kirata da karfi tana murna kamar zata tsaga
wayar, daya bayan daya suka dunga gaisawa suna ta korafin amarci Dadi ta Kama waya
ta rufe wato Bata so a shigar musu rayuwa ko? Hakuri ta Basu tare da fada musu tayi
missing din waccen wayar ne har sim din, sai daga karshe sajida ta karbi wayar.
"'yar duniya wato kinji dadin lamarin ko Kika wani shareni, ni yanzu ai yallabai
Mahmud ya fiki kirki kinsan ya kirani Kusan sau uku? Daman ko Baki kirani ba Zan
kiraki dazu wurin Sha daya ya kirani Wai na kiraki na lallasheki yayi tafiya ya
baroki kina kuka?".
Ya fada tana kunshe dariyar ta.
"Malama ki fito kiyi dariyar ki sosai kada ta kume Miki a ciki,da kike wani
kunsheta".
Dariyar tayi da gasken sai tayi Mai isarta tace. "Dan Allah bestie mekika bawa
wannan guy din Kinga yanda yayi masifar macewa a Kanki? Wlh har tausayi yake bani
Ni har mamaki nake idan ya kirani Yana min maganarki ranar Nan fa cewa yayi na
bashi labarin zamanki a Nan syprus din wlh nayi zaton da Wasa yaki tunda nasan ba
Karamin cajin kudi za'ayi ba. Amma haka na ware na rinka bashi labarin har na Gama
ko a jikinsa, yanzu Ina aka tsaya da fatan komai ya dai daita? Dan nafi son dai
dai lokacin ganawarmu muyi murna biyu graduation da naming ceremony".
"Wlh Zan kashe yaushe Kika zama haka Mai bin kwakwkwafin jama'a? to bazakiji ba an
fada Miki kowa ma irinki ne ai wlh ya Abdul Hakeem ya debo ruwan dafa kansa Dan
nasan Dan bawan Allah saiya rinqa guduwa daga gidan"
Wata irin dariya ta saki tana fadin "billahil Azeem gara wata wainar data wake
yarinya gyara zancen ki idan ana cin baure ba'a tona cikinsa Kuma idan ana sallah
ba'a magana".
"Wlh sharri zakiyi Masa Amma shi dai salihi ne".
"A inda salihai sukayi karanci ba".
"Mubar zance kawai tunda abun ya Zama haka".
Zahra ta fada tana cire hijabinta daga jikinta vest ce Fara Kal sai wando shima
fari ai pink din kananun flowers gashin tayi parking a tsakiyar Kan ta kashe da
band shima pink, sai fito baby sak.
Gyara kwanciya tayi, tayi ringinnine da wayar a kunnenta Hira sukaci gaba da sajida
yawanci duk akan auren zahrar ne. Sun dauki lokaci Mai Dan tsawo suna tattaunawa
akan bututuwa da dama kafin suyi sallama, ta nufi toilet wanka take son yi kafin ta
fita cin abinci.

********

Jirginsu Mahmud a Addis Ababa Bole international airport yayi landing, daki biyu
Sameer ya kama musu Nan kusa da airport din tunda a kalla zasuyi Kusan three hours.
Saida ya kaiwa Mahmud jakar laptop dinsa sannan ya nufi nasa dakin, bayan fitar
Sameer Mahmud wanka yayi sannan yayi sallah maimakon ya kwanta ya Dan huta sai
kawai ya bude wayarsa so yake ya ganta duk wani matsi da yayi tana manne da
zuciyarsa so yake ya ganta kafin ya kirata. CCTV ya shiga ta wayarsa duk abinda
akeyi ya rinka bi Yana gani yasha dariyar karon Zayyan da wannan matar wadda ko
sunanta Bai sani ba, shi yasa ya dauko shi yasan shi kadai ne cikin amuntattunsa
Wanda ze Masa wanna aikin ba tare da an samu matsala ba.
Saida ya gama kallon ko ina na gidan yaga ba wata matsala, sannan yayi zooming din
cikin bed room dinta daga ita sai vest purple da wando skintight kanta tayi parking
da purple din band sai tayi wani irin kyau na musamman, kura Mata ido yayi Kamar ya
warto ta yakeji, turare ta dauko tana fesawa a jikinta. Nan ya shiriri ce Yana
kallonta knocking din da akayi Masa ya katse Masa abinda yakeyi, umarni ya bada a
shigo Sameer ne sai ma'aikaciyar hotel din dauke da tray na abinci sai karairaya
take shi har dariya abin nata ya bashi, me Kamar zahra yaushe irin wadannan zasu
burge shi, bayan ta wuce ne ya dago ya dubi Sameer "kada ka qara zuwar min da irin
wannan a rinqa bawa maza suna kawo min kawai".
"Noted sir"
Ledar dake hannunsa ya Mika Masa Mai tambarin wani boutique ne, sannan ya aje
Laptop dinsa a kusa dashi Yana nuna masa wasu ayyukan da ya Gama yanzu, sun jima
suna aikin kafin sameer ya fita saboda lokacin tashinsu ya kusa cika shi kuma
Mahmud ya ciro kayan da nufin sakawa.

Saida Zahra ta Gama feffesa turarenta sannan ta dauko after dress ta zura ta yane
kanta da gyalen sannan ta nufo parlour, zalai ta samu tana 'yan goge goge duk da ba
wani datti a gurin, gaishe da zilan tayi tana Mata sannu, ajiye mofar tayi "Allah
ya taimaki uwar dakina ga abincin can nayi Miki abinda kikeso faten dankalin turawa
da pepper soup din kifi"
Zama Zahra tayi tana fadin "Kai Amma wlh na gode kwarai da gaske shi yasa nake
yinki kinsa favorite Dina wlh".
"Ai shi yasa na cewa Ammah kada a wani dauko yarinya tun daga Mubi Nima na isa na
zauna dake saina kirawo Kanwata Alawiyya ta cigaba da yiwa Ammar kafin Allah yasa
yallaban ya dawo, ai ni har zaman wanka ni zanyi Miki Koda kuwa bakwa garin Nan
ne".
Dan smile tayi kawai bata ce komai ba saima ta canza akalar zancen.
"Ni Kuma Aunty zilai kin mikawa mutumin Nan abinci kuwa?".
"Ai tunda na Gama na zuba na hada harda ruwa da lemo na mika Masa. Naga Dan gayu ne
beyi kalar masu gadi ba".
Dariya zahra tayi tana fadin "Aunty zilai kenan shi Mai gadi har Kama gareshi".
Yana da kama Mana Wai Kinga wannan din?"
Na ga wani dai dazu ban sani ko shine Wanda aka Kira jiya cikin dare".
" Cikin dare Kuma?"
Kai ta gyada "Mata kusan Hakan tunda Sha biyu ta wuce ya kirawo wani kawai umarni
ya bashi yazo garin Nan da safe kinsan bakwai a Nan tayi mass nifa mutumin Nan wlh
tsoro yake bani na kasa gane kansa".
Dan murmushi zilan tayi tana kallon Zahra "kiyi hakuri uwar dakina a hankali Zaki
San komai a kansa badai Kuna tare ba da sannu Zaki gane shi din waye, kici abincin
sai muci gaba da hirar idan kin gwma".
Bata k'i Shawarar zilan ba ta tashi ta nufi dining ita Kuma zilan ta nufi dauko
Mata ruwa da mutuniyarta farm fresh, sai da ta Gama cin abincin sannan ta dawo
parlourn gurin da tabar Aunty zilan sukaci gaba da hirar su, amma Kusan hankalin
Zahra yana Kan Mahmud haka Nan sai taji ya fado Mata ta yarda da ake cewa sabo
turken Wawa, yanzu da baya Nan sai taji duk kewarsa ta kamata, tun dazu take duba
waya ko zataga kiransa Amma shiru tasan tsakanin Nigeria da inda zasu indai da
gaske chinan zasu da nisa a kalla jirgin zeyi landing a Ethiopia da India yaci ace
ya kirata Amma shiru har Yanzu ko lfy? ta ayyana a cikin zuciyar ta.
Ganin tunanin Zahra yayi zurfi yasa zilan ta tashi tana fadin Bari nayi wanke wanke
tunda kin Gama da kwanukan"
Tayi hanyar kitchen, ita kuma ganin tunanin ze dameta yasa ta kunna tv ta kamo MBC
MAX tana son finafinan su sosai,Aunty zilan ma data Gama Zama tayi sukaci gaba da
hirar jefi jefi har aka Kira magariba suka shiga sallah. Tana addu'oin yaumiyya na
cikin du'aul mustajaba ne kira ya shigo wayarta da sauri ta dauko tana duba Mai
Kiran Ummee ta gani da sauri ta daga tana fadin "Ummeena"
Amsawa tayi suka gaisa Ummeen ke fadar an fada Mata ta kirane nan tayi Mata fadan
rufe layi da tayi,nan Zahra taji kuka yazo Mata, Nan da Nan Ummeen ta rude tana
tambayar ta ko tana da damuwa ne ta fada Mata cikin kukan tace "Ummee Shima fa
wannan daga kawo ni gidansa ko sati daya ban rufa ba ya tafi ya barni Wai aiki
zejeyi uk" shiru Ummee tayi kafin ta shiga rarrashinta da kalamai na kwantar da
hankali da nuna Mata ba lallai ne hasashenta ya kasance gaskiya ba, kada ta damu
saboda ita har Umara tayi bayan auren tayi mata addu'oin samun nasara akan dukkan
lamuranta, sannan ta yi mata fadan ta kiyayi yawan kukan Nan bashi da ma"ana, daga
karshe tayi Mata albishir zawan su next week harda Mama Hanifa da Aunty Nawwara
duk suna hanya Daman ko Bata sameta a waya ba zata kira Hajiya Asma'u tasa a fada
Mata. Murna ta shigayi Kamar tayi me har Ummee na Mata dariya Nan da Nan ta ware ta
shiga lissafo abinda takeso Wanda za"a taho Mata dashi.
Bayan maga wayarsu da Ummeen Ammah ta Kara kira lokacin tana tare da Abba.
Tana zubawa Abba Dan fruit salad wayar ta dauki ringing Abban ne ya dauko ya duba
'yar dariya yayi Yana mikawa Ammar wayar tare da fadin.
"Uwata ce ke kira". Ganin Kiran ze yanke yasa Abban karbar fruit salad din yaci
gaba da zubawa Yana fadin "A dauki Kiran uwata kada ya yanke".
Daukar tayi tana amsa sallamarta da gaisuwar da take mata.
"Ammah yanzu Dan Allah bazakizo ba Kuma Aunty Hasana ma fa batazo ba fa Kuma Ni
sonake na ganki".
"Ikon Allah yanzu ke saboda Allah sai a ganni a gidanki a irin wannan kwanakin ai
sai a dauka ba lafiya Auntyn taku dai zatazo Daman jiya take fad'a zata shigo ta
ganki tunda mijin naki baya Nan, ai Mahmud din ma ya turowa Abban ku da sako ba
dadewa ta whatapp yace sun sauka lafiya, ke dai abinda nakeso ki kwantar da kiyi
Masa biyyayya kinji".
Ta fad'a tana rarrashinta.
"To Ammah, daman kira nayi na fada Miki Ummee tace next week zasu shigo Nigeria
nasan zata fada Miki".
"To Allah ya kaimu Daman munyi maganar shekaran jiya har take tambayar meya faru da
taki wayar? Nace ta Dan samu matsala ne, ga Abbanku yace a gaishe ki"
"Lah! Ammah Daman yana Nan amma ba'a fada min ba Bashi na gaishe shi"
Sun gaisa da Abban har Yana Dan tsokanar ta, tunda a wani bangaren kakace a
gurinsa, Nan yake fada Mata mijinta yace ya tafi da motarta Kano tana airport Dan
haka daga nan Zuwa jibi za'a kawo Mata daya motar ta gurin Muttaka, godiya ta yiwa
Abban sannan sukayi sallama.
Ta jima Bata aje wayar ba, tana juya maganarsu da Ammah Wai ya fadawa Abba sun
sauka wato ita da bayaso Bata da matsayin da ze kirata ko sako ya fada Mata sun
sauka, kenan Daman duk abinda yake Mata a 'yan kwanakin Nan yaudara ce Dan ya lasa
Mata Zuma a baki ya gudu ya barta da kewarsa inda ta godewa Allah be lalata mata
rayuwa ta gudu ya barta ba wlh duk rintsi sai ta bar Kasar Nan ta koma Jordan, Dan
tasan Allah kadai yasan halin da Ammah zata shiga idan bawan Allahn Nan yaqi
dawowa....

✨✨✨
✨✨✨

AUREN HUCE HAUSHI.

✨✨✨
✨✨✨

Story
&
Written
by
Naman Fateemah.

page 31

______________Har aka Fara Kiran sallar insha'i tana zaune tana faman tunanin
makomarta, tashi tayi tayi sallah, nan Kan sallayar ta kwanta tana lazimi a haka
har barci yayi awon gaba da ita.
Tun zilai na saka ran fitowa Zahra har ta hakura ta shige ciki duk da ba barci take
ji ba, tun yamma take ganin zahrar wani sukuku Kamar marar lfy.
Zahra ba ita ta farka ba sai Kusan daya da kwata, tashi tayi tana mik'a tare da
salatin Annabi, duk jikinta ciwo yake Mata hijabin ta cire tare da after dress din
ya Zama daga ita sai vest da wandon toilet ta shiga Bata Dade ba ta fito canja
kayan jikinta tayi da rigar barci ta Kashe wutar Mai haske ta kunna bed side camp
tayi shiru tana istigifari ga Allah s.w.a da Salati ga fiyayyan halitta Annabin
Rahama duk yanda tunani yaso ya bijiro Mata saida ta kawar dashi kawai ta fawwalawa
Allah lamarinta tasan duk rintsi Yana tare da ita, a haka har barci yaci karfinta.
Da safe har zulai ta Gama share share da mofin Zahra bata fito ba ganin shirun tayi
yawa yasa tayi tunanin buga Mata kofa kada ta Zama babbar banza zuwanta ya Zama
marar amfani rabonta da yarinyar nan tun magaribar jiya Bata Kara sakata a idonta
ba, kofar bedroom din ta nufa tayi knocking taji shiru lokacin Zahra na Wanka, Kara
bugawa tayi still dai shiru taji Nan da Nan hankalinta ya tashi kada fa wani abu
ya Sami yarinyar Nan ta shiga uku.
Tana Nan tana shawarwarin ta bude ta gani ko lafiya? taji alamun motsin tafiya daga
ciki da sauri ta Kara knocking din, Zahra da towel a jikinta ta nufo kofar ta bude.
"A'a Aunty zilai kece? Ina kwana?"
Ta fada tana goge gashinta daya jike gurin wanka.
"Lafiya kalau, naji ki shiru ne tun daga shiga sallah jiya harna gaji da zama Baki
fito ba, gashi yanzu ma naji shiru har Ina kokarin Kiran Ammah na sani koba lfy
ba".
Ta fada tana kokarin barin gurin "na gode da kulawar ki Aunty zilai wlh jiya barci
ne ya daukeni a nan Kan sallaya bani na farka ba sai Kusan karfe biyu na dare".
"Ikon Allah kice kwanan kasa kikayi da sanyin tayis Bai Kama ki ba, tunda Naga
gidan naku ko Ina sanyi Kamar gidajen larabawa".
Sai Kuma ta rufe bakinta da hannu.
"Kin jini ba wlh na manta Ashe gidan nasu ne".
Dariya Zahra tayi "Kayya Ina wani balarabiya anan ai da uba ake ado Ni bafulatana
ce kalarce dai na dauko tasu Amma idan masu abun suna yarawa wani abun sai kallo
Dan ma Allah ya hadani da jarimin uba da yayi tsayin daka gurin ganin na iya yaren
saboda na samu saukin mu'amala da dangin Mamana".
"Wannan gaskiya ne Allah ya sakawa Alhaji da Alkhairi ya biya Masa bukatunsa na
Alkhairi"
"Allahumma Amin".
Zahra ta fada.
"Me za'a dafa miki? Mu dai nayi Mana nida bakon ku".
"Wai bakon mu wato dai bazaki ce Mai gadin ba ko?.
Dariya tayi. "Wlh baya Kama da masu gadi Kinga kuwa ai bana ce Masa ba".
"Haka ne ki dafa min indo mie da cooker oat kawai".
"To an gama sai kin fito".
Ta fada tana juyawa zuwa main parlour din yayin da Zahra ta koma ciki.

*************
DAMAGARAM NIGER REPUBLIC.

Cikin takun ta na nutsatstsiya kuma wayayyar mace 'yar gayu ajin karshe ta shigo
parlourn tana sanye da doguwar rigar madam gezber kalar peach sai gyalen kalar
light yellow touching din flowers din dake jikin kayan sai takalmi plat Mai azabar
kyau shima light yellow din tun kafin ta karaso kamshinta ya hade gurin.
A hankali ya dago ya dubeta har ta karaso gurinsa, tattara aikin da yake yayi ya
Maida hankali a kanta lokacin da take Zama a kujerar dake gefen da yake.
"Sannu da aiki Yaya barka da Asuba".
Ta fada tana sadda kanta kasa Bai amsa ba Jin shirun yayi yawa yasa ta dago kanta
ta dube shi, ita yake kallo.
"Yanzu abinda Kika zaba kenan Zainab da girmanki da hankalinki ki zazzage jiki ki
baro dakin mijinki kizo ki nemi guri ki zauna mijinki yayi rarrashin duniyar Nan
kinqi ki saurare shi daga karshen ma Kika zabi ki dawo Nan Damagaram saboda a Yamai
uncle Yousoufu ya nuna Miki rashin kyautatawar abinda kikayi shine kikayo yajin Nan
ko?.Ni tunda tubus ne Bari kizo ki zauna ki Mike kafa gashi nan har an Fara kawo
Miki caffar ana son aurenki idan kin Gama idda wannan arzikin ki ne?".
Ya fada Yana kureta da ido, da sauri ta cira Kai ta dube shi. "Ni Kuma Yaya ake
jawo min zawarci kawai daga ganin mace sai ace zawara ce".
"Kada kiga laifinsu sun ganki yau sun ganki gobe Baki da niyyar tafiya,idan Badi'a
zata fita ki wanke jiki ku kama tafiya ba dole ace Miki haka ba".
Idonta taf da hawaye ta dube shi "to Yaya ya akeso nayi kasan dai yanda abun Nan ya
kasance duk yanda naso a saurareni idanuwa suka rufe ba Wanda ya kula da abinda
nakeso su gane Saida suka rabani da Dana yabar gida cikin bacin Rai Wanda har gobe
ba Wanda yasan inda yake, gaskiya Kuma tayi halinta yanzu za'a matsamin da zarya na
fada musu niba yaji nayi ba duk ranar da yarona ya dawo Zan dawo".
"Zainab a gabana kike fadar danki, Dan farin ba zakiyi min Kara ba".
"Kayi hakuri Yaya na Bari d'anka to" ta fada.
'yar dariya yayi na nawa Kuma sai dai a koki gaba, yanzu Dan Allah Alfarma zakiyi
min kiyi hakuri ki koma dakinki Suma sauran yaran suna bukatarki kusa dasu ko badan
Babansu ba ki duba girman Hajiya Inna har Yamai Saida tasa aka kaita ko a jirgine
dai ai tanayi dake ne amma Kika kasheta da dadin Baki akan kina tafe kikayi zaman
ki karshe ma kikayo hijira daga can, duk laifin Hajja ne wlh ita an taba Mata dan
'yar so ba zaman lfy, gobe nace aje Abuja a daukeki tunda ba jirgin sokoto direct,
kije kiyi ta yi masa addu'a bakin uwa Mai Albarka ne akan 'ya'yan ta muma muna
tayaki nasan fushi yayi idan ya huce ze nemi gida".
Har ranta bataso wannan hukuncin ba Amma yata iya da Yaya ishaq uba ne sak tun
bayan rasuwar mahaifinsu bai barsu da kukan maraici ba, duk rintsi baya Bari su
koka uwa uba yanda ya janyo gudan jininta ya nuna Masa hanyar nema tun a kananun
shekaru duk abinda yaronta ya zama shine sila gashi Zuwa yanzu Allah yayi Masa
karfin daya fi na Yayan. Hira sukaci gaba har Aunty Badi'a ta fito itama kamar me
Zuwa gasar sarauniyar kyau ita Fara ce tas buzuwa kallonta Yaya ishaq din yayi
"wato ta wata fuskar naji dadin zuwanki Zainab ko banza mutuniyar ta koyi gayu irin
naki da dai sai a hankali".
"Kai Yaya wlh bani na koya Mata gayu ba Daman Aunty na me class ce ko Aunty?".
"Fada Masa dai,kawai nasan dai na koyi amfani da perfumes designers dani kowa ne ma
saye nake Amma yanzu tunda ta bani naji dadinsu nake amfani dasu". Dariya yayin
Yana fadin .
"Ba cinya ba Wai 'yan magana sukace kafar baya, Wai yanzu Ina da kikace min zakuje?
Bana son yawo har an Fara min sallama idan ta Gama idda".
Ido Aunty Badi'a ta kwalalo "sallama Kuma?.
"Wlh kuwa shi yasa nace ta tattara tayi hakuri zanyi Mata booking ta tafi kawai
muci gaba da addu'ar Allah ya bayyana shi duk inda yake".
"Gaskiya kam shi yasa kenan ranar da mukaje gidan sarki kingmakers sun fito daga
meeting da Mai martaba Naga ana nuna ta har wani dogari Yana kokarin Zuwa gurin mu
muka tafi".
"Kinsan kuwa sakon daga fada yake".
Baki Ammi ta rike "tab gara nasan inda dare yayi min kafin wannan labarin ya Isa
kunnen general".
Ta fada suna nufar kofar fita daga falon.
"Da dai kin yiwa kanki gata"
Yaya Ishaq ya fada.

*********

Tun safe su Mahmud suka fita da Sameer su shiga can su fita can duk da Sameer Kusan
Dan kallo ne an Kai ruwa Rana kafin a samu ganawa da Wanda alhakin matsalar ke
hannunsa Basu suka dawo ba sai dare a gajiye suka dawo Jin dadinsu daya ba a hotel
suka sauka ba gida ne. Sameer yayii musu order din abincin Africa. Saida sukayi
wanka sannan sukaci abincin inda Allah ya taimaka sunyi sallah a wani masallaci a
hanya. Bayan Mahmud ya shiga daki wayarsa ya Ciro ya shiga ciki gurin da akayi Masa
connecting da CCTV nan ya lalace gurin kallon Zahra yanda yake more kallonta yasan
da ace tasan da CCTV a dakin bazata Bata sakewa haka ba tana sabgoginta. Amma ganin
ita kadai a dakin take zuba yanda takeso, amma yanda ya fuskanceta kamar wani Abu
Yana damunta ya Raina yanda take walwalarta, ya rasa aikin me suke ita da Mai Taya
ta zama Dan gani yayi ita Mai tayata zaman ta fita waje da alama wani Abu ta sawo
Dan can baya yaga ta hada wuta da gawayi akan wani Abu ta Dora tukunya Mai Dan
girma, so yake yaga wace wainar zasu toya.
Dayar wayar ya dauko Yana kokarin kiranta sai kuma Kiran Mr Lee ya shigo akan Yana
fada Masa kome yake ya fito bakin da zasuzo daga Thailand sun karaso shi kadai ake
jira, tashi yayi Yana Kiran Sameer akan ya zama ready zasu fita.

**
ZAHRA.
Tun bayan data gama break Basu zauna ba aiki Zahra ta dauko dambun Nama take son
yi yau akwai Naman da yawa sai kuma abinci shima Mai Dan yawa haka Nan taji tana
son kaiwa Abban ta da Baba Malam abincin juma'a zilai ce tace a sawo kufat ayi
suyar dambun a Kai tunda da yawa za'ayi ta Bata kudin aka sawo ta Dora, Basu suka
Gama aikn ba sai bayan azzahar zilai ita ta mikawa zayyan bayan ta wuce ne ya bude
abincin yaga irin garar da aka kawo Masa yayi ta mamakin yanda matar oga ta iya
girkin hausa haka Mai shegen Dadi gashi ita Kuma ba bahaushiya bace ko Ina ya samo
wannan da Kuma dalilinsa na zabar wannan rayuwar shifa ko a mafarki baiyi tunanin
ogan nasa ze iya sakewa har ya Mike kafa yayi zamansa a irin wannan muhallin ba da
iyalinsa, haka yayi ta sakawa Yana kwancewa.
Sai da su Zahra suka Gama Zuba komai a mazuban da suka Dace sannan Zahra ta wuce ta
Kira magaji a waya akan yazo tana nemansa sannan ta shige wanka sai bayan la'asar
magajin yazo lokacin ita kadaice a falon tana tulawar alqur'ani, Saida ya cika
cikinsa Yana zuba Santi sannan ta bashi yace ta fito Masa na Baba Malam Dana
gurinsu Ammah har ya Kai kofar fita daga parlour ya juyo Yana fadin "inyeeh su Adda
Zahra an girma har an Fara aikin neman ladar tsaffi da fatan dai kin fadawa mijin
naki kada garin neman lada a kwaso zunubi". Ya karasa fada Yana dariya.
"Allah ya shiryeka magaji Kai Kullum baka girma ko?"

"A'a zancen gaskiya ne Dan bawan Allahn nan baki San yanda yayi ya Nemo kudin sayen
kayan nan ba Amma kin tashi kin zuba irin wannan garar Dan kawai Kinga baya gari
ko?"

Harararsa tayi "To nayi kayan nan dai nawa ne mijina ya aje min Bai Kuma yi min
iyaka ba duk abinda nakeso zanyi dasu idan bazaka Kai ba dawo ka aje min sai Aunty
zilai ta Kai ko naje da kaina". Ta taso ta nufo inda yake da sauri yayi gaba Yana
fadin.
"Allah ya huci zuciyar uwar gidan Mahmud tuba nake".
"Dan rainin hankali shi dai gurinsa ya saka mutane magana".
Aunty zilai ce ta Bata amsa Sam Bata lura da fitowarta ba.
"Kema uwar dakina Kamar kin manta halin Mai sunan Alhaji ai shi burinsa Ke nan yayi
jan magana".

"Ai sai yayi tayi tunda halinsa ne"


Abincin zilai ta kawowa Zahra Nan cikin parlour some times Bata fiye son zaman
dining ba, kitchen zilai tayi niyyar komawa Zahra ta Hana "ki zauna a nan muyi
lunch din Ina Zaki kuma koni bafulatana bana irin wannan d'abi'ar".
Sun Fara cin abincin kenan door bell din tayi k'ara zilai ce ta tashi taje ta bude
Mujiba ce tare da wata yarinya Sa'ada 'yar makotansu.
"Kai! Kai!! Kai!!! Tab amma dai batan hanya kikayi Mujiba, yanzu Alkawari da amana
sunce haka? Yaushe rabonki da gidan Nan?"
Dariya mujibar tayi tana fadar "eh lallai da sauranki irin wannan Baki zai- zai,
Kuma shike Nan daga kawoki saina dunga sunturi a gidanki ai Mai gidan saiya saka
Mai gadi ya hanani shigowa tinda Zan zamar masa matsala, Wai ke tsaya waye a gate
din gidan nan daya tsaremu da dogon turancin daga Ina zuwa Ina me mukazoyi ke
tambayoyi dai gasu nan kamar zanga Mrs president".
Ta fada Tana Zama a kujerar dake kusa da zahrar Sa'ada ma ta zauna.
Spoon din hannunta Zahra ta aje "Bari kawai Muji wlh Nima haka na ganshi haka Nan
Rana tsaka ya canzawa Mai gadin gurin aiki ya mayar dashi makarantar gidan Baba
Malam ya ringa share share ya kirawo wannan bansan ko daga Ina ba yanda aka wayi
gari da Mahmud shima haka aka ganshi nifa lamarin yafi karfin tunani na kawai na
saka ido ne Naga karshen film din".
Ta fada tana Dan tab'e Baki.
"Amman wlh Baki da kirki auren naki kike cewa film dan bawan Allah ya biya sadaki
ya daukoki daga gidan ku ya killace ki guri daya ya Baki ci da Sha amma ki Kira
Masa aure Shirin film humm zakiyi bayanin film da alama komai normal yake tafiyar
Miki ko Aunty zilai?"
Dariya tayi "A'a babu ni a cikin wannan maganar kunga tafiya ta".
Ta wuce kitchen da plate din abincin ta.
" Kinga Sauko kiyi serving din ku, ni ban iya abinda Kika iya ba ku Kenan bakinku
ba kintsi ku dunga sakin magana irin haka Ina Dadi Kinga kin Kori Aunty zilai daga
wurin".
Tasowa tayi ta sauko kusa da zahrar tana fadin "lallai kina Jin Dadi irin wannan
garar haka sauko sa'ada Wai Ina Mai gidan na Dan kwana biyu ban ganshi ba?"
Plate din ta ture gefe ta dauko tissue tana goge bakinta.
"Yayi tafiya jiya baya Nan".
Tsayawa mujiba tayi da cin abincin. "Bayanan Kamar ya?"
"Kamar yanda na fad'a Miki yaje taron gamayyar Qungiyoyin da suke taimakawa ilimin
makarantun government Dana allo a Nigeria da wasu kasashen Africa, to a Nan zone
din namu na north east shine aka dauka a Bauchi state, a jigawa da Kano ma duk suna
da nasu wakilan tunda state uku suka dauka".

"Masha Allah kice wata Rana ku sai turai tunda Mai gida ya Fara irin wannan babbar
harka ai ku hannu sama chololo lallai mutuniyar kinzo da goshi".
Tsaki tayi wlh ki raba kanki da camfi Wai nazo da goshi to tun kafin nazo yake
aikinsa Kuma tafiyar ma dagawa sukayi tun ba labarina a rayuwarsa zasuyi abarsu
Nima da abinsa na same shi sai yanzu ne dai ta Kara tasowa.
Haka suka dunga Hira har Kusan magariba sannan suka tafi Zahra ta Basu kilishi da
biscuits masu yawa.

Saida magaji ya Fara Kai sakon Baba Malam sannan ya karasa gida, yauma aikin Ammah
ne lokacin daya shiga parlourn ta ba kowa sai Alawiyya tana saka turaren wuta da
freshner tambayarta yayi Ina Ammah? Tace Masa taji dakin Abbansu can ya nufa da
basket din da ledar knocking tare da sallama a kofar falon Mamace ta amsa Masa ya
bude ya shiga da alama wani Abu suke tattaunawa.
Gaishe da Abban yayi sannan ya gaishe dasu Ammah Yana aje basket din da ledar Naman
da aka kunshe cikin poil paper.
"Abba gashi inji Adda Zahra tace a kawo maka".
Mama ce ta taso tana fadin"Kai Masha Allah lallai wannan 'yar tana ji da Abbanta".
warmers din ta Fara cirowa tana bude miyar falon ya cika da kamshi Curry da spices.
"Abban ne yace "magaji sannunka Kaima lallai uwata ta haifu Allah ya yiwa wanna
aure Albarka ya tsane idon makiya wlh naji Dadi kwarai da gaske a Miko min nan Naga
abinda uwata ta kawo min".
Ya fada Yana mik'awa magaji bugun Abuja biyar zuwet.
"Na gode Abba, Kuma ta bada an kaiwa Baba Malam ma ya fada Yana nufar kofa.
"Masha Allah nasan uwata zatayi abinda yafi haka".

Cikin rawar jiki mama ta kinkimi basket din ta Kai gurin da Abban yake zaune ta
dora akan coffee table, sannan ta dauko ledar, ledar yace ta bude lafiyyayan dambun
naman rago ne yasha kayan Hadi ya sayu jawur dashi sai Kamshi ke tashi, Dina yayi
yakai Bakinsa ya tauna Yana fadin "Masha Allah uwata ta Gama min komai wlh har
Raina Ina son yarinyar Nan bilhaqqi uba ta daukeni sak duba ki gani Rabi'a ga
Asma'u a zaune amma Ni ta yowa wannan garar Kai madallah, Yau abincin ki sai dai
yayi hakuri na uwata zanci".
Ya fada yana kallon Ammah. 'yar dariya tayi Ammah tana fadin "Ana ta sabon d'a wa
yake ta tsohon da inji barmani choge".
"Gaskiya kam, ai Babu Mai shafewa Zahra Zane a gurin Abba"
Mama ta fada.
"Ki Fadi ki Kara Zahra yarinya ce mai tsananin yi min biyayya ki duba yanda lamarin
auren Nan ya kasance Amma tunda tayi 'yan koke-kokenta ta hakura ba Wanda ya Kara
Jin kanta, duk da mijin nata Mai Karamin karfi ne akan wadanda suka nemi aurenta
Allah be nufa ba da Kuna duba da inda ta fito da Kuma uwa uba dangin mahaifiyar ta
Amma tayi zaman ta Ni kuwa ba abinda bazan yi Mata ba matukar baifi karfin arzikina
ba".
"Wannan gaskiya ne duba da yanda ta waye tayi karatu Mai zurfi ai ba wata ce
bijirewa zatayi ayi ta Kai ruwa Rana"
Mama ta fada.
Yar dariya kawai Ammah tayi duk Dadi ya cikata Bata taba tunanin Zahra nada wayo
haka ba tasan dai abun duniya Bai rufe Mata ido ba.

✨✨✨
✨✨✨
AUREN HUCE HAUSHI
✨✨✨
✨✨✨

Maman Fateemah.

Page 32

_______Qaran alarm din daya saita ne ya tashe Shi sallar Asuba, duk da bai
kwanta da wuri ba Dan sai Kusan karfe biyu na dare suka shigo gidan, meeting din
nasu sun jima suna tattaunawa akan sabon kafanin da zasu bude a jihar kebbi na
shinkafa, masallacin da suke sallah da gidansu akwai tazara sosai shiyasa ya saita
kafin sallar Asuba da kamar hour daya, sai da yayi yaqi da Shaidan sannan ya samu
ya sauko daga gado Bai jima a toilet ba ya fito sanye da bathrobe Fara tas Mai
jikin towel. Jallabiya ya saka yayi raka'atanul fajri sannan yayi waje a Yana
niyyar yiwa Sameer knocking ya bude ya fito.
"Barka da Asuba" Sameer ya fada yana mikiwa Mahmud hannu sukayi musabaha,
"Ashe ka tashi ai nayi tunanin saina shafa maka ruwa sannan ka mitsa".
'yar dariya Sameer yayi Yana fadin "irinku da kuka San inda kuka dosa Kuna dagewa
da mujahada to mu ta Yaya zamuyi kwance muna barcin asara ai sai lalacewa tayi
yawan".
"Kayya Kai dai Allah ya datar damu kawai"
"Allahumma Amin"
Sameer ya fada lokacin da suka jero suna Kara tattaunawa akan harkokin yau da
Kullum, Sameer ne yaja musu motar suka fice daga gidan, bayan sunyi sallar zama
sukayi akayi karatu Kusan masallacin mahadar 'yan Africa ne mazauna can Kusan duk
Wanda yake a kukkuken gurin Baya Bari khamsu salawat ta wuce shi, sai da gari ya
waye sannan suka nufo gida.
A hanyar ne Sameer ke fadawa Mahmud sunyi waya da Habib jiya a kan training din da
za'ayi na matasa maza da Mata na koyon sana'a.
Har suka zo gida suna zancen, yaso yayi barci amma ya fasa, so yake ya Kira Nigeria
baze iya mazewa ba Kamar yanda yayi niyya Bai gane shi Mai rauni bane sai akan
yarinyar nan,sai da yayi Mata nisa ya gane shayi ruwa ne, duk da Bata shigo
rayuwarsa da Wasa ba kafin ya hadu da ita shi jarimi ne sannan shi baima fa San
yanda kake kwana da Abu ka Kuma tashi dashi, shifa idan ya tunata har wani ji yake
zuciyarsa ta harba, yaso ya dan Bata iska, so yake ya fahimci shin ta karbeshi da
zuciyarta da gangar jikinta ko Kuma har yanzu tana zaune dashi ne by force na
iyayenta, amma idan ya kalli kwayar idanunta Yana hango wani Abu na daban a cikinsu
Kuma uwa uba yanda sukayi rayuwa a Dan zaman da sukayi da ita.

Bayan sun shiga gida kowa nasa gurin ya dosa Dan shi dai Sameer barcin ya kama, shi
kuma daya shiga wanka ya sake, shifa idan ze wuni Yana zubawa jiki ruwa bashi da
damuwa. Sai da ya gama komai ya Haye gado daga shi sai singilet Fara sol da boxer
short.
Wayar ya dauko dauko cikin ikon Allah yaga Zahra online ji yayi wani Dadi yaji ya
rufe shi, vedio call ya Kira daya wayar Kuma ya bude connection din CCTV.
Tana cikin charting da Aunty Nawwara kawai kiran nasa ya shigo Yana kallon yanda ta
kwalalo Ido waje abin har yaso bashi dariya, hijabin da tayi sallah ta dauko ta
rufa kirjinta sannan ta daga Kiran suna hada Ido taji gabanta ya Fadi ji tayi abun
Nan na da ya dawo Mata.
Sallama yayi mata da husky voice dinsa wanda ya saukar Mata da wata muguwar kasala,
a hankali ta daga idonta ta kalleshi cikin murya Mai rauni da rashin karsashi ya
amsa Masa sallamar, kuri yayi da idon Yana kallonta yanda tayi Masa wani irin kyau
Kamar shi gani yayi a tsakanin jiya da shekaranjiya Kamar an Kara Mata kyau.
"Ki bude Ido ki kalleni ki bani labarin abinda ya faru daga tafiya ta Zuwa yau,
kuma wlh ki cire hijabin nan tunda ba sirikinki bane Ni da Zaki dauko hijabi ki
Kama rufe jiki wato Ni ban cancanta Naga abinda yake halalina ba ko?"
Kai ta girgiza tana masa kallonsa a shagwabe.
"Nifa tunda nayi sallah nake sanye da abuna bawai saboda Kai na saka ba nida bansan
zaka tuna Dani bama ballentana ka kirani, nifa na dauka Kama shafe babina tunda
baka nemana wanda ka damu dasu kake nema".
Ta fada tana juya sexy eyes dinta wanda Bai sani ba ze dauka da niyya tayi Hakan.
Ajiyar zuciya yayi Yana Hadiyar yawu shifa ganin Nan da yayi Mata ta jangwalo masa
wata fitinar da sai Allah kawai.
"Ki cire hijabin Nan Allah kona Baki mamaki". Kafada ta make tana kallon gefe Dan
wani fitinan nan kallo yake Mata.
"Dan Allah ka dena kallona".
"Ikon Allah wato naje nayi ta kallon Mata a titi kenan ba ruwanki ke ko irin 'yar
kissar Nan ta Mata Ni baza'ayi min ba tunda ni ba Mai aji bane banyi boko mai zurfi
ba ko
"Ni kuma? Yaushe nace bakayi karatu Mai zufi ba?"
Yar dariya yayi irin ta kana cikin ?nishadi din nan.
"Wato wayo zakiyi min na bar maganar hijab wlh ki cire Kona biyo dare nazo Nigeria
na....
"Dan Allah ka Bari wlh Zan cire kada ka fada".
"Ki Bari kiji mezance Mana my previous".
Ya fada Yana Kashe Mata ido.
Itafa mamaki yake Bata idan Yana fadar wasu kalmomin turanci sai taji Kamar zurfin
iliminsa ya wuce yanda ake fada, ta ko Ina a waye yake ga wata irin tsabta ta ban
mamaki itafa idan ba karya idonta yayi Mata ba sai tace Bata taba ganin ya Mai
maimaita Kaya ba idan ya saka Bata qara ganinsu a jikinsa.
"Wlh kiyi abinda nace kona baro Miki aikin da Baki shirya Masa ba, 'yar yarinya
dake kin hana zuciyarta sakat tunda na Dora idona a kanki komai ya kwance min duk,
akanki na iya tsayawa nayi doguwar magana na iya ja in ja akan Abu duk soyayata da
Hajiya Innata saida mukahau sama da ita mukayi uwar watsi nayi Mata yaji Kuma haka
kawai Allah ya dubi diminiya ta ya tausayawa Dan malam kiyi min rowar ganin
halalina, wlh Zan fadawa oga Sameer ayi min afuwa na dawo gida na fasa attending
din meeting din a saka wani na dawo na rungumi 'yan kayana".
" Wai Kai baka jin komai idan ka Fadi magana! Dan girman Allah kayi zamanka kayi
abinda ya kawoka in dan hijab bari ba cire. Amma Dan Allah ka Bari na saka riga
Allah ba kaya a jikina sai vest".
Wani kallo ya jefeta dashi na Amma kin Raina ni.
"Dan Allah, wlh kunyarka nakeji da gaske"
Ta fada tana sunkuyar da Kai kasa.
"Kunyata ni Kuma wlh immediately kuwa Zan cire kunyar Nan aini cutuwa zanyi, To wai
tsaya na tambaye ki yaushe Hakan ta faru? Ko bayan na baro kasar ne ki? amman ai
bakya jin kunyar kallon tsabar idona ki tarewa wani Kato fada Dan nace masa lusari
kika Kare min tas har kina fadin na Kama ki na runguma ko kina min kallon Dan
duniya ko? humm Ashe ma duka nine lucky din a cikinsu dama na San abin nawa ne Aida
saina dama daddawata da moda a lokacin Dan wlh a Ranar sai da na Raina kaina Banda
mutum besan gobensa ba Aida saina Yi wandaqata a lokacin" fuskarta ta rufe da tafin
hannunta dayan, da gaske so yake ya koya Mata fitsara taga alama shima ba kyalle
bane cikakken zani ne. Idonsa ne ya sauka q gurin data cire hijabin.
"wow!! Masha Allah! Koke fa Amma da kin zumbuda hijabi Kamar wata matar liman ai
yanzu hirar zatafi Dadin yi ki kawar min da tunani kowa daga zuciyata sai naki,
Baki fada min abinda kukayi jiya ba Naga harda spare girki a waje" .
Zaro ido tayi tana dubansa "waye fada maka nunyi wani Abu a gudan?
"Nina gani kinsan nabar idona daya a Nan na taho da daya, ga Kuma Dan gidana magaji
shine yayi min voice note ya bani labarin selfishness din da kikayi na kawai su
Abba Kika garar arziki ta juma'a Kika ware min iyayena Mata, shi yasa Kika saye
zuciyar su Abba da Baba malam kenan,? Kullum maganar daya ce ga amanar yarinyar Nan
ka kula da ita Ashe dai tushiyar Baki kike bayarwa".
"Kai wlh ba haka bane ai gani nayi idan na kaiwa Abba Kamar na bawa Ammah ne, haka
Baba malam ma ai Iya Abula na bawa koba haka ba"
"Eh kusan Hakan ne amman dai da gyara, Kuma kike wani cewa Abula ko 'yar Karar Nan
Babu nifa sunan tsohuwata ne,amma kici gaba da fada wata Rana kunya zakiji idan
Kika fada a gabanta tunda bakinki ya Saba fada kinsan dai mu mutanen karkara bama
Raina abun fada can zakiji zance ya zagaye cikin kauyen mu ace Mamuda ya auro 'yar
birni ko sunan Inna Bata sayawa gatsau take fada".
Kai ta Dade tana tadan turo Baki irin na sakatattun yaran Nan tana fadin "Nifa
ban sani ba Ina janta ne tunda sunan kakata ne babar su Ammah zakace min waye waye
nima ai Mamana ce ba taka bace Kai kadai yanda kayi kutse a gurin Amma Nima haka
zanyi a gurin Mamana harda Hjy Inna".
"Kice nayi celebration ana son da Ammi, inye matar Mahmudun ba, fada min wace
addu'ar kike min Dana kasa kallon ko wace mace da sunan so tun bayan kin shigo
rayuwata, da dai bana musu da kowa Amma a kanki humm har bore Saida na koya, oya
fada min sirrin inji?"
Shiru tayi saboda ji tajeyi kamar zir take a gabansa, Amma ta lura shi ko a jikinsa
kamar ma be damu da yanda take din ba.
"Kinyi shiru ko abun sirri ne baza"a fada min ba?"
"To me kake so na fada maka".
"Komai ma, me kike fadawa samarin ki idan sunzo zance? Nima yau zancen nazo Wanda
ban samu damar yi ba a baya shine yanzu nike qara'i".
Batasan sanda tayi dariya ba "Au dariya ma na baki ko? Shike nan wlh nifa a kanki
na iya zance me yawa da mace ada daga Ammi sai Hjy Inna kawai nake doguwar Hira
sadu, nasan duk ranar da Hjy ta ta ganki sai tayi Miki ciwon Baki tace dan kwali
yaja hula kinsan meta fada lokacin Dana fada Mata mgnr ki?" Girgiza kai tayi alamar
A'a.
"Cewa tayi idan na cika cikakken namiji na shiga duniya na nemoki, Ni kuma nayi
wani Alkawari daga ni sai Allah saina bata mamaki wlh".
Kama Baki tayi tana Dan Zuba masa sexy eyes dinta wadan da ke rikita Masa lissafi.
"Kakar taka zaka bawa mamakin duk soyayyar da kake yi Mata kace za'a ganku a
rana?".
Kai ya gyada Mata yana gyara kwanciyarsa.
"Yes ai kece mahadin aikin da zanyi na Bata mamakin ko bazaki tayani ba?".
"Ni kuma meya hadani da dabin ku?"
"Kina son sani na fada Miki?"
"Uhm".
Karan doorbell ne ya dakatar dashi daga kokarin bayanin da ze Fara mata.
"My precious Afuwan naji ana bukatar shigowa Bari naje I will call you later, take
care by".
Ya tura mata wani hot kiss Yana kashe Mata ido ya sauka daga online din.

********

DAMAGARAM.

Waya ce a kunnenta tana magana cikin tsantsar ladabi kamar tana gaban Mai magabar,
cikin ladabi ta Fara fadin "wlh Hajiya ba haka na fada Masa ba cewa nayi kada ya
tura kowa Abuja nayi booking din flight ne daga Abuja Zuwa sokoto, tunda Yaya ishaq
jirgin Abuja ya yi min booking Kuma nace masa ko nazo sokoto bana son a turo min
kowa yanda na fita Ni kadai haka bake bukatar dawowa ni kadai kinji yanda mukayi
dashi ai nace masa Zan dawo Amma gani yake kamar gaba zan karayi"
"To ai yanda Kika gindaya Masa dokar ne yake tantamar hucewar taki, kiyi hakuri
Zainab anyi Miki ba dai daiba Amma ki zama mai yafiya akan laifin da akayi Miki
kema sai Allah ya yafe Miki naki kura kuran, ki Kara godewa Allah kece karama ke
Kuma Allah ya daukaki naki Dan fiye da kowa a dangi ki dauka abinda ya faru
jarabawarsa ce tazo a haka,Daman Allah swa yace shin bana jarabceku ba? to ki dauka
hakan rubutaccen al'amarine daga Allah idan aka daure wata Rana sai labari, shi ba
yaro karami bane da za'ace ya bata kawai yayi Mana fushi ne inaji a jikina Yana
kusa da dawowa garemu da izinin Allah, ai kawunsa mustapha yace min ba abinda ya
tsaya a harkokinsa Dan yana bibiyar lamuransa a yanar gizo yaga komai yana tafiya
daidai".
"Nima Ina bibiyar lamarin nasa Hajiya Amma abinda yafi damuna koni bai taba kirana
ba ko sau da har zuwa Yau".
"A'a Zainab mu duka masu laifine lokacin daya kamata a saurare shi kowa baya ya
juya masa, Banda Mai biyaya bane yanda Allah ya daukaka shi ko ganinsa basai yayi
Mana wahala ba? Amma yaro Mai ladabi da biyyayya mun taru mun yi masa naqi ba dole
yayi nesa damu ba".
Saita balle da kuka, da kyar Ammi ta lallasheta tayi shuru. Sannan tayi mata
sallama tana Kara jaddada Mata zuwan tare da fadin ta turo direbanta ya daukota Dan
gidanta zata sauka tunda anan tabar motar data zo gurin Hajiyar da ita a Ranar data
wuce YAMAI.
Aunty Badi'a ce ta karaso kusa da Ammin tana fadin "ina ganin soyayyar uwar miji da
matar d'a amma ban taba ganin irin taku ba inaga yanda Hajiya Inna ke sonki ko
Yallabai Bata so haka gashi ta kwallafa rai kan Mahmud kamar me"

Zama sukayi a Kan sofa daya dake cikin dakin.


"Wlh Ni kaina Aunty Ina jinjina yanda Hajiya ke Sona da dukanin yarana shi yasa sau
da yawa idan wani Abu ya taso a gidan bana Bari taji ko labarin sa Dan nan da nan
zata tashi hankalin gidan sai Kuma abun ya Zama wani Abu daban Dan Kullum gani
sukeyi na Gama da kowa a gidan ballentana abinda ya biyo bayan rigingimun da akayi
wanda suka saka na baro musu gidan,sai Abun ya Kara zafi ganin irin tujarar da
general yayi da irin hukuncun daya yanke".
Dan nisawa Aunty Badi'a tayi kafin tace. "Abinda dai baiyi tsabta ba Kam sai dai
fatan Allah ya kiyaye gaba, Daman shigowa nayi muyi magana akan hukuncin da Zaku
yanke ne hada Mahmud Aure da 'yar aminiyarki matar takawa, tun a jiyan naso mu
tattauna sai nayi Baki sauka cinye lokacin, me ze Hana ki Bari aga dawowar tasa
tukunna sannan kiyi masa tayin yazo yaga yarinyar idan Allah yasa tayi masa a irin
matar da yake ra'ayin ta Zama iyalinsa Kinga shike Nan idan Kuma an samu sabainin
haka Daman ba'a amsa ba bare zumuncin ku ya samu matsala ko ya Kika gani?".
Shiru Ammi tayi tana nazarin maganar matar yayan nata Kuma 'yar uwa abokiyar
shawara.
"To ai abin dubawa Aunty kada fulani taga ban kyauta mata ba tayi min na huce ace
na buda Mata kasa a ido bazan iya ba, idan Allah ya dawo dashi mijin mace hudu ne
idan Yana da wadda yake muradin aure ya Kara da ita Dan nasan bazeki Haura'ul
Insiyya ba, duk abinda ake nema ga Diya mace Allah yayi Mata ga uwa uba nasaba".
"Haka ne Allah ya dawo Mana dashi lfy ya Kuma zaba abinda yafi Alkhairi, Amma dai
in ina Raye wlh ba Mai yiwa yarona dole ba ruwana da Amincin ku can tsaninku"
Baki Ammi ta Kama tana Fadin "Tofa kaji masu 'ya'ya wato kin nuna side ko?"
"Ki fadin koma meye Amma dai a barmin yaro ya samu peace of mind gaskiya, shi bashi
da idon ganin matan ne? Ina cewa kasashen duniya yake yawo Kinga kuwa wane irin
Mata ne be gani ba, Kuma da bakinki kike fadin yace shi da wadda yake so daman
biyayya ce kawai zeyi ya karbi auren da aka bashi Amma komai Daren dadewa zeyi wani
auren to ki cire kanki a cikin jerin masu tilasta 'ya'yan su auri abinda sukeso, ki
bishi da addu'ar Allah ya hada shi da abokiyar Zama ta gari kawai, se kimarki ta
karu a idanunsa ki Zama abokiyar Shawarar sa babu abinda ze rufe Miki Amma kina
shigo Masa da irin wannan zance ze Miki wani aji na daban, baze saki jiki dake ba
balle kisan menene matsalarsa, ki tsaya kiyi nazarin abin nidai shawara ce na baki"

Tunda Aunty Badi'a ta Fara Kora bayani jikin Ammi yayi sanyi saboda suk abinda
Aunty Badi'ar ta fada gaskiya ne, nisawa Ammin tayi "haka ne Aunty wannan
observation ne me kyau hakan zanyi Daman fulanince ta Fara kawo maganar Naga Kuma
ya dace na Bata goyon baya, Amman in Sha Allah zanbi Shawarar ki...✨✨✨
AUREN HUCE HAUSHI

✨✨✨

Page 33.

MAMAN FATEEMAH.

________Zahra ta Dade a kwance tana sakawa da kwancewa, wani irin yanayi takeji a
jikinta ita abun har mamaki yake Bata "Wai menene hakan" tayi tambayar da ba Mai
Bata amsa. abinda takeji wani Abu ne na daban Wanda Bata taba Jin irinsa ba akan
kowane da namiji ba, cikin kankanin lokaci ya cika Mata zuciya ita abun har kunya
yake Bata,ta gama bore harda su somewa dasu wunin Asibiti Kuma yanzu a wayi gari a
ganta dumu dumu cikin soyayyarsa ai da kunya wlh.
Wani tunanin ta qarayi Bata San lokacin data rufe idonta ba tana ambaton "Ya
Ilahiy wlh abun da matukar Allah ka agajeni gaskiya idan hakan ta kasance naji
kunya".
Ta fada tana qara qanqame jikinta.
Saida ta Kusan Bata minti talatin tana abu daya sannan ta yunqura da kyar ta
tashi,wanka tayi ta shirya cikin English wears yellow irin shaking material din Nan
sai sukayi Mata wani irin kyau Karamin mayafi ta rufe gashinta dashi black Mai
shara shara ana kallon bakin gashinta Mai santsi da laushi ta cikin gyalen, sama
sama ta fesa turarenta ta fito parlourn ba kowa sai kamshin freshner da turaren
wuta kawai sai Kuma sanyin A/C daya ratsa ko Ina,cikin takunta na nutsuwa ta doshi
kitchen inda take jiyo motsin zilai a cikinsa.
Sansanyan kanshi ta ya Fara shiga hancinta zilan kafin ta karasa shigowa.
"Masha Allah! Uwar dakina dawisu sarkin ado, Allah ya barki gidan Yallabai muhmudu,
ubangji ya kawo Mana kazantar daki Amma Bata shara ba".
Dan murmushi Zahra tayi tana Fadin kin jiki Aunty zilai ni kibar wannan maganar
gaskiya, Ina kwana".
Ta fada tana komawa parlour biyota zilan tayi tana Fadin "yau fa abinda kikafi so
nayi Miki" ta fada tana kokarin bude warmers din abincin,waina ce manya irin tasu
ta Bauchi sai Kuma pepper soup na cow leg da kunun gyada Wanda yaji Madara.
"Wow! Amma aunty zilai kin gama min komai na gode" ta fada tana janyo plate din da
zata Zuba, zilan ce ta karba da sauri tana fadin "haba dai gani a tsaye Zaki Zuba
abinci da kanki to meye amfanina".
Rike plate din Zahra tayi tana fadin "Dan Allah kada muyi haka dake Ina laifin
dafawar ma ai dadin sai yayi min yawa, Ina kwance Ina barci kina ta faman dawainya
sannan Zuba abincin ma Sai anyi mini".
"To menene ai aikina ne".
"A'a wlh ba Aikinki bane a Nan cewa akayi ki tayani Zama kwarai".
Ta fada tana bude abinci akan dole zilan ta hakura ta koma kitchen inda take wanke
waken alale zatayi musu cikin abincin Rana.
Bayan ta Gama yin break din parlour ta dawo ta kunna tasharta mbc max tana kallon
wani film da sukeyi, tana Nan zaune taji karar door bell ta tashi ta nufi kofar ta
bude yara ne kamar 'yan sheka sha uku haka suna rike da manyan ledoji kowa guys
biyu a hannunsa.
Cikin girmamawa suka gaishe da Zahra tare da fadin "gashi inji Baba Malam yace a
kawo Miki Kuma Yana gaishe ki".
Suka fada a tare, hanya ta Basu suka shigo da kayan ciki sai raba Ido suke suna
kalle-kalle.
"Sannunku ku aje ku zauna, na gode kwarai da gaske Allah ya saka da Alkhairi, a me
kukazo ne?". Dayan da yafi magana yace "Yaya Habibu ne ya kawo mu Yana kofa gurin
wancen mutumin" ya fada Mata.
"Masha Allah". Ta fada tana Kiran zilai, da sauri ta fito tana fadin. Gani uwar
dakina".
"Kaya ne Baba Malam ya Aiko aka kawo min".
Gurin da kayan suke ta karasa tana fadin "Masha Allah 'yar gatan Baba malam, an
gode madallah sai a Basu tukwaici". Zilan ta fada tana kokarin bude ledar dake kusa
da it's.
"To Bari na dauko musu ki shiga da kayan ciki sai ki zuba musu abinci a robobin nan
na take away Wanda aka kawo saboda zuba kayan gara Dan kada su zauna yau Ranar
wanki da 'yan aikace aikacensu ne," ta fada tana yin gaba.

Bedroom dinta ta shiga ta duba Sam ba kudi a gurinta, Dan Jim tayi sai Kuma ta bude
bedside locker ta dauko keys din dakin Mahmud daya Bata.
Kamar' Mai tsoron wani Abu kada ya kamata ta bude dakin, komai tsab hatta kamshinsa
Yana dakin kamar yanzu ya fesa yabar dakin,limshe ido tayi tana shakar kamshi,
komai na dangin electronic a kashe yake a dakin a hankali ta ratsa ta nufi inda ya
nuna Mata yace idan bukatar wani Abu ya tashi ta dauka, locker din ta janyo 'yan
dari biyar ne da dubu dubu ko wanne rapper uku uku 5k kawai ta Ciro daga cikin 'yan
1k din ta mayar ta rufe tana tunanin Kiran magaji yazo ya Ciro Mata kudin saboda
irin haka Bata bukatar komai tunda ba abinda ba'a aje Mata ba wani abun ma Sai a
shekara Bata nema ba.
Bayan ta kawo musu sukayi gdy suka fita, gurin Aunty zilan Zahra ta shige.

***********

Karfe biyar na yamma jirginsu Ammi ya sauka a sokoto, lokacin data fito Harabar da
masu jiran saukar 'yan uwansu suke,Habu direban Hajiya Inna ne ya nufo Ammi da
sauri Yana fadar "barka da sauka Hajiya, nine Hajiya Inna ta turo nazo na tare ki".
Ya fada Yana karbar karamar luggage din dake hannunta .
"To sannu da kokari nagode kwarai".
Direct gidan Hajiy innar ya nufa da ita da yake unguwar mabera, duk yanda Abban su
Mahmud yaso ta zauna part dinta daya Gina Mata Amman ta nuna tafi son daga nesa
dai.
Har kofar falon Hajiya Malam Habun ya kawo ta bisa umarnin Hajiya, lokacin da ze
tafi dauko ta fada masa ya kawo Mata ita har kofar parlour.
Kafin ta fito Yara qananu guda biyu suka fito da gudu daga parlour wanda yayi dai
dai da fitowar Ammi daga mota da gudu suka karaso, suna fadin ga Ammi! Ga Ammi"
suka fada jikinta a tare suna fadin "Ina kikaje Ammi Baki tafi damu ba mukayi ta
kuka".
Kansu ta shafa tana fadin "sorry My babies ba gashi na dawo ba, ai kuka Kuma ya
Kare"
Hannunsu ta rike ta nufi kofar da suka fito, sun riketa ram kamar zata gara guduwa
ta barsu.
A zaune Ammi ta samu Hajiya inna tana lazumi, gurinta ta nufa cikin takunta na
nutsuwa tana fadin "Hajiya barkanmu da yamma".
.
Ajiye tasbahar dake hannunta tayi tana kallon Ammi wadda tayi wani tas da ita,
bazaka taba cewa ta aje kamar' Mahmud ba, idan aka jera su mafi yawan mutane zasu
ce yayarsa ce. Gefen Hajiyar ta zauna daga kasa wannan d'abi'ar ta ce Bata taba
Zama a kujera matukar Hajiya na Kan kujera, cikin ladabi irin na D'a da uwa Ammi ta
gaishe da Hajiyar Tana fadin "Masha Allah zainabu kin cika Alkawarin da Kikayi min
Koda kuwa ba a lokacin bane nagode kwarai da gaske Allah ya Albarkaci zuciyar ki ya
Baki rinjaye akan duk masu son su tagayyara Miki zuri'a, ki Kara hakuri akan Wanda
kike yi lallai duk Wanda akace yayi hakuri an Bata masa ne, Allah yayi Albarka
yanda kike min biyayya kema Allah ya Baki surukar da zatayi Miki fiye da yanda like
min, Wai kin samu yin magana da mutumina kuwa bayan munyi wayar nan?".
"A'a har yanzu be nemi kowa ba ina ganin ko ba lafiya ba dai shirun tayi yawa ya
Kamata ace zuwa yanzu yayi hakuri ya huce ya dawo gida".
Ammin ta fada cikin damuwa.
"Ba komai in Sha Allah lfy na fada Miki yanda mukayi da mustapha kema kince kina
bibiyarsa ayi ta addu'a Allah ya sassauto da fushinsa ya waiwayo gida wallahi ko
cikin dare yaron Nan ya Fadi min a Rai to barcina ya Kare Kullum ta Allah sai anyi
mini saukar Alqur'ani akan Allah ya bashi kariya a duk inda yake wallahi nayi Dana
sanin fada masa maganar da nayi danasan maganar tawa ze dauketa da zafi wlh da
bazan fada masa ba yana cikin zafi".
Hawaye ne ya balle Mata kamar lalataccen famfo har da shashhshekar ta.
"Dan Allah Hajiya kiyi hakuri wlh ba maganar ki bace tasa yabar gida nakin dai yazo
Kan gab'a ne kawai".
"A'a keda Baki Nan mukayi yazo Nan Yana ta huci Dan motar dazo a ciki ma ko kashe
ta baiyi ba ya fado min Kamar an jefo shi, Yana huci Yana Fadi wlh duk duniya ba
Wanda ya Isa yasa ya auri safna Koda Matap sun kare shi Daman koya aureta biyayya
ne zeyi Yana da wadda yake da muradin aure, ni kuma a lokacin bani da cikakken
masaniyar abinda yake faruwa kinja layin kada a fada min gaskiyar maganar,Ina bude
Baki sai ce Masa nayi idan ya ciki shi d'ane na halali ya shiga duniya ya Nemo min
yarinyar da yake maganar a kanta Wanda take ganin darajarta tafi ta zuwairiyyar,
wlh shiru yayi a inda yake tsaye kasa cemin komai yayi Kusan tsawon minti biyar,
kafin ya kalli idona yace min wlh zakiga cikakken Dana halak, ki rubuta ki aje idan
kin qara ganina a sokoto ba tare da ita ba to kuwa shege ne ni,idan Kuma ban sameta
nida sokoto har abada ya juya ya wuce ko motar Bai kalla ba Kuma tun daga Ranar har
Rana Mai kamar ta yau ban Kara saka mahmudu a idona ba, sai dai Babban yaronsa Yana
zuwa ganina Yana kawo min duk abinda Mahmudun yake kawo min ciki kuwa harda
magungunan da nake sha na hawan jini".
Ammi tayi mamakin Jin Sameer na zuwa gurin Hajiyar koda Wasa Bata taba Jin haka ba,
Kenan wato kafa ya bawa mutane Yana cikin Nigeria din kenan bawai inda ake zaton
zashi ba.
"Allah kyau Hajiya ki daina damun kanki, jikina Yana bani Yana cikin kasar Nan Kuma
Yana da labarin komai tunda kikace min Sameer na zuwa, duk inda yake ya sani ya
hana shi ya fada ne kinsan halin kayanki dai".
Mardiyya da Urat Hajiyar ta kalla Tana fadin "yan nema kunki iyayenku sai uwar wasu
tun barinki garin Nan yaran Nan suka tare a Nan Wai saina kaisu Yamai gurinki tunda
aka fada musu naje suka tada hankalin iyayen sai su dawo Nan idan Zan koma na tafi
dasu, Kinga mardiyya jiya da Iyayen sukazo daki ta gudu ta rufe Dan ma kada su tafi
da ita, ko makaranta sai dai direban ya biyo ya dauke su anan ya dawo min dasu
Nan".
Kansu Ammi ta shafa tana fadin rigima ta kare tunda ga Ammin ku ta dawo ko?".
Kai suka gyada Mata a tare.
Masu aikin Hajiya ne suka shigo ta kofar baya daga kitchen suna fadin "lale
marhabin da Ammi barka da zuwa".
Gaisawa sukayi a mutunce tana tambayar su iyalansu.
Abinci na musamman masu aikin suka gabatarwa da Ammi Wanda Hajiya ta hanasu sakat
tun safe ake saukewa da dorawa da gaske Babu Mai shafewa Ammi Zane a gurin Hajiya
tana sonta kamar me.
Sai bayan insha'i Ammi ta kwashi su Urat ta nufi gida cikin motar data Bari a gidan
Hajiyar. So take ta bada mamaki yanda ta fice batare da sanin kowa ba a wayi gari a
ganta batare da kowa yasan sanda ta dawo ba, duk gidan amintacciyar Mai aikinta
kawai ta Kira ta fada Mata tana Nan Zuwa garin yay ko su Abeeda ba Wanda ta fadawa
tasan zumudin su ze saka kowa ya sani.

************

Safa da marwa take tun bayan gama wayarta da Aunty Ladi ranta idan yayi dubi a bace
yake Wai shi wannan yaron wane iri ne aiki akeyi a kansa Amma Kamar ana zubawa a
teku wannan guri na uku ne da Aunty Ladi taje Mata a Jos Amma amsar daya ce wannan
yaron yafi karfinta, Mata ne guda biyu a teaye a kansa da addu'a sannan yana da
tsarin jiki na ban mamaki Nan kusa ba abinda zeyi tasiri a kansa sai ikon Allah.
Wayarta ta dauko Asabe ta Kira cikin k"an k'anin lokaci ta daga Kiran "kizo ina
jiranki yanzu". Ta kashe wayar tayi wurgi da ita Kan gado.
Cikin abinda bai wuce minti Sha biyar ba Asabe ta shigo gidan ko part din Ammah
Bata shiga ba kamar yanda ta Saba direct ta wuce gurin Mama.
Parlourn ba kowa ganin haka yasa ta wuce bedroom dinta a tsaye ta sameta tana kaiwa
da kawowa Ido yayi Mata jawur kamar na tsohon mashayi.
Ko sallamar ta Mama Bata ba ta amsa ba ta, fara fadin "Ina ne garin da kikace min
'yar dago kawarki ta fada Miki da wani shahararren mutum Mai aiki kamar yankan
wuka?".
Shigowa tayi ta zauna tana kallon mamar "Wai lafiya na ganki haka?"
"Ina fa lafiya! Aunty Ladi ce ta tasheni daga barci take fada min taje har guri uku
ba sa'a, Wai yanda suka fada Mata yanzu ne ma Zahra ta gamu da Wanda ake ta fada
Mana a baya bawai wadanda mukayi ta aiki a kansu ba, Kuma Shi wannan din duk ya
fisu Shirin jiki Dan da alama yanda sihiri baya tasiri a jikin ita yarinyar shima
baya yi a jikinsa, Wai wasu Mata ne guda uku a da maza biyu tsaye a kansa duk juyi
sihirin baya kaiwa inda yake, yanzu Kiran da nayi miki ina son Jin tabbacin kin
koma kin tabbatar da Mai gadin ya saka wannan abubuwan da Kika bashi?".
Dan murmushi tayi irin na kwararrun 'yan duniya din Nan kafin tace "Haba Hajiya
shekara nawa muna tare ban taba ha'intarki ba sai yau an aiwatar da komai sai jiran
sakamako kawai ai wannan yaron bama Azare ba Kasar Bauchin ma gaba daya shi da ita
har abada, Kuma malamin da 'yar dagon ta fada min a wani gari yake cikin kasar
katsina ana ce Masa Bakiyawa tace idan na shirya zata rakani garin iyayen mijinta
ne daya rasu". Hake sukayi ta kullawa da kwancewa,Asabe nata Kara zugata akan ko
nawa zata kashe kada ta Bari Ammah da 'yar zumunta su fisu komai, tunda ta Nan take
samun nata rabon a jikinta idan Bata encouraging dinta itama zata rasa income nata.

**

Tun bayan ganawa da Bakinsa Mahmud ya shige bedroom ya Haye gado yaso ya Kira Zahra
suci gaba da Hira Amma saiya fasa Dan yasan yanzu gari ya waye sosai a 9ja Bari ya
kyaleta sai dare hirar zatafi tafiya yanda yake so. Bai tashi ba sai lokaci sallah,
wanka yayo ya saka kananu Kaya yayi sallah yana cikin addu'a yaji ana knocking din
kofa umarnin shigowa ya bayar Sameer ne ya shigo Bakinsa yaki rifuwa.
"Barka da Rana". Sameer ya fada Yana mikawa Mahmud wayar hannunsa.
Hannu yasa ya karba yaga menene yasa shi irin wannan murmushin.
Wani fine Baby ya gani nade cikin farin towel na jarirai fari sol.
Kallon shi Mahmud yayi Yana neman Karin bayani.
"Takwaranka ne madam ta haihu jiya cikin dare".
Cikin madaukaikin mamaki Mahmud ya kalli Sameer "are you serious?"
Kai ya gyada Masa Yana Fadin " yes sir".
Mahmud sai juya wayar yake Yana Kara kallon babyn.
"Masha Allah, my friend Allah ya Raya mana, amma me yasa ka taho ka baro yarinyar
mutane a watan haihuwarta ai sai iyayenta suga rashin kyautatawar ka ga 'yarsu".

Shafa Kai yayi Yana Dan murmushi "ba wani Abu,idan na zauna me zanyi musu duk
abinda ake bukata nabar musu".
Wani kallon baka da lfy Mahmud yayi Masa "an fada maka Bata bukatar kulawar ka ne a
irin wannan lokacin?" wlh Dana San lokacin haihuwata yayi ba inda zakazo Kuma yanzu
ka nemi visa ka koma gida daman Nan anyi clearing din komai U A.E din naji da komai
kawai, naji kace takwara na nayi zaton sunan Abban koko za'a saka masa?".
"Ai umarninsa ne yace nayi masa huduba da sunan ka".
"To Masha Allah! Godiya ta har gida zanje na yiwa Abban tafi karfin ta waya Allah
ya Raya Mana Mahmud yayi Masa Albarka, kaje ka Fara shiri tun yanzu ka shiga kasuwa
kayi musu abinda ya Dace".
"In Sha Allah".
Godiya Sameer yayi ya nufi kofa Yana fita alarm na shigo Masa Wanda Saida ya
girgiza shi baya yayo yana Murda kofar ze dawo ya jira yayi locking dinta, dariya
yayi Yana Fadin "manya gatan Wasa, Allah ya biya maka bukatunka na Alkhairi".
A Ranar cikin dare suka bar Kasar su duka Sameer yayi Nigeria shi Kuma Mahmud ya
nufi U.A.E .

✨✨✨

AUREN HUCE HAUSHI.

MAMAN FATEEMAH.

Page 34

AssalamuAlaikum warahamatullahita'ala wabarakatuhu.


'yan uwa muna barar addu'oin ku bisa rashin abokiyar aiki da mukayi ECCD co-
ordinator ta KIRIKASAMMA LOCAL GOVERNMENT JIGAWA STATE muna rokon Allah s.w.a ya
jikaanta yayi Mata Rahama yasa Aljanna makomarta tare da Iyayen mu da sauran
Al'ummar musulmi Baki daya ya Raya abinda ta Bari ya Albarkaci bayanta.

______ Misalin karfe uku da rabi jirgin sun Mahmud ya sauka a DUBAI INTERNATIONAL
AIRPORT (DXB) cikin amincin Allah, yana cikin kusan rukunin mutanen karshe a
fitowa, yana sanye da suit ash colour na kamfanin Armani hannunsa sanye da ogogo
Rolex, baya tare da komai sai jakar laptop dinsa a hankali yake gangarowa cikin
takunsa na cikakken namiji me ji da lafiya da karfi, direct gurin da taxin airport
suke ya nufa, baya bukatar asan yazo garin so yake ya tantance wata jimurda da aka
hada, taxin ya shiga saida sukayi balance a titi sannan ya fadawa direban ya kaishi
JW moritte marquis hotel cikin harshen larabci,sunyi tafiya mai tsayi kafin su
karaso hotel din, bashi da matsalar kama daki dan tun yana china yayi booking din
dakin ta online, katin dakin kawai ya karba ya koma waje yin 'yan uzurirrika daga
baya ya nufi ciki, wanka ya fara kafin yayi order abinci, sai da ya gama komai
sannan ya kwanta dan yayi matukar gajiya, yaso kwarai ya kira 'yar gidansa amma
yana son su tattauna sosai, sai yanzu yake jin haushin wani ra'ayin nasa badan haka
da suna tare da ita suna hutawarsu, yanzu kadaicin rashinta da be dameshi ba, wlh
da beyi alkawari ba da visa zesa ayi mata ta sameshi a nan saboda hotel din yayi
masa, yana daga cikin lattest hotels na duniya be taba sauka a wani hotel ba a
dubai sai BURJ AL ARAB JUMAEIRAH dakinsa parmanent ne duk mai hulda dashi a dubai
nan suka sani, duk da yana da gidaje a kasar shi be fiye son yakai abokanin
bussiness dinsa gida ba. Wannan shigar ta sirri ce shi yasa ya canza sheka baya son
asan ya shigo kasar mamaya sake son yakai wasu gurare, yanda har ya gama abinda
yake yabar kasar wani be sani ba duk da abune mawuyaci hakan ta faru.
Barcinsa yasha sosai dan har akayi sallar magariba be sani ba, lokacin daya tashi
ana gab da kiran sallar insha'i, a gurguje yayi wanka ya zura sabuwar jallabiyar
daya saya cikin kayansa a kasar, a cikin dakin yayi sallar magariba ya fito yabi
lifter zuwa masallaci,koda suka idar da sallah be dawo daki ba a nan harabar hotel
din ya Zauna da gaske yanayin gurin ya burge shi sosai, coffee yayi order ba'a jima
ba wata matashiyar balarabiyar yarinya ta kawo masa coffeen sai yaga kamar 'yar
gidansa, nan da nan yaji duk rintsi ita yake muradin gani number dinta ya lalubo ya
kira duk ba baya son kira direct yafi son ta Whatsapp.
Suna zaune a parlour ita da zilai tana Shan mutuniyar tata farm fresh, Kira ya
shigo a wayarta dake kusa da ita, tayi mamakin ganin code din Dubai har sai da ta
kusa katsewa sannan ta dauka, batayi magana ba Shima baice komai ba, ganin shirun
yayi yawa yasa zilan Fadin "naji kinyi shiru koba Kira bane".
Karamin tsaki Zahra tayi "wlh na daga amma naji shiru inaga ko wrong number ne dan
code din na Dubai ne ni kuwa waye ze kirani daga Dubai da dai Aunty Nawwara Bata
saudiyya da saina dauka ko sunje ne da mijinta tunda business man ne, Bari na kashe
wata kilama ba'asan an Kira ba"..
Kafin ta dauke wayar daga kunnen ta taji yayi magana cikin husky voice kada ki
kashe min waya, ki bude data zamuyi magana". kit ya kashe Kiran wayar tabi da
kallo a zuciyar ta tana Fadin "ikon Allah shine Kuma a Dubai ya illahiy, to Wai
wannan Dan talikin waye shi lamarin fa Yana neman Zama abin tsoro fa, yace Yana
yiwa kungiyoyin waje aiki ita Kuma a gefe guda wani Abu yake yi irin na Mai bada
umarni Kuma bataga yanayi gaban kowa ba sai ita, kamar Ranar da taji yana Kiran
zayyan da umarnin daya Bashi akan lallai ya sameshi da safe Kuma Bai karya Umarnin
ba"
Wayar ta kalla tana mikiwa zuwa bedroom dinta Saida ta shiga ta duba data idan Babu
ta saka tunda Sam Bata taba saka data ba tunda ta Fara amfani da wayar datar data
gani tayi bala'in Bata mamaki 4.5 BT ta gani sub din shekara daya ne.
Cikin sofa ta zauna Tana juya wayar Bata bude datar ba, wani Kiran ne ya sake
shigowa still dai nashi ne, dagawa tayi tana fadin Assalamu Alaikum warahamatullahi
ta'ala wabarakatuhu".
"Wa'alaiki Salam warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu, meya hanaki bude datar danace
a bude?"
Shiru tayi ta kasa magana,.
"Wai ko sai nayi ramuwar sayen bakin da banyi bane ake min jan aji irin haka. Dan
Allah kimin magana kona samu nutsuwa wlh ji nakeyi Kamar na gudo tun ba'a gama ba
duk kin mamaye ko Ina na kasa komai sai tunanin ki, Ni danasanin zuwan ma nakeyi
gashi sun rarraba mu wasu suna London mu kuma suka kawo mu hadaddiyar daular
larabawa, shine nace Bari na kira na fada Miki Koda abinda kike bukata na taho Miki
dashi tunda da kudinki a gurina"
"Kudina kuma? Name nene kuma yaushe na baka".
"Bake Kika bani ba ke aka bawa na manta na Baki Sai a Nan na tuna danaga Kaya irin
naku na 'yan Mata".
Ya fada Yana dariya.
"Wai 'yan Mata".
Ta fada tana Dan turo Baki irin bataji dadin Nan ba.
"Au ashefa an wuce wannan stage din ko?"
Ya fada da alamun zolaya.
"Wato kinki bude data sai kin cinye min 'yan canjin da aka saka Mana kinsan dai ni
ba iya saka Kati zanyi a kasar Nan ba, pls Dan Allah ki bude datar na ganki kona
samu nutsuwa nayi aikin daya kawoni, naso ace kina gefena a wannan gurin Kinga
dakina kuwa? da Hali gareni anan zamuyi honey moon irin Wanda naji su Habib suna
fada idan ana hira ko Zaki biya ki taho ki sameni?"
Ido ta ware kamar Yana kallonta.
"Na biyoka nayi maka menene?"
"Kiyi min abinda mace take yiwa mijinta ai kin gane?".
"Ya Salam haba Ya Mahmud menene haka kaifa yayana ne".
Wata dariya ce ta kubce Masa "A yaushe na zama Yayanki? Ki gyara zancen niba
Yayanki bane, haka kawai ki haramta min abinda Allah ya halasta min idan Zaki Ware
ki Dan ina dawowa labarin ze canza salo gara mu fuskanci juna ki tausaya min Kinga
Sameer fa ya Zama Daddy madam dinsa ta haihu sunyi min takwara,ai gara muma mu zage
dantse ko?"
Dokin haihuwar da aka fada Mata ita ta Hana ta gane inda nasa zancen ya dosa, cikin
nuna farin ciki tace "Dan Allah da gaske yaushe Fateehar ta haihu? Masha Allah!
Allah ya Raya kace mu sai Kano ko Yaya?".
"Allah bakinki ya kiyayi fada min yayan Nan tsabar kinibibi kawai yau Kika tashi
dashi Wai wani Yaya kamar a kauye, kibar 'yan garinmu su Fadi Amma Banda ke wato Ni
da yake ba Dan bokon kirki bane ba baza'ace min sweetie ba ko irin su my love ko
Dear, saboda almajirin soro ne ni ko?"
"A'a wlh ni ban fada ba, kawai dai Naga abokin Ya Abdul Hakeem ne kai ai kaima
yayan ne".
"To anki wayon, Kuma da kike cewa Zaki Kano ganin yaro keda wa zakuje kuma waye ze
kaiki Kuma kice Mata wacece ke".

"Address zata turo min Mana, Kuma maganar kaiwa sai Malam Bala direba kaimu nida
mujiba wuni daya dai, Kuma nace Mata matar yaron mijinta ce ko ba haka ba?
"Yayi Kam Amma saina dawo ki rakani muje tare anfi saurin ganeki ga kafarki ga
tawa, kice na sawo Miki kayan baby na zuwa barka kenan? ko kema a hado Miki kayan
naki babyn? tunda da karfina Zan dawo wata kilan ni double shoot ma zanyi tunda
Nima Dan biyu ne Ina da twins sister Aishat".
"Twins sister da gaske?"
"Kin taba ganin nayi Miki karya? wlh mu biyu Ammin mu ta haifa first born dinta,
mun B'ata ne da ita shiyasa bakisanta ba. Amma nan gaba zaki santa ne Amma fa Zaki
Sha surutu Dan sister Aishat parrot ce".
"Amman laifin me tayi maka da zafi haka? Mu namu twins din basa doguwar batawa
gaskiya gashi kaima Ammin irin na Ammah tayi mace da namiji".
"Ki Bari kawai labarin da tsawo sai na dawo ai nace Zaki San duk labarina kaf ba
abinda Zan boye Miki tunda kin sarkafo min zuciya tun kina free matured dinki Kika
Hana duniyata zaman lfy,da farko na dauki irin mutum ya burge ka ne Ashe diban
Karan mahaukaciya Kikayi da gudan tsokar kirjina".
Dariya maganarsa ta bata.
"Au dariya ma kike min ko? bayani zakiyi da yarenki, yanda nayi ta fama da garari
saina fanshe kayana tas idan Zaki shirya ki shirya".
Cuno Baki tayi kamar tana gabansa ta Fara turza kafa tana fadin "Ni yaushe kaga Ina
maka dariya kawai dai... ni banyi maka dariya ba kaifa yayana ne koka manta my big
bro....." Ta wani ja cikin salon da ita kanta Bata San tayi ba.
"Ya salam" ya fada a hankali Dan yanda tayi magana har cikin bargonsa.
"Kinaso ki karya min budget ko?"
Ya jefa Mata tambayar.
"Wane irin budget Zan karya maka kana Nan Ina Nan".
"Idan kina min irin haka ai sai kisa na saki layin Dana hau na tattaro ya nawa ya
nawa ko komo gida ko ba'a gama ba".

"To me nayi daga magana tom shike Nan sai anjima".


"Wlh Kika kashe min Kira sai kinzo Dubai ko a kafa ne kuma saina yi Miki abinda
bazaki manta ba Dan tarihi me kyau Zan kafa Miki ki kashe ki gani, muna hira kina
bani nutsuwa Zaki gudu nida ake yashewa Yan canjina Baki tausaya min ba shine Zaki
tsere ki barni da Mata masu farauta ta ko? Yanzu haka guda uku tun dazu suke
shawagi a gabana suna tunanin irin nasu ne Dan hannu".
Gyara Zama Zahra tayi kirjinta ba dukan tara tara bama uku uku ba.
"Mata kace ko me?"
"Eh Mata Mana bake kina min rowar ganin halalina ba to gashi Nan free sai Wanda
yayi maka ka zabi son ranka, ba nace ki bude data na kalli kayana ba Amma kika Kiya
Kinga kuwa yanzu saina duba na darje na zaba ta rage min dare, koya kikace my
previous?"
Ya Dana Mata kiss ta cikin wayar ya kashe abarsa.
Yana fadin gobe ma idan bace ki bude datar ki qiya, saina kowa Miki kishina ba
gaske kafin na kaiki Ina zakiyi da hujja Amma ki shiga yanzu ai Africa ce da sauran
gyara.

AUREN HUCE HAUSHI

MAMAN FATEEMAH

PAGE 35.

________Yana katse Kiran ya tashi tsam ya nufi masaukinsa laptop dinsa ya janyo
ya shiga aiki sai kusan karfe daya ya kwanta lokaci bayan lokaci sai yayi murmushi
idan ya tuno yanda suka rabu da 'yar gidansa yayi zance mata tana neman tikitawa
kanta lissafi Wai ita me miji, kamar ta wani san dadin mijin,Saida yayi wanka yayi
nafila sannan ya kwanta.
*
Zahra kasake tayi da waya a hannu kamar itace Mahmud din "me yake nufi da zasu
rage Masa dare kenan neman Mata yajeyi?"
Take wata zuciyar tace Masa A'a Yana zolayarki ne da manemin matan ne koda
karfin tuwo saiya nemi wani Abu a jikinki, kauda wannan tunanin tayi daga zuciyar
ta tasan zato zunubi ne, parlour ta koma gurin zilai sukaci gaba da hirarsu sai
kusan Sha daya suka shiga ciki.
Washe gari Zahra Bata tashi da wuri ba sai kusan Sha daya, tun cikin dare bata
Jin Dadi wata irin murdawa mararta ke Mata, tana samun irin wannan pain din duk
karshen wata idan zatayi period Amma wannan yanda yake mata yayi tsanani sosai tun
wurin karfe ukun dare ciwon ya tashe ta farka a gigice, inda Allah ya taimaketa
Bata sakaci ta rasa maganinta duk rintsi Yana tare da ita, a lokacin ta sha cikin
ikon Allah lokaci kalilan ciwon ya lafa ta koma barci da Asuba ma data tashi sallah
da sauki sosai sai Kuma yanzu data farka taji Yana neman dawo Mata, da kyar tayi
wanka ta sake inner wears ta zura rigar matarial marar nauyi ta koma ta kwanta idan
tana wannan yanayin ko turare Bata so sai guda daya kawai body mist ne na
strawberry shi ta fesa ta koma ta kwanta Dan abinci dai baya ciyuwa a irin wannan
yanayin.
Ganin Sha biyu tayi Zahra Bata fito ba yasa zilai nufar bedroom din nata ta
gani anya lafiya kuwa?
Knocking tayi taji Shiru ta qara you taji Shiru Bata kara ba uku ba ta tura
kofar a can tsakiyar gadon ta ganota a kudundune, da sauri ta karasa gaban gadon
tana ambatar sunan ta "Zahra kafiyarki kuwa har Sha biyu ta gota Baki tashi ba abin
Karin ki har ya Fara sanyi?"
Da kyar ta dago ta kalli zilan cikin miryar marar lafiya tace Mata "bana Jin
dadi tun cikin dare marata take ciwo".
"Subahaballahi Kuma Kikayi Shiru Baki fada ba idan haka ne bani da amfani Kenan
ace tun cikin dare kina fama da ciwo ki kasa fada mini, ina maganin da kike Sha
yake na dauko Miki Ni wlh cewa nake tunda ance idan Kikayi aure ze dena, to na
dauka kin rabu dashi yanzu, ai haka wannan likitar ta fada Miki zuwan mu na karshen
ko?".
Kai Zahra ta gyada Mata kawai alamar Eh Dan ita kadai tasan azabar da takeji.
"Fada min Ina maganin yake na dauko Miki"
A hankali tace mata "Na sha".
"Kin sha Kuma marar Bata Dena ciwon ba?"
"Eh" ta fada tana runtse ido saboda azabar ciwo.
Fita zilai tayi da sauri ta koma dakin da aka sauketa ta lakubo keyboard dinta
ta lalubo number Ammah, lokacin tana tare da Abba suna maganar komawa makarantar
Imam Kiran zilan ya shigo.
"Abba Bari na daga Kiran Nan Zilai ce naji ko lafiya".
"In Sha Allahu ma lfy".
Abban ya fada.
"Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu"
Ammah ta fada bayan ta daga wayar daga can zilan ta gaishe da Ammah sannan ta
Dora da fadin "wlh Ammah jikin Zahra ne ba Dadi tun cikin dare ciwon mararta ya
tashi Tasha maganin Kuma a banza shine nace Bari na Kira na fada Miki Koda abinda
zakiyi mata tunda kema Aikinki ne ko Kuma a turo Mana malam Bala ya kaimu Asibiti
taga likitar ta" .
"Ikon Allah! Yanzu ina zahrar?".
"Tana daki tana faman mukususu kamar me nakuda wlh abin gwanin ban tausayinsa".
"To shike Nan ki dubata za'a San yanda za'a yi ki jira".
Ta kashe wayar ta dubi Abba Wanda Shima itan yake kallo, kafin tayi magana ya
rigata.
"Meya samu Uwata naji Kuna magana Bata da lfy ne?"
Ajiyar zuciya Ammah ta sauke "wlh ciwon mararta ne Wai ta tashi tun cikin dare
Tasha maganin da take Sha Amma ba wani cigaba shine zilan tace ko Asibiti zasu koma
suga likitar da take gani Dan munyi expecting idan tayi aure zasu rabu to Kuma a
yanda zilai ta fada min kamarma yafi na baya zafi".
"Ikon Allah! Allah ya saukake Bari a tura musu magaji ya kaisu Asibitin tunda duk
sauran basa Nan sai mu bisu daga baya mu kuma, ai hakan yayi ko?".
Kai ta gyada Masa tana kokarin tashi da nufin tafiya, riko hannunta yayi ya mayar
da ita inda ta tashi dayan Kuma Yana Kiran wayar magaji.
"Ka dauki mota kaje can hayin banki zaka Kai uwata Asibiti".
Ya kashe Kiran yana kallon Ammar.
"Ina zaki Kuma Kika tashi? Ki kwantar da hankalinki in Sha Allah ba wata damuwa
Kika sani ko jika zamuyi kwanan nan"
Ya fada Yana dariya irin tasu ta manya.
Itama Dan murmushi tayi tana fadin Allah yasa".
"Amin yauwa kokefa dauko gyakenki mu bisu wata Kila muje tare tunda gani a gida
araha sai nayi aikin bariki tilas ne".
Zilan Ammah ta Kira ta fada mata su shirya ga magaji Nan ze kaisu Asibitin, Suma
zasu samesu a can..
Dakin Zahra zilan ta koma yanda ta barta haka ta sameta, kusa da ita zilan ta matsa
tana fadin na hado Miki ko ruwan shayi ne kisha Asibiti zamu".
Kai ta girgaiza Mata alamar bazata Sha ba.
"Ki daure ko kadan ne Dan Allah Kinga wata Kila ayi Miki allura gara kici ko kadan
ne".
"Cornflakes".
Abinda ta iya fada Kenan ta koma ta kwanta.
Ba laifi tasha cornflakes din da Dan dama, rolling kawai tayi suka nufi parlour
zilai na rike da ita. Basu jima ba sukaji dirin mota alamar magajin ya karaso
Kenan, zilaice ta bude kofar tun Bai karaso ba direct inda zahrar ke kwance ya nufa
akan two seater.
"Sannu Adda ya jikin naki?"
Da kyar ta cira Kai ta dubeshi tana fadin "da sauki".

"Allah ya Kara sauki, kamota muje kada Rana ta karayi yanzu twenty five
minutes to one fa".
Zalai ta riketa tana tafiya da kyar suka fito compound din Zayyan yana zaune
Yana game a waya tunda bashi da aikinyi a Nan sai zama,ba zato yaga an fito da
Zahra haka, da sauri yayi wurgi da wayar Allah ya taimake kan jacket dinsa ta fada
da sai dai wata ba ita ba, ya nufo gurinsu Yana tambayar "Lafiya meya faru? Oga
kuwa ya sani? sannu" duk a lokaci daya yake jero wadannan tambayoyin da gani a
rude yake.
Magaji ne ya nufi inda yake suka Kara gaisawa Yana farin.
"Ba wani abun damuwa bane Bata Jin Dadi ne zamuje Asibiti kada ka damu".

Zilai magajin ya duba "kun fadawa mujinta kada mu tafi babu sanin sa".
"A'a bamu fada Masa ba ai ko daga bayane an fada Masa yanzu dai muje Asibitin
wannan ma wani Bata lokacin ne".
Da sauri Zayyan ya bude musu gate suka fita yayin da Zayyan din ya dauko wayarsa
Yana Kiran Mahmud.
Ya kirawo shi Amma Sam taqi shiga sai text kawai Zayyan ya tura Masa ya koma ya
zauna yana mamakin ogan nasa na neman gurin Zama a wannan Dan gurin shi ko takura
ma yaga alama bayayi wata sabuwar rayuwa yake shimfidawa cikin kwanciyar hankali.

Direct A&E magaji ya nufa zilai ce ta taimawa Zahra ta fito daga mota suka shiga
ciki shi Kuma magaji ya nufi inda ze karbo file.
Ba jimawa yazo ya kawo file din, bayan duguwar tambayar da wata likita da take on
call tayi Mata ta rubuta Mata magunguna da allurai da drip ana cikin saka Mata ruwa
su Ammah suka shigo dakin, ma'aikatan da masu jiyyar suna ta gaishe da Abba, gaban
gadon Abban yaje ya tsaya sunan ta Abban ya Kira ta bude Ido ta kalli Abba tana
kokarin tashi zaune "A'a uwata koma ki kwanta ya jikin naki?"
"Da sauri Abbana, Ina kwana?"
"Lafiya kalau".
Ammah ce ta matso tana fadin "sannu Ashe ciwon cikin ne ya tashi?"
"Eh Ammah wlh har yafi Wanda nakeyi kamar Zan mutu".
Ta fada tana goge hawayen daya zubo Mata.
"A'a uwata Banda kuka ai kin girma".
Abba ya fada Yana dariya. Itama Zahra dan murmushi tayi ta juya Kai kunya ta kamata
ta.

Abba Bai bar Asibitin ba Saida aka Maida Zahra Aminity ward.
Tun bayan tafiyar su Zahra Zayyan ya kasa tsaye ya kasa zaune, ya nemi number
Mahmud tafi cikin carbi amsa daya balarabiyar da akayi linking da computer ke bashi
wadda ba fashimta yake ba, sai dai hasashe kawai number Bata tafiya take fada Masa.
A gida Abba yayi sallar Azzahar bayan an fito ne ya fadawa Baba malam Zahra tana
Asibiti Bata Jin Dadi.
Cikin nuna jimami Malam yace "tun yaushe take Asibitin ba'a fada min ba, kuma
menene yake damun diyar tawa?".
"Wlh ciwon cikin ne take fama dashi tun cikin dare shine dazu Mai Taya ta Zama ta
kita Asma'u ta fada mata, sai nasa magaji ya Kai su Asibitin sai suka Bata gado Wai
zasuyi Mata hoton cikin da sauran gwaje-gwaje don su fadada bincike akan ciwon
tunda ta jima tana fama da lalurar".
"Ikon Allah! Allah ya Bata lfy yasa kaffara ne, ai da anyi magana tun a bayan da an
Nemo Mata taimakon ciwon Amma yanzu ma Bata baci ba, idan anyi binciken an gano
wane irin ciwo ne a fada mini akwai magungunan ciwon cikin Mata da yawa a gurina in
sha Allah koda tsiron mahaifa ne da sauransu in Sha Allah zasu narke Koda na aikine
zebi jinin al'ada ya narke ya zube".
"To in Sha Allah Zan fadawa Asma'u kome Kenan Zan fada maka".
Sun jima a harabar gidan Abban kafin suyi sallama.
Bayan sallar la'asar malam yasa Habib ya tukashi zuwa Asibitin lokacin da sukaje
Zahra tana barci sun gaisa da Ammah Malam ya jajanta Mata Habib ma ya jajanta Mata
jikin Zahrar Basu dade ba suka tafi.

****

Tun safe da Mahmud ya fita tare da daya daga cikin amuntattun hadimansa na kasar
suka fice sun Kai ziyarorin bazata Dan tono wasu laifuka da ake son binnewa, ya
dakatar da mutum hudu ya sallami mutane biyu wadanda sukayi sama da fadin maqudan
kudade tun bayan rashin sanin inda Mahmud din yake ganin tafiya tayi nisa Kuma baya
bibiyar su Sam sai kawai suka tsunduma cikin dukiyar sukayi dumu dumu a ciki, zuwan
Sameer ne ya bankado badaqalar wadda tafi karfin shi wadda tasa dole Saida Mai
takanas din ya taso, China Kuma issue ne na rufe musu kamfanin laces da materials
da akayi Wanda suke zargin ba'a biya kudin harajin kasa ba a tun farkon bude
kamfanin, Mahmud yayi kokarin tura duk evidence dinsa ta wibeside nasu Amma sunqi
yarda Wanda dole tasa Saida yazo da kansa sannan lamarin ya gyaru.
Sai dare sosai ya dawo masaukinsa yaso ya fita ya dan shaqata beach Amma yayi
matukar gajiya sosai Koda yayi wanka coffee kawai yayi order da snacks, tunda garin
Allah ya waye Bai samu kanshi ba sai yanzu wayarsa ya dauko ya kunna Dan rabon da
ya kunna ta tun jiya, sakonni ne suketa shigowa rututu, amma na Zayyan da Habib su
sukafi daukar hankalinsa lfy? Ya tambayi kansa.
Sakon Zayyan ya fara budewa ai baisan lokacin daya Mike tsaye ba duk gajiyar dake
tare dashi Nan take tayi nata guri, cikin tashin hankali ya Fara lalubar number
din Zayyan cikin kankanin lokaci Kiran ya shiga, Bai saurari gaisuwar da yake Masa
ba ya Fara fad'in "wace irin magana kake min haka? Ashe ajiyekan da nayi bashi da
anfani,tun safe Amma kaqi fada min halin da yarinyar mutane take ciki sai yanzu da
tsohon Daren nan? Kana son ace ban damu da halinda 'yarsu ke ciki ba tunda
throughout yau ban kirata ba nayi busy sosai".."sorry oga wallahi tun lokacin nake
neman wayar ka Bata shiga kwata kwata shine nayi make text".
"Oh shit! Wlh ban bude wayar ba sai yanzu, yanzu ina zahrar?"
"Wallahi Yallabai bansan inda take ba tunda suka fita ban Kara samun wani
information akan komai ba".
Tsaki Mahmud yayi ya datse kiran. Habib ya lalubo ai sakonma bai tsaya dubawa ba ya
Kira shi.
"A gaggauce ya amsa sallamar da gaisawar da Habib din yake Masa.
"Wai meke fatuwa ne da Zahra?".
"Wallahi Nima bani da masaniyar takamaimai kawai dai bayan anyi sallah baba Malam
yace na kaishi Asibiti ya gano jikinta sai a lokacin na Sami labarin Bata da lafiya
ance ciwon ciki ne, lokacin da mukaje tana barci Amma idan an jima zan koma na qara
dubota kome kenan Zan fada maka ka kwantar da hankalinka naji Abban su Yana fadin
Daman tana fama dashi ne Saida na yau yafi zafi fiye dana bayan gaskiya Dan har
hoto da gwaje-gwaje zasuyi Mata inga in Sha Allah ba wani damuwa kome ake ciki Zan
sanar da kai Allah ya Bata lafiya".
"Allahumma Amin".
Ya fada jikinsa a mace da duk ya shiga cikin damuwa.
Number zahrar ya Kira tana ta ringing Amma ba'a dauka ba tsaki yayi tunda yaji haka
yasan wayar na gida Basu dauka ba.
A karo na farko ya Kira wayar Ammah lokacin wayar na hannun Auta Wanda ya biyo mama
da Asabe Asibitin, Dan lokacin da su Ammah suka taho mamar Bata Nan Wai taje
duniyar kanwar Babar su Asaben, shine da suka dawo.Abba ke fada Mata Zahra ba
lafiya suka taho harda Auta, Autan dake kusa da Mama da wayar Amman a.hannu Yana
game na football Mamar dake kusa dashi ta karbi wayar ta mikawa Ammah, batare da
Ammah ta duba wayar ba ta daga tana fadin.
"Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu".
Cikin girmamawa Mahmud ya fara gaishe da Ammah, ita har ga Allah Bata tab'a kawo
Mahmud ze Kira ba.
Dan Jim yayi Yana Jin nauyin tambayar ta Zahra, Jin shirun yayi yawa bayan gaisuwar
yasa Ammar fadin "wa ake nema ne".
"Ammah nine na kirane naji ya jikin Fateemah? wlh ban sani ba tun safe ban bude
wayar ba muna aiki sai yanzu dana bude ake fada min Bata da lafiya Kuna Asibiti,
Dan Allah ayi hakuri in Sha Allah hakan bazata fatuwa ba".
Ammah ji tayi kamar ruwa ya cinyeta Ashe sirikinta ne wlh Sam bata Gane shi ba.
Ciki Jin kunya da Kara Ammah tace Masa "ba komai ai jikinta da sauki yanzu ma barci
takeyi, ya akayi suka fada maka haba ka kwantar da hankalinka Daman takanyi irin
wannan ciwon lokaci lokaci sai dai wannan ne ya Dan matsa Mata sukayi admitting din
ta zasu bincike a Kai".
Ammar ta fada tana dan jin nauyinsa.
"To Ammah nagode in Sha Allah da safe Sameer ze shigo zasuje Kano Nan Aminu Kano
zasu dubata sosai tunda suna da Gynecologist consultant Ina ga kamar hakan zaifi
can suna da kayan aiki na zamani, Zan Kira Abba da Baba Malam muyi maganar, na gode
Allah ya Bata lafiya".
"Allahumma Amin, Allah ya bada sa'a yayi Albarka".
Sukayi sallama.
Bayan sunyi sallama Ammah wayar tabi da kallo tana mamakin yanda yake magana da ita
tamkar mahaifiyar shi, ya kama sunanta radau.
Mama ce ta kalli Ammah tana fad'in "ko mijin nata be? Naji kina masa bayanin
yanayin ciwon nata gashi abin takaicin tun ba'aje ko Ina ba ya tsallake ya bar
yarinya da wahala, Allah dai yasa ba juduwa yayi ba ya barta da jangwam yanda aka
Fara 'yan ciwace ciwacen Nan ai karshen maganar ace ciki ya bayyana shi Kuma yayi
masa wuri tunda Daman tsintacciyar magen ce Bata mage ya sulale yabar gari naji
ance harda motarta ya tafi Kinga ribar kafa Kenan".

Duk surutun da Mama keyi akan Zahra ko kallon ta Ammah batayi ba Dan tasan tana
fada ne dan ta Bata Mata Rai kawai, Zilai ma Mai aikin su tana tsaye kusa da Zahra
tana gyara Mata hannunta da aka saka mata drip, itama ko tari be kunce Mata ba
bata tofa tata ba, to me zata ce maganar ba ta ta bace.
Jin ba Wanda ya tofawa Mama ko A a cikin maganarta yasa Asabe cewa.
"Wallahi kuwa mama Allah abin tsoro mutum abin tsoro daman nasan in ba wani ikon
Allah ba yaron Nan guduwa zeyi yayi gaba kinsan irinsu Yan hujja ne ba wani Zama
zeyi na din-din-din ba a garin Nan, abin gudun ma ya jonawa yarinya ala kakai ya
tafi ya barta da 'ya'ya, Kuma ki duba kiga yaro Nan a wanke yake Kar bashi da duhun
jahilci ko kauyenci ko qanqani haka kawai ya jonawa yarinya alakakai ya gudu ya
barta, idan tafiya ta Mike wata Ranar har azo ana yiwa yaro gorin mahaifi ga babu
jinjinan dangi kana ji a sheganta yaro
ko yarinya".
Har Zilai ta baro bakin gadon da zimmar maida martani, sai maganar Zahra suka juyo
suka juyo tana kallon Asabe Tana fad'in "lafiya kalau muka rabu, bai Kuma bar
garin Nan ba Sai da ya fada min salinsa da iyayensa daga karshe ma mutum ya aje min
saboda yana yin rayuwa koda ta Allah ta kasance shine ze kaini har dakin
mahaifiyar sa Kinga kuwa ai bani da damuwa a Kan lamarin".

AUREN HUCE HAUSHI

MAMAN FATEEMAH

PAGE 35.

________Yana katse Kiran ya tashi tsam ya nufi masaukinsa laptop dinsa ya janyo
ya shiga aiki sai kusan karfe daya ya kwanta lokaci bayan lokaci sai yayi murmushi
idan ya tuno yanda suka rabu da 'yar gidansa yayi zance mata tana neman tikitawa
kanta lissafi Wai ita me miji, kamar ta wani san dadin mijin,Saida yayi wanka yayi
nafila sannan ya kwanta.
*
Zahra kasake tayi da waya a hannu kamar itace Mahmud din "me yake nufi da zasu
rage Masa dare kenan neman Mata yajeyi?"
Take wata zuciyar tace Masa A'a Yana zolayarki ne da manemin matan ne koda
karfin tuwo saiya nemi wani Abu a jikinki, kauda wannan tunanin tayi daga zuciyar
ta tasan zato zunubi ne, parlour ta koma gurin zilai sukaci gaba da hirarsu sai
kusan Sha daya suka shiga ciki.
Washe gari Zahra Bata tashi da wuri ba sai kusan Sha daya, tun cikin dare bata
Jin Dadi wata irin murdawa mararta ke Mata, tana samun irin wannan pain din duk
karshen wata idan zatayi period Amma wannan yanda yake mata yayi tsanani sosai tun
wurin karfe ukun dare ciwon ya tashe ta farka a gigice, inda Allah ya taimaketa
Bata sakaci ta rasa maganinta duk rintsi Yana tare da ita, a lokacin ta sha cikin
ikon Allah lokaci kalilan ciwon ya lafa ta koma barci da Asuba ma data tashi sallah
da sauki sosai sai Kuma yanzu data farka taji Yana neman dawo Mata, da kyar tayi
wanka ta sake inner wears ta zura rigar matarial marar nauyi ta koma ta kwanta idan
tana wannan yanayin ko turare Bata so sai guda daya kawai body mist ne na
strawberry shi ta fesa ta koma ta kwanta Dan abinci dai baya ciyuwa a irin wannan
yanayin.
Ganin Sha biyu tayi Zahra Bata fito ba yasa zilai nufar bedroom din nata ta
gani anya lafiya kuwa?
Knocking tayi taji Shiru ta qara you taji Shiru Bata kara ba uku ba ta tura
kofar a can tsakiyar gadon ta ganota a kudundune, da sauri ta karasa gaban gadon
tana ambatar sunan ta "Zahra kafiyarki kuwa har Sha biyu ta gota Baki tashi ba abin
Karin ki har ya Fara sanyi?"
Da kyar ta dago ta kalli zilan cikin miryar marar lafiya tace Mata "bana Jin
dadi tun cikin dare marata take ciwo".
"Subahaballahi Kuma Kikayi Shiru Baki fada ba idan haka ne bani da amfani Kenan
ace tun cikin dare kina fama da ciwo ki kasa fada mini, ina maganin da kike Sha
yake na dauko Miki Ni wlh cewa nake tunda ance idan Kikayi aure ze dena, to na
dauka kin rabu dashi yanzu, ai haka wannan likitar ta fada Miki zuwan mu na karshen
ko?".
Kai Zahra ta gyada Mata kawai alamar Eh Dan ita kadai tasan azabar da takeji.
"Fada min Ina maganin yake na dauko Miki"
A hankali tace mata "Na sha".
"Kin sha Kuma marar Bata Dena ciwon ba?"
"Eh" ta fada tana runtse ido saboda azabar ciwo.
Fita zilai tayi da sauri ta koma dakin da aka sauketa ta lakubo keyboard dinta
ta lalubo number Ammah, lokacin tana tare da Abba suna maganar komawa makarantar
Imam Kiran zilan ya shigo.
"Abba Bari na daga Kiran Nan Zilai ce naji ko lafiya".
"In Sha Allahu ma lfy".
Abban ya fada.
"Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu"
Ammah ta fada bayan ta daga wayar daga can zilan ta gaishe da Ammah sannan ta
Dora da fadin "wlh Ammah jikin Zahra ne ba Dadi tun cikin dare ciwon mararta ya
tashi Tasha maganin Kuma a banza shine nace Bari na Kira na fada Miki Koda abinda
zakiyi mata tunda kema Aikinki ne ko Kuma a turo Mana malam Bala ya kaimu Asibiti
taga likitar ta" .
"Ikon Allah! Yanzu ina zahrar?".
"Tana daki tana faman mukususu kamar me nakuda wlh abin gwanin ban tausayinsa".
"To shike Nan ki dubata za'a San yanda za'a yi ki jira".
Ta kashe wayar ta dubi Abba Wanda Shima itan yake kallo, kafin tayi magana ya
rigata.
"Meya samu Uwata naji Kuna magana Bata da lfy ne?"
Ajiyar zuciya Ammah ta sauke "wlh ciwon mararta ne Wai ta tashi tun cikin dare
Tasha maganin da take Sha Amma ba wani cigaba shine zilan tace ko Asibiti zasu koma
suga likitar da take gani Dan munyi expecting idan tayi aure zasu rabu to Kuma a
yanda zilai ta fada min kamarma yafi na baya zafi".
"Ikon Allah! Allah ya saukake Bari a tura musu magaji ya kaisu Asibitin tunda duk
sauran basa Nan sai mu bisu daga baya mu kuma, ai hakan yayi ko?".
Kai ta gyada Masa tana kokarin tashi da nufin tafiya, riko hannunta yayi ya mayar
da ita inda ta tashi dayan Kuma Yana Kiran wayar magaji.
"Ka dauki mota kaje can hayin banki zaka Kai uwata Asibiti".
Ya kashe Kiran yana kallon Ammar.
"Ina zaki Kuma Kika tashi? Ki kwantar da hankalinki in Sha Allah ba wata damuwa
Kika sani ko jika zamuyi kwanan nan"
Ya fada Yana dariya irin tasu ta manya.
Itama Dan murmushi tayi tana fadin Allah yasa".
"Amin yauwa kokefa dauko gyakenki mu bisu wata Kila muje tare tunda gani a gida
araha sai nayi aikin bariki tilas ne".
Zilan Ammah ta Kira ta fada mata su shirya ga magaji Nan ze kaisu Asibitin, Suma
zasu samesu a can..
Dakin Zahra zilan ta koma yanda ta barta haka ta sameta, kusa da ita zilan ta matsa
tana fadin na hado Miki ko ruwan shayi ne kisha Asibiti zamu".
Kai ta girgaiza Mata alamar bazata Sha ba.
"Ki daure ko kadan ne Dan Allah Kinga wata Kila ayi Miki allura gara kici ko kadan
ne".
"Cornflakes".
Abinda ta iya fada Kenan ta koma ta kwanta.
Ba laifi tasha cornflakes din da Dan dama, rolling kawai tayi suka nufi parlour
zilai na rike da ita. Basu jima ba sukaji dirin mota alamar magajin ya karaso
Kenan, zilaice ta bude kofar tun Bai karaso ba direct inda zahrar ke kwance ya nufa
akan two seater.
"Sannu Adda ya jikin naki?"
Da kyar ta cira Kai ta dubeshi tana fadin "da sauki".

"Allah ya Kara sauki, kamota muje kada Rana ta karayi yanzu twenty five
minutes to one fa".
Zalai ta riketa tana tafiya da kyar suka fito compound din Zayyan yana zaune
Yana game a waya tunda bashi da aikinyi a Nan sai zama,ba zato yaga an fito da
Zahra haka, da sauri yayi wurgi da wayar Allah ya taimake kan jacket dinsa ta fada
da sai dai wata ba ita ba, ya nufo gurinsu Yana tambayar "Lafiya meya faru? Oga
kuwa ya sani? sannu" duk a lokaci daya yake jero wadannan tambayoyin da gani a
rude yake.
Magaji ne ya nufi inda yake suka Kara gaisawa Yana farin.
"Ba wani abun damuwa bane Bata Jin Dadi ne zamuje Asibiti kada ka damu".

Zilai magajin ya duba "kun fadawa mujinta kada mu tafi babu sanin sa".
"A'a bamu fada Masa ba ai ko daga bayane an fada Masa yanzu dai muje Asibitin
wannan ma wani Bata lokacin ne".
Da sauri Zayyan ya bude musu gate suka fita yayin da Zayyan din ya dauko wayarsa
Yana Kiran Mahmud.
Ya kirawo shi Amma Sam taqi shiga sai text kawai Zayyan ya tura Masa ya koma ya
zauna yana mamakin ogan nasa na neman gurin Zama a wannan Dan gurin shi ko takura
ma yaga alama bayayi wata sabuwar rayuwa yake shimfidawa cikin kwanciyar hankali.

Direct A&E magaji ya nufa zilai ce ta taimawa Zahra ta fito daga mota suka shiga
ciki shi Kuma magaji ya nufi inda ze karbo file.
Ba jimawa yazo ya kawo file din, bayan duguwar tambayar da wata likita da take on
call tayi Mata ta rubuta Mata magunguna da allurai da drip ana cikin saka Mata ruwa
su Ammah suka shigo dakin, ma'aikatan da masu jiyyar suna ta gaishe da Abba, gaban
gadon Abban yaje ya tsaya sunan ta Abban ya Kira ta bude Ido ta kalli Abba tana
kokarin tashi zaune "A'a uwata koma ki kwanta ya jikin naki?"
"Da sauri Abbana, Ina kwana?"
"Lafiya kalau".
Ammah ce ta matso tana fadin "sannu Ashe ciwon cikin ne ya tashi?"
"Eh Ammah wlh har yafi Wanda nakeyi kamar Zan mutu".
Ta fada tana goge hawayen daya zubo Mata.
"A'a uwata Banda kuka ai kin girma".
Abba ya fada Yana dariya. Itama Zahra dan murmushi tayi ta juya Kai kunya ta kamata
ta.

Abba Bai bar Asibitin ba Saida aka Maida Zahra Aminity ward.
Tun bayan tafiyar su Zahra Zayyan ya kasa tsaye ya kasa zaune, ya nemi number
Mahmud tafi cikin carbi amsa daya balarabiyar da akayi linking da computer ke bashi
wadda ba fashimta yake ba, sai dai hasashe kawai number Bata tafiya take fada Masa.
A gida Abba yayi sallar Azzahar bayan an fito ne ya fadawa Baba malam Zahra tana
Asibiti Bata Jin Dadi.
Cikin nuna jimami Malam yace "tun yaushe take Asibitin ba'a fada min ba, kuma
menene yake damun diyar tawa?".
"Wlh ciwon cikin ne take fama dashi tun cikin dare shine dazu Mai Taya ta Zama ta
kita Asma'u ta fada mata, sai nasa magaji ya Kai su Asibitin sai suka Bata gado Wai
zasuyi Mata hoton cikin da sauran gwaje-gwaje don su fadada bincike akan ciwon
tunda ta jima tana fama da lalurar".
"Ikon Allah! Allah ya Bata lfy yasa kaffara ne, ai da anyi magana tun a bayan da an
Nemo Mata taimakon ciwon Amma yanzu ma Bata baci ba, idan anyi binciken an gano
wane irin ciwo ne a fada mini akwai magungunan ciwon cikin Mata da yawa a gurina in
sha Allah koda tsiron mahaifa ne da sauransu in Sha Allah zasu narke Koda na aikine
zebi jinin al'ada ya narke ya zube".
"To in Sha Allah Zan fadawa Asma'u kome Kenan Zan fada maka".
Sun jima a harabar gidan Abban kafin suyi sallama.
Bayan sallar la'asar malam yasa Habib ya tukashi zuwa Asibitin lokacin da sukaje
Zahra tana barci sun gaisa da Ammah Malam ya jajanta Mata Habib ma ya jajanta Mata
jikin Zahrar Basu dade ba suka tafi.

****

Tun safe da Mahmud ya fita tare da daya daga cikin amuntattun hadimansa na kasar
suka fice sun Kai ziyarorin bazata Dan tono wasu laifuka da ake son binnewa, ya
dakatar da mutum hudu ya sallami mutane biyu wadanda sukayi sama da fadin maqudan
kudade tun bayan rashin sanin inda Mahmud din yake ganin tafiya tayi nisa Kuma baya
bibiyar su Sam sai kawai suka tsunduma cikin dukiyar sukayi dumu dumu a ciki, zuwan
Sameer ne ya bankado badaqalar wadda tafi karfin shi wadda tasa dole Saida Mai
takanas din ya taso, China Kuma issue ne na rufe musu kamfanin laces da materials
da akayi Wanda suke zargin ba'a biya kudin harajin kasa ba a tun farkon bude
kamfanin, Mahmud yayi kokarin tura duk evidence dinsa ta wibeside nasu Amma sunqi
yarda Wanda dole tasa Saida yazo da kansa sannan lamarin ya gyaru.
Sai dare sosai ya dawo masaukinsa yaso ya fita ya dan shaqata beach Amma yayi
matukar gajiya sosai Koda yayi wanka coffee kawai yayi order da snacks, tunda garin
Allah ya waye Bai samu kanshi ba sai yanzu wayarsa ya dauko ya kunna Dan rabon da
ya kunna ta tun jiya, sakonni ne suketa shigowa rututu, amma na Zayyan da Habib su
sukafi daukar hankalinsa lfy? Ya tambayi kansa.
Sakon Zayyan ya fara budewa ai baisan lokacin daya Mike tsaye ba duk gajiyar dake
tare dashi Nan take tayi nata guri, cikin tashin hankali ya Fara lalubar number
din Zayyan cikin kankanin lokaci Kiran ya shiga, Bai saurari gaisuwar da yake Masa
ba ya Fara fad'in "wace irin magana kake min haka? Ashe ajiyekan da nayi bashi da
anfani,tun safe Amma kaqi fada min halin da yarinyar mutane take ciki sai yanzu da
tsohon Daren nan? Kana son ace ban damu da halinda 'yarsu ke ciki ba tunda
throughout yau ban kirata ba nayi busy sosai".."sorry oga wallahi tun lokacin nake
neman wayar ka Bata shiga kwata kwata shine nayi make text".
"Oh shit! Wlh ban bude wayar ba sai yanzu, yanzu ina zahrar?"
"Wallahi Yallabai bansan inda take ba tunda suka fita ban Kara samun wani
information akan komai ba".
Tsaki Mahmud yayi ya datse kiran. Habib ya lalubo ai sakonma bai tsaya dubawa ba ya
Kira shi.
"A gaggauce ya amsa sallamar da gaisawar da Habib din yake Masa.
"Wai meke fatuwa ne da Zahra?".
"Wallahi Nima bani da masaniyar takamaimai kawai dai bayan anyi sallah baba Malam
yace na kaishi Asibiti ya gano jikinta sai a lokacin na Sami labarin Bata da lafiya
ance ciwon ciki ne, lokacin da mukaje tana barci Amma idan an jima zan koma na qara
dubota kome kenan Zan fada maka ka kwantar da hankalinka naji Abban su Yana fadin
Daman tana fama dashi ne Saida na yau yafi zafi fiye dana bayan gaskiya Dan har
hoto da gwaje-gwaje zasuyi Mata inga in Sha Allah ba wani damuwa kome ake ciki Zan
sanar da kai Allah ya Bata lafiya".
"Allahumma Amin".
Ya fada jikinsa a mace da duk ya shiga cikin damuwa.
Number zahrar ya Kira tana ta ringing Amma ba'a dauka ba tsaki yayi tunda yaji haka
yasan wayar na gida Basu dauka ba.
A karo na farko ya Kira wayar Ammah lokacin wayar na hannun Auta Wanda ya biyo mama
da Asabe Asibitin, Dan lokacin da su Ammah suka taho mamar Bata Nan Wai taje
duniyar kanwar Babar su Asaben, shine da suka dawo.Abba ke fada Mata Zahra ba
lafiya suka taho harda Auta, Autan dake kusa da Mama da wayar Amman a.hannu Yana
game na football Mamar dake kusa dashi ta karbi wayar ta mikawa Ammah, batare da
Ammah ta duba wayar ba ta daga tana fadin.
"Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu".
Cikin girmamawa Mahmud ya fara gaishe da Ammah, ita har ga Allah Bata tab'a kawo
Mahmud ze Kira ba.
Dan Jim yayi Yana Jin nauyin tambayar ta Zahra, Jin shirun yayi yawa bayan gaisuwar
yasa Ammar fadin "wa ake nema ne".
"Ammah nine na kirane naji ya jikin Fateemah? wlh ban sani ba tun safe ban bude
wayar ba muna aiki sai yanzu dana bude ake fada min Bata da lafiya Kuna Asibiti,
Dan Allah ayi hakuri in Sha Allah hakan bazata fatuwa ba".
Ammah ji tayi kamar ruwa ya cinyeta Ashe sirikinta ne wlh Sam bata Gane shi ba.
Ciki Jin kunya da Kara Ammah tace Masa "ba komai ai jikinta da sauki yanzu ma barci
takeyi, ya akayi suka fada maka haba ka kwantar da hankalinka Daman takanyi irin
wannan ciwon lokaci lokaci sai dai wannan ne ya Dan matsa Mata sukayi admitting din
ta zasu bincike a Kai".
Ammar ta fada tana dan jin nauyinsa.
"To Ammah nagode in Sha Allah da safe Sameer ze shigo zasuje Kano Nan Aminu Kano
zasu dubata sosai tunda suna da Gynecologist consultant Ina ga kamar hakan zaifi
can suna da kayan aiki na zamani, Zan Kira Abba da Baba Malam muyi maganar, na gode
Allah ya Bata lafiya".
"Allahumma Amin, Allah ya bada sa'a yayi Albarka".
Sukayi sallama.
Bayan sunyi sallama Ammah wayar tabi da kallo tana mamakin yanda yake magana da ita
tamkar mahaifiyar shi, ya kama sunanta radau.
Mama ce ta kalli Ammah tana fad'in "ko mijin nata be? Naji kina masa bayanin
yanayin ciwon nata gashi abin takaicin tun ba'aje ko Ina ba ya tsallake ya bar
yarinya da wahala, Allah dai yasa ba juduwa yayi ba ya barta da jangwam yanda aka
Fara 'yan ciwace ciwacen Nan ai karshen maganar ace ciki ya bayyana shi Kuma yayi
masa wuri tunda Daman tsintacciyar magen ce Bata mage ya sulale yabar gari naji
ance harda motarta ya tafi Kinga ribar kafa Kenan".

Duk surutun da Mama keyi akan Zahra ko kallon ta Ammah batayi ba Dan tasan tana
fada ne dan ta Bata Mata Rai kawai, Zilai ma Mai aikin su tana tsaye kusa da Zahra
tana gyara Mata hannunta da aka saka mata drip, itama ko tari be kunce Mata ba
bata tofa tata ba, to me zata ce maganar ba ta ta bace.
Jin ba Wanda ya tofawa Mama ko A a cikin maganarta yasa Asabe cewa.
"Wallahi kuwa mama Allah abin tsoro mutum abin tsoro daman nasan in ba wani ikon
Allah ba yaron Nan guduwa zeyi yayi gaba kinsan irinsu Yan hujja ne ba wani Zama
zeyi na din-din-din ba a garin Nan, abin gudun ma ya jonawa yarinya ala kakai ya
tafi ya barta da 'ya'ya, Kuma ki duba kiga yaro Nan a wanke yake Kar bashi da duhun
jahilci ko kauyenci ko qanqani haka kawai ya jonawa yarinya alakakai ya gudu ya
barta, idan tafiya ta Mike wata Ranar har azo ana yiwa yaro gorin mahaifi ga babu
jinjinan dangi kana ji a sheganta yaro
ko yarinya".
Har Zilai ta baro bakin gadon da zimmar maida martani, sai maganar Zahra suka juyo
suka juyo tana kallon Asabe Tana fad'in "lafiya kalau muka rabu, bai Kuma bar
garin Nan ba Sai da ya fada min salinsa da iyayensa daga karshe ma mutum ya aje min
saboda yana yin rayuwa koda ta Allah ta kasance shine ze kaini har dakin
mahaifiyar sa Kinga kuwa ai bani da damuwa a Kan lamarin".

✨✨✨

AUREN HUCE HAUSHI

✨✨✨

MAMAN FATEEMAH.

Page 36

______Zahra tana Gama fadawa Asaben abinda ke cikinta ta juya musu baya, ko
banza bazata kwana da fushin zuciya ba, dan tasan idan ba ita tayi magana ba Babu
abinda Ammah zata ce Dan sau da yawa idan irin haka ta faru ko kallon Mama batayi
sai dai ta bawa banza ajiyarta.
Daga Asaben har Mama ba Wanda ya Kara magana,haka Ammar ma da Zilai ba Wanda ko
tari ya kuncewa, Auta kuwa wayar mamar ya dauka yaci gaba da sha'aninsa.
Shiru dakin ya dauka kamar mutuwa ta ratsa, sallamar Abdul Hakeem da Abba ta katse
shirun cikin nuna tsantsar duniyanci Mama ta tashi da sauri tana fadin "Abba har
kun karaso sannu da Zuwa" tana gyara Masa kujerar kusa da gadon.
Sai da ya zauna sannan ya amsa gaisuwar dasu Zilai da Asabe ke Masa suna jajanta
masa, suka gaisa da Abdul Hakeem sannan suka fice daga dakin.
Mama ce ta Fara gaishe da Abban kafin Ammah ma ta gaishe shi, sannan Abdul Hakeem
ya gaisu dasu Ammar Yana tambayar Mai jikin.
Zahar ce ta juyo tana fadin. "Abbana sannu da Zuwa, ina yini?".
"Yauwa uwata lafiya kalau Alhamdulillahi jiki yayi kyau".
"Eh Abba Daman Kai nake jira kazo kayi musu magana su sallameni mu tafi Nina warke
na gaji da Asibitin tunda sunyi min hoton da gwajin da safe mun dawo mu karba bana
son kwanan gurin Nan".
Ta fada tana hade rai.
"Eh Nima abinda ya taso ni Kenan maganar tafiyar taku gidan ne Dan yanzu haka daga
office din doctor din muke sun bamu referral Zuwa Aminu Kano kamar yanda mijinki ya
bukata yace da safe zaku tafi kiga gynecology doctor ayi bincke tunda ance kin jima
kina fama da matsalar".
Kafin Ammah tayi magana Mama ta rigata.
"Wane irin Kano Kuma ana zaune lafiya, Wai ciwon har ya Kai haka ne idan Asibitin
ake son canzawa aje Bauchi Mana Amma har kano akan ciwon mara kawai".
Dan murmushi Ammah tayi Bata ce komai ba.
Abban ne yace. "Yanzu kina nufin na Kira shi nace masa abinda ya fada baze yuwu ba
Kenan ko Kuma Yaya kike son ayi?".
Shiru tayi Bata ce komai ba. Ammah ya kalla "kinyi Shiru ko kema hakan ne nufinki".
Kai ta girgaiza tana fadin "A'a tunda ga yanda ya fada ai shike da iko da
matarsa ita da waye zasu tafi kanon?".
"Yace Sameer ne zezo sai zilai ta rakata haka dai ya fada min yanzu da Daren nan"
" To Allah ya kaimu yanzu tafiya zamuyi ke Nan?".
"Eh haka ne, ku kuje Abdul Hakeem ya mayar daku gida kafin ya dawo ruwan ya Kare
sai na raka uwata gida" ya fada Yana murmushi.
Sororo Mama tayi Jin Abba da kansa ze maida su Zahra gida.
Badai ta tofa ba Amma a ranta taji ba dadi. Tun kafin Ammah ta dauko hand bag dinta
Mama ta fice daga dakin.

******
MAHMUD
Bayan sun gama waya dasu Abba, Sameer ya Kira harta katse ba'a dauka ba sake Kiran
yayi tana Fara ringing ta dauka.
"Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu".
Ya fada Yana Zama kusa da Fateeha tana shayar da jaririn su.
Daga can Mahmud ya amsa sallamar ya Dora da fadin "gobe in Allah ya kaimu ka shiga
Azare ka taho da madam zataga doctor a Nan kanon na Kira doctor Haseena za'a kawo
patient dina".
"Doctor Haseena fa! ita zata duba maka madam din?".
"Eh Mana ko da matsala ne?".
"A'a gani nayi kada taga anyi Mata cin fuska".
"Ba wani damuwa kawai,do what I said".
"Ok. In Sha Allah".
"Kada ka kaisu gidanka a kaisu gidan dake Nan DAWAKI ROAD su zauna har su Gama
abinda zasuyi su koma".
"Kana ganin Bai musu girma ba kuwa? dana karkasara aka kaisu yafi kusa da
Asibitin ma akan na Nasarawa GRA".
"A Nan nake son ta zauna kake maganar girma har wani babban gida ne ka barta ta
saba da Zama a irinsu tun yanzu Kai dai kasan kuma abinda zaka fada Mata, a Kai
musu duk abinda ya kamata sai dai na fada ba kayi komai kawai, ka fadawa momi ta
Basu house maid daya su hadu da tata sai su ringa aikin tare, kayan sakawa dai
nasan ba matsala ka Kira Rukayya ta duba abinda ya kamata sai taje ta sawo, ka Bata
card din master bedroom na kasa ta sauka a nan.
"Shike Nan za'ayi yanda kace, amma baka tunanin taga wata shaida data danganceka a
gidan?"
"Gaskiya bana tunanin akwai wata alama dake alamtani da gidan".
"Anyway, Allah ya kaimu goben, takwaranka na gaisheka".
"Oh sorry a shafa kansa sai nazo ganinsa, kaina ne ya dauki zafi".
Dan murmushi Sameer ya kashe Kiran Yana kallon Fateeha dake Masa kallon Karin
bayani.
"Oga ne, Kinga yanda ya shiga damuwa kuwa nifa Banga abinda oga ya damu dashi ba
irin yarinyar Nan idan Kika cire Iyayensa to ba na biyunta, ai ban Gama sarewa da
lamarin sa ba saida ya nemi guri ya zauna a dakin kofar gida na almajirai duk da
gurin bashi da wani aibu". Baki bude Fateeha ta bi Sameer da kallo "dakin Almajirai
fa tace shi ogan da kansa? Tab lamarin Azimun ne, Allah ya bamu ko Rabin yanda tayi
sa'ar sace zuciyar jarimi kamarsa Wanda Mata ko kallo basu isheshi ba".
Lakuce Mata kumatu yayi Yana fadin.
"Waya fada miki ba'a Miki so irin Wanda ake mata?" 'yar dariya tayi kawai tasan
zance ne inji 'yan magana

*******

Lokacin da Ya Abdul Hakeem ya dawo ruwan ya qare har an cire Mata.


Cikin marairaita Zahra ta kalli Abban da Ya Abdul Hakeem.
"Dan Allah Abba ka tafi Dani gida wlh jiya nasha wahala gashi ba kowa a kusa dani
kada na mutu Ni kadai a daki".
Saita saka Masa kuka.
Baki Ya Abdul Hakeem ya bude alamar mamaki.
"Ke! Amma wallahi wannan dai abun kunya ne ki wani kama kuka, kin manta yanzu ba da
bane kema fa soon Zaki Zama uwa".
"Ungo Abdul uwata kake fadawa haka a gabana? Fita ka Kirawo zulaihatu ta tattara
musu magungunan Nan sai mu tafi can din"..

Dariya yayi ya fice Yana mamakin Abba yanda yake nunawa Zahra soyayya fiye da kowa.
Ba zato ba tsammani Amma taga zilai ta shigo da Kaya a hannu Zahra na biye da ita.
"A'a ku kuma ya haka Naga Abba yace ze rakaki gida sai Kuma gaku a nan?"
Maganar Abban Ammah taji a bakin kofar parloun.
"Ni nace ta taho gida tunda batajin dadi Kuma gida su kadai, gashi Mai gidan nata
yace goben zasu wuce kanon gara su kwana a Nan kawai tunda ke dai ba can zaki bita
ba gara su tafi a gaban ki".
"Ok, ai ban sani ba nayi tunanin ko gaban kanta tayi nasanta da kulafucin gida
ganin ta samu dama zata iya fakewa da haka ta taho kaima Abba kasan halinta"..
D'an Bata fuska tayi "Kai Ammah Dan Allah fa....."
"Kinga uwarta wuce ki kwanta ki huta Keda Baki da lafiya gida dai ai na danki ne,
ba Mai hanaki shigowa Zan Kira shi Mahmud din na fada masa ".
"To Abba na gode".
Ta fada tana shigewa cikin Zilai ta bita da ledar magungunan ta.

Abban Bai jima ba ya fice saboda ya baro mutane masu son ganinsa da yawa a kofa.
A bakin kofar bedroom din Ammah suka had'u da zilai tana kokarin fitowa.
"Ku kuma sai koyo gudun hijira bakwa tsoron maganar mutane masu jiran k'iris su
karawa miya gishiri?".
"Kayya Ammah idan za'a biyewa maganar mutane ai ko ruwa ruwa ka shiga sunce ka tada
k'ura, Kuma ma waye ya ganta Kuma gobe da safe zamu wuce Kano idan Allah ya dawo
damu ta wuce dakinta".

Zahra na shiga ta fada toilet Dan babu abinda take bukata sama da wanka du ji take
jikinta na warin Asaibi.
Ta jima tana zubawa kanta ruwa kafin ta fito, sabuwar rigar barci ta dauko cikin
kayan Ammah ta saka, ta dauko zumbuelen hijabin Ammah ta Fara sallah.
Ammah ce ta shigo dakin lokacin Zahra ta Idar da sallah Tana addu'a, sai da ta
shafa sannan ta juyo tana fadin.
"Sannu da dawowa Ammah".
"A'a ke za'a yiwa sannu, ya jikin naki?".
"Da sauki sosai nifa da Abba ze fada Masa bama sai munje wani Kano ba, na warke
tunda Daman na Saba duk wata inayi wannan ne kawai ya matsa min sosai".
"Kamar Yaya Abba ya fada Masa shi wa za'a fadawa?".
Ammah ta fada tana kallon zahrar, Baki ta turo tana fadin. "kema Ammah kin sani fa
kowa nake nufi".
Dan murmushi tayi kawai.
"Ki Kira ki fada Masa bazakije ba Mana sai Abba ne ze Miki tafinta, tunda yace ga
yanda yake so ai haka Zaki hakura kuje a duba ki tunda Naga alama Nan din be kwanta
Masa ba, Kuma dazu naji kina maidawa Asabe har da Mama magana tona Hana kada na
k'ara Jin makamanciyar magana irinta daga bakinki, ki bar mutum da halinsa kedai ki
Zama me kauda Kai kawai ki Kuma rike Addu'a takobin mumuni ce kuma hassada ga Mai
rabo taki ce".
"Kiyi hakuri Ammah in Sha Allah bazan Kara tankawa kowa ba,gani nayi basuji kunyar
maganar a gabanki ba shi yasa na rama Nima".
Knockig da Sallamar Abdul Hakeem ce ta dakatar da abinda Ammah zata fada. Ammah ce
ta amsa sallamar ta bashi uzinin shigowa.
Sannu da dare ya Kara yiwa Ammah sannan ya mikawa Zahra wayarsa dake Hannunsa da
alama vedio call yakeyi, Yana fadar "gashi Mahmud zeyi magana dake".
A d'an kaikaice ta kalli gafen da Ammah take kafin ta Mika hannu ta karbi wayar.
Tana karba Ya Abdul Hakeem ya juya, Ammah tabi bayansa tana Masa maganar danyar
Madarar da akace ya Aiko da ita da yamma lokacin tana Asibiti.
Saida Zahra ta tabbatar sun fice gaba daya daga dakin sannan ta dubi
Screen din wayar fuskarsa ta gani Yana kallon ta sai taga yayi wani zuru-zuru kamar
Wanda yayi ciwo sai hancinsa ya Kara fitowa zuwat dashi hakensa ma ya qaru.
"A hankalin tayi masa sallama tana fadin "Ya M baka da lafiya ne Naga ka rame?".
Bushashshen lebensa ya da tura cikin Bakinsa ya lumshe idanunsa tun lokacin da aka
fada Masa Bata da lafiya bai samu peace of mind ba sai yanzu daya ganta. Dan ita ke
ciwon Amma shi keda zulumin da ramar Dan tun daga lokacin zuwa yanzu daya ganta
Baya Jin yaci wani Abu na kirki a cikinsa.
A hankali ya bude idonsa ya Dora akan tata fuskar dake kallonsa, wani yarrrr taji
da suka hada idon.
Cikin tsantsar kasala da jigata ya bude Bakinsa a hankali yace.
"My previous hankalina ya tashi, wallahi gani nakeyi kamar Zan rasaki, ya jikin
naki? Kuma tun yaushe ciwon ya kamaki Baki fada min ba? sai Zayyan ne yayi min text
Wai an wuce dake Asibiti, kinsan kuwa yanda hankalina ya tashi? Daman kina yin irin
hakan ne ko yanzu ya Fara Miki?".
Dan walainiya tayi da idanunta tana fadin " Naji fa sauki Daman inayi kawai wannan
ne yayi min tsanani sosai, amman tunda akayi min allurai da drip na warke, kaga ai
ba sai munje Asibtin Malam din ba ko?". Wani kallon Baki da lissafi yayi Mata, shi
Yana can ya kasa tsugun da ransa ita Kuma tana fada masa wani shirme.
"Zuwa can ba fashi, kuma da izininwa Kika taho gida jinya kin tambayeni Zaki zo
gida?" Narai narai tayi da Ido abinda ke tsuma shi kenan yaji Yana neman sakin
layi.
"Kai Yaya wallahi na fada maka Zanzo gurin Ammah Kuma ka amince kace nazo koka
manta Ranar da zaka tafi?" Ta fada a shagwabe tana zubawa Masa sexy eyes dinta da
suka Kara wani hasken wahala data Sha.
"Kawai dai kin min wayo tunda kin fini sanin takan duniya kin fini ilimin boko me
zurfi shine zakiyi min education, haka ake cewa ko?".
Shiru tayi Masa.
"Kiyi magana Mana nifa bana son Shiru sai Naga kamar jikin ne"
"Nifa na fada maka na warke sai wani jikon Kuma".
Zaro Ido yayi Yana Mata kallon mamaki.
"Sai wani jikon kamar Yaya? Kenan har kina tunanin Zaki qara fuskantar wani ciwon
bayan wannan?".
Kai ta gyada Masa alamar Eh.
"Pls talk ki bude Baki kiyi min bayani as how kike expecting Zaki Kara irin wannan
ciwon?".
Sai da ta kauda kanta ta daina kallonsa sannan tace Masa.
"Nifa each and every month sai nayi wannan ciwon".
Ta fada tana Kara juyar da kai.
Cikin damuwa yace. "Pls juyo muyi magana Ina son sanin yanda ciwon yake ne Zan
fadawa wani doctor Kinga ai saina San komai kafin na fada Masa yanayin ciwon"
Cikin Jin kunya da nauyinsa tace. "Nifa idan zanyi period ne nake yin ciwon cikin
Baya sauki sai anyi min doclofenic injection yake denawa".
"Ok, to idan period din yazo Kuma shike nan baya Kara ciwon?".
Kai ta gyada masa. "Ki cire hijabin Naga yanda Kika rame tunda Nima daba ciwon nayi
ba na rame lokaci daya dubi yanda nayi Rama? a lokaci aiki ma zanyi amma na kasa
tabuka komai".
Rufe bakinta tayi cikin mamaki tace.
"Dan Allah ka daina haka ka manta a dakin Ammah fa nake idan ta shigo fa ta ganni a
yanda nake me kake son na fada Mata?".
"To ya za'ayi Kenan Ranar data ganki da ciki Kuma a jikinki tunda kina kunyar taga
muna video call ba hijabi kamar Wanda ta aikata alfasha Allah idan na dawo dole
asan abinyi na Fara gajiya gaskiya sai ragaita nake kamar marayan da bashi da uwa,
alhalin Allah ya Gama min sutura, koba haka ba?".
Shiru tayi Kamar ruwa ya cinyeta idan ta biye masa kunya ze Bata tunda taga alama
Yana neman fitsare idanunsa.
Jin tayi Shiru yasa Shima ya bar zancen ya koma Kan batun tafiyar su Asibiti.
"Goben idan Allah ya kaimu magaji ya kaiki ki dauko wayarki tunda tana gida ki
dauko Yan abun bukata tunda sai kun Gama komai kafin ku dawo wata Kila zaku dauki
lokaci ba'a Gama gwaje-gwajen da zasuyi Miki ba, itama wannan Matar ta dauki abinda
ya Kanata nata saiki fada Mata".
Sun Dade suna wayar har Ammah ta wuce part din Abba Basu Gama ba, sai kusan Sha
daya ya hakura sukayi sallama.
Da safe tunda wuri Ammah ta saka magaji yakai Zilai gidan ta karkashe kayan
electronics, ta cire duk abinda ake ganin ze iya lalacewa ta Mika gidan maman
junior bisa Umarnin Ammah.
Karfe bakwai da rabi Mai kyau su zilan sun koma gidan Ammah da kayan Zahra a jaka
set biyar da sauran tarkace na bukatar yau da Kullum.
Sam Mama Bata da labarin kwanan zahrar a gidan Sai da zilai ta shigo da Kaya a
hannu magaji Kuma karamar luggage a hannunsa da sauri ta aje bowl din dake hannunta
ta nufo Zilai tana fadin "lafiya kuwa daga Ina haka zilai?"
Gaishe ta zilan tayi tana fadin "munje mun daukowa Zahra kayan sawarta tunda Bata
koma gidan ba Nan muka kwana daga asibitin gida mukayo". Ikon Allah wallahi ban
sani ba, Babu Wanda ya fada min tun daren, Bari na shiga Naga jikin nata".
Suka nufi part din Ammah.

✨✨✨

AUREN HUCE HAUSHI

✨✨✨

MAMAN FATEEMAH.

Page 37.

_______Cikin wani irin takun Jin Dadi da karsashi Mama ta shiga parlourn Ammah
tana fadin "Ina patient din take? Ashe nan Kuka kwana jikin ne yaqi Dadi bayan mun
taho? wlh ban sani ba sai yanzu da naga zilai ta shigo da kaya ta fada min". Ammah
ce ta fito faga kitchen din part din ta tana fafin "ko daya sangarta ce kawai Wai
kada ciwon ya tashi cikin dare, kamar an fada Mata a Nan din ciwon baze tashi ba".
Dan murmushi Mama tayi "ai kinsan yanda take da son gida ai inaga idan sun dawo ma
saita zauna a nan din tunda ba'a San ranar da mijin nata ze dawo ba gara tana kusa
tunda Naga alama ba wani iya riqeta zeyi ba da farawa da iyawa, Allah ma yasa Bata
da juna biyu ai da abun yayi yawa ga zawarci ga goyo".Dan Jim Ammah tayi Dan da
gaske maganar ta doketa wane irin mugun fata ne haka bako kawaici gurin fadin
maganar.
"Allah ya rufa asiri, duk abinda Allah ya tsarawa zahra Zan karba da hannu biyu ba
komai, idan Allah ya hukunta Mata rabuwa dashi bani da tsimi bani da dabara,kinsan
shi dare ga Mai rabo hantsi ne, fatan da muke dai Allah ya rabata da wannan ciwon
me bibiko".
Zahrar ce ta fito Shar da ita cikin doguwar Rigar material Baki da pink din flowers
manya ta saka gyale medium a kafadarta tana baza kanshi kamar anyi barin turare a
jikinta a hankali ta shigo cikin takunta na rausaya tana amsa wayar sajida wadda ta
kirata tana dubata da jiki.
"Ke kuma waya fada miki bani da lafiya?" Zahra ta fada tana Zama kusa Auta da yake
breakfast ze tafi school.
Tunda zahrar ta shigo idanun mama ke bin zahrar da kallo.
Wayar taci gaba da amsawa tana fadin "jikin fa da sauki kawai shine yake ta bankama
abun kema fa kinsan ciwon tun Mana kazaure shi ne fa yaketa faman tsallen tsinka
tsimma akansa".
Ta fada tana dariya kasa kasa.
"Amma Baki da kirki mijin naki ne me tsallen tsinka tsimman? Saura kadan nayi Miki
tawaye bestie irin wannan cin fuska haka?".
"Sai anjima Zan kira".
Ta fada a hankali duk da Daman idan ba Kuna kusa sisai ba bazakaji abinda take fada
ba.
Sai da ta kashe wayar sannan da dubi inda Mama take zaune ta Dan rankwafa kada daga
zaune tace
"Mama Ina kwana?"
Ba yabo ba fallasa ta amsa tana fadin "ya jikin duk da dai ba alamar ciwo a tare
dake, Banda son yawo Ni banga abin tafiya har Kano ba akan ciwon mara na Mata".
Badan Ammah ta jawa Zahra layi ba da Babu abinda ze Hana ta bawa Mama amsar
maganarta ba to ba Hali sai zilai ce ta magantu "To Mama tunda yace taje a duba
lafiyar ta ai dole taje tunda da gaske Yana cikin damuwa".
Dan tabe Baki tayi tana fadin. "Ai kam sai kuje nasan dai rabe-rabe zakuyi a gidan
uban gidan nasa".
Duk abinda ake Ammah najin su amma ko kallon su batayi ba, haka zilan ma Bata Kara
fadin komai ba ta fice daga parlourn.
Hamza ne ya leko parlourn ya gaishe da Ammah tunda sun gaisa da Mama, Zahra ta
gaishe shi Ya amsa yana fadin "ya jikin naki? Ku fito inji Abba zaku wuce kanon".
Ta amsa da "to Yaya, jikin da sauki nafa ware wlh, kawai dai".

"To Allah ya Kara lafiya".


Ya juya ya koma.
Zilai ce ta shigo da sauri tana "Ammah zamu tafi ayi Mana addu'a".
Dan murmushi tayi "Allah ya tsare ya bada lafiya".
"Allahumma Amin".
Gurin Ammah Zahra ta karaso a hankali ta rungumeta kamar zatayi kuka, zamu tafi
Ammah saina Kira idan munje kada ki Kira Aunty Hasana tunda Bata Dade da tafiya ba,
Allah yasa ma gobe zamu juyo gida wallahi bana son zuwa nifa".
Bayan ta Ammah ta Dan shafa tana fadin "kuje ba komai In Sha Allah za'a dace a gano
menene matsalar tunda suna da Qualified Gynecologist doctors, Allah ya tsare
hanya".
Kai ta gyadawa Ammar ta saketa ta koma ta dauki hand bag dinta sai lokacin tayiwa
Mama kallon Ido cikin Ido.
Zamu tafi Mama sai Allah ya dawo damu". Tayi gaba tana rike da hannun Musaddiq
sukayi waje, Bata bi takan abinda mamar ke fada ba, da sauri mamar ta rufa musu
baya ko sallama batayiwa Ammah ba, wani lokacin Ammah tana mamakin yanda Mama ke
nuna tsana da hassada akan Zahra idan abin ya taso Mata Bata iya hiding dinsa dole
saita nuna an gane.
"Allah ya raba na gari da mugu li'ilafi quash".
Ammar ta fada tana komawa kitchen inda take kokarin hadawa Abba break fast.
Zahra na rike da hannun Musaddiq suka fito compound din.
Mama na fitowa sukayi kicibus da sahura da sauri ta kyara Mata tabi Zahra a baya,
ta nufi part dinta ita Kuma sahurar tabi Zahra da sauri.

Ganin Abba a harabar gidan ya hana sahura garasowa gurin zahrar dole taci burki a
gefen second gate din. Zahra gurin Abban ta nufa Yana ganota ya Fara fadar "Masha
Allah! Uwata jikin yayi kyau, ya kika kwana?".
"Da sauki Abba, Ina kwana?"
Ta fada tana tsugunnawa kusa dashi.
"Lafiya kalau Aina leka dana dawo daga masallaci akace Baki tashi ba".
"Eh Ammah ta fada min, nifa Abba dama hakuri akayi da zuwan Nan nafa warke ba inda
yake min ciwo yanzu".
Sameer ne ya shigo da alama daga wurin Baba Malam yake Dan harda Habib suka shigo,
gurin Abba suka nufo Habib ya gaishe da Abban sannan Zahra ta gaishe su shida
Sameer din suka dubata, mikewa tayi suka nufi inda Malam Bala direba yake jiran
Auta su tafi makaranta, sai ya shiga ya zauna sannan Zahra ta bashi 1k, tace ga
kudin chocolate Nan idan ka dawo Ammah zata baka wasu na saka Aunty zulai ta debo
maka".
"Nagode Aunty Allah ya sauwaqe Miki Zan Miki addu'a idan nayi sallah, malam Bala ne
ya karaso suka gaisa da Zahra ya tada motar suka fice Musaddiq Yana daga Mata
hannu.

Ta juyo kenan ta hango zilai da sahura sun nufi gurin su Abba suna gaishe su sannan
Habib ya karbi key din motar suka zuba kayan dake hannun su.
Sallama su Sameer sukayiwa Abban suka nufi gurin motar, zahrar ce ta dawo gurin
Abban tana fadin "zamu tafi Abbana ayi Mana addu'a"
"Allah ya tsare hanya uwata ya Baki lafiya yasa daga wannan zuwa Asibitin a samu
warakar wannan ciwon".
"Amin Abba nagode mun tafi sai nu dawo" ta juya ta nufi motar.

Har gurin motar Abban ya karaso Yana musu Addu'a da fatan sauka lafiya.
A hankali Sameer yayi kwana ya nufi gate din fita Abban Yana daga musu hannu, haka
ma Ya Hamza shima Saida yaga ficewarsu sannan ya koma side dinsu, sunzo fita Sameer
ya dunkulo kudi yaba Mai gadi cikin murna ya Fara jero Masa Addu'oi da fatan
Alkhairi har yayi Dan nisa suna jiyo muryarsa.
A wurin gidan sarki Habib ya sauka, sukayi sallama da Sameer yayiwa zahra sallama
da fatan samun lafiya Mai dorewa, yayi gaba zuwa ina zaya.
Sun mika a tafiyar sosai Sameer ya Dan juyo kadan Yana fadin.
"Madam tun jiya nake Kiran wayar ki ba'a dauka".
Dan kwantar da Kai tayi jikin seat din tana fadin. "Wallahi rabona da wayar tun
jiya da safe a gida na barta lokacin Ina Zan iya tunawa da wata waya Ina tunanin ko
ranar karshen ce tazo, sai dazu da Aunty zilai ta dauko min nabi wasu missed calls
din kafin na Kira taka number din ya Hamza ya shigo yace kazo mu fito, na gode
kwarai da kulawar ka Allah ya Raya Mana babyn mu". Ta fada tana Dan murmushi.
Shima murmushin yayi tana fadar "wato baby kadai Zaki tambaya Banda mamansa wato
saboda sunan mijinki ne son Kai ko?.
Hannunta ta saka ta rufe fuskarta.
Dariya zilai tayi tana fadin tuba muke Yallabai ai baza'a Fara haka ba, gani tayi
baby shine bako".
"Kin Kare ta dai kawai Aunty".
Tafiyar awa biyu da minti Arba'in da biyar suka shigo Kano.
Suna area mariri Sameer ya lalubo Rukayya.
"Da fatan komai yayi yanda akeso ya zama ready ko?"
Sauraren amsar da take fada Masa yake, kafin yace "ok mun shigo ki Kira mommy tasa
salmanu ya kawo iya Rahane yanzu".
Bai jira abinda zata fada ba ya kashe Kiran.
Wani Kiran ne ya shigo masa, shima dai yana da alaqa da zuwan nasu duk dai zahrar
naji tayi mamakin Yanda Sameer yake magana cikin ladabi irin haka to shida waye
yake wayar Wanda ya jibinci lamarinta haka? Wata qila inda sukeyiwa aiki ne suka
dauki nauyin zawa Asibitin nata, haka ta ringa sakawa da kwancewa, shi Kuma Sameer
shiga can kurda can har suka shigo Nasarawa G.R.A sultan road.
Tunda suka shigo Kano zilai ke baza idanu, Tana bawa idonta abinci, ita fa zilai
duka zuwanta Kano baifi sau uku ba,
Shima Ammah take yiwa rakiya idan wani uzurin ze kawota.
Gidaje ne na garari take gani da ban mamaki yinsu ake kamar baza'a mutu a barsu ba,
tana ganin gidajen da take mu'amala dasu sun Kai sun kawo Amma yanzu sai take ganin
tamkar akurki ne kan wadan da take gani Bata gara sarewa ba Saida taga gidan da
Sameer ya dosa, take hantar cikinta ta kada, innalilllahi takeyi a zuciyar ta, Nan
da nan jibi ya Fara karyo Mata Daman tana mamakin gidan da zahrar ke ciki na can
Azaren to kuma saiga wani, duk da Bata San mamallakinsa ba, wata Kila karar kwanace
tasa ta biyo zahrar irin wannan gidan da sai ayi dambun Naman ka na waje baiji ba.
Kofar wani mahaukacin gate ya tsaya yayi horn sau biyu aka bude suka shige.
Ba zilan ba ita kanta Zahra ta sare da lamarin gidan Dan tasan yes Sameer masu kudi
ne ko kungiyoyin su suna sakin kudaden aiki kamar ba gobe amma Bata taba tunanin ya
mallaki irin wannan mahaukacin gidan ba. Dan da gani ba tambaya mamallakinsa yaci
ya tada Kai. A kofar parlourn ginin da yafi ko wane tsaruwa da kyawun gani ya tsaya
yana hamdala ga Allah s.w.a.
Wata matashiyar buduruwa ce ta fito daga parlourn cikin rigar atamfa fitted tana
takun yanga da gayu ta nufo motar tana fadin "sannunku da zuwa, Amma wallahi I am
very surprised Dana ganka yanzu".
"Rukayya Kenan kin dauka Ina Miki Wasa ne idan Kinga banyi driving ba nine bansa
kaina ba".
Dariya tayi "ai na yarda Kuma nasan wannan assignment ne me mahimmanci a gurinka".
Fitowa yayi Yana fadin "yauwa sannunki da kokari, kuma haka ake tarar Baki a garin
ku? kinzo kinata surutu kin tare Mata kofar fita".
"Oh! Sorry" ta fada tana budewa Zahra kofa duk da Bata ganinta sosai saboda tintac
glass ne a motar.
Dan matsawa tayi ta bude Mata kofar, kanshin da yayi Mata sallama ne yaja hankalin
Rukayya ta kalli kofar lokacin Zahra ta sako kafarta daya Kan fuskar zahrar idanun
Rukayya suka sauka.
"Kam bala'i"
Rukayyar ta fada a zuciyar ta "wacece wannan din Kuma? Tun jiya lokacin da ya
Sameer ya aiketa shopping na abubuwan amfanin gida da kayan Mata ready made take
Masa kwawar ya fada Mata na waye? sai dai yace Mata wata ce Zaki ganta yarinya ce
ko sa'ar ki Bata kai ba yayanta ne ya hada su ya kawota Asibiti, sai oga yace a
sauketa a gidansa har su gama da asibitin.
Rasa wane yare Rukayya zatayi Mata tayi saboda tasan wannan ko zo da hausa Bata
sani ba duk da shigarta ta hausawa ce. Aunty zulai ce tayi magana lokacin data fito
"haba yallabai Ina laifinta gashi ta fito ta tarbe mu".
Dan murmushi zahra tayi lokacin data fito daga motar gaba daya ta kalli Rukayyar
tana wani smile Mai daukar hankali tana fadin "sannu Aunty mun gode" ta fada tana
mika Mata hannu, ba Karamin mamaki Rukayya tayi ba Jin zahrar na zazzaga tsantsar
hausa bako gargada. Bangaren Sameer zahrar ta kalla tana fadin "Haba oga Ina laifin
Aunty na ko wannan fitowar da tayi ai shima Yana cikin entertaining ne mun gode".
Ta fada lokacin data rike hannun Rukayyar.
Sai lokacin zilai ta Dan samu Peace of mind ganin Rukayya tasan dai da alama gidan
bana macuta bane duk da ba tana zargin Sameer bane,yau din ce wata iri baka saurin
amincewa da mutane.
"Sannunku da hanya".
Rukayyar ta fada tana kallon Zahra, yayin da Sameer ya shiga motar ya nufi parking
lot ya ajeta.
"Yau Aunty mun gode"
Zulai kuwa sai kalle kalle take tana jinjina girman gidan Dan wasu gine - gine take
hangowa na Alfarma ga shuke-shuke Nan sai wani sanyin kamshi ke tashi a gidan ko
Ina Kuma tas ba alamar datti a cikin, dukiya dai Mai sunan dukiya an kasheta a
gidan Nan.
Ita tunda uwarta ta kawo ta duniya Bata taba shiga irinsa ba, sai yau da dalilin
uwar dakinta Zahra ya kawo ta.
Maganar Rukayya ce ta dawo da ita cikin hankalin ta.
"Bismillah mu shiga daga ciki".
Rukayyar ta fada tana nufar kofar parlourn numbers ta daddanna ta bude musu kofa
ita dai zilai yau jinta take kamar ba cikin kasar take ba.
Lokacin da suka shiga parlourn ba zilai ba kifin rijiya ita kanta zahrar sai da
wani shock ya shigeta na wucin gadi, badan Zahra tana fita waje ba Kuma kakanninta
masu dashi ne kuma tayi zaman syprus taga guraren hutawa da yawa da gidajen Alfarma
da Babu abinda ze Hana ta zabga kauyanci, dan Babu karya naira tayi kuka a cikin
parlourn Nan tamkar fadar sarauniyar ingila komai na ciki off-white ne da sirkin
ash colour ba tarkace da yawa sai dai an kawata shi da wasu irin cutains masu
azabar kyau dan shi kadai abin kallo ne, sai fremes masu kyau da tsari da wasu irin
flowers, sai wani special kamshi daya hadu da sanyin A/C ya bada yanayi Mai dadi,
sai plasma kusan bango guda.
Zilai dai 'yar kauye sak ta koma ko Zama kasayi tayi sai da Rukayya ta juyo tace
Mata Bismillah ki zauna Mana ku Sha ruwa".
Ta fada tana yin gaba ta nufi wani steps gurin dining table ta shige wata kwana.
Zahra zilai ta kalla "Wai Ina ne Nan din Kuma gidan na wanene nifa duk a rude nake
na kasa samun nutsuwa ko kadan, irin wannan gidan ai sai sarki ko wani gagarimin
Mai kudi".
Da watsa hannu Zahra tayi.
"Toni Ina nasan amsar tambayar taki, Nima duk daya muke dake bansan komai ba, nasan
dai yace zamu zauna a Nasarawa GRA kawai ba wani Karin bayani da yayi min".
Rukayyar ce ta shigo dauke da babban tray da robobin farmfresh dasu ruwa da Shani
na gwangwani, sai fruit fresh ones.
"Bismillah kusha ruwan sai muje ku huta sai kuci abinci".
Sannu Zahra tayi Mata, itama zilan tayi mata, Sameer ne ya shigo da wani matashin
saurayi da luggage din Zahra da 'yar madaidaiciyar jakar zilai a hannunsa ya gaishe
su ya aje ya koma.

Rukayya ce nufo inda Sameer din yake tana fadin "Ya Sameer Dan Allah ka jirani Zan
bada sako gurin mommy ka taho min dashi"
"Kefa Ruky kina da damuwa kiyi Abu Mai mahimmanci sai ki tsaya kina Wasa".

"Allah Yaya da gaske nakeyi ka taimaka min".


"Ok"
Gurin su Zahra ya duba Yana fadin "sannunku madam kun sha hanya ki huta zuwa dare
zamu fita Asibitin doctor tace mu hadu da ita a Nan Asibitin Nasarawa zataga
patient yau a can da dare saita dubaki idan yaso sai mu hadu da safe a malam din".
"To ba damuwa in Sha Allah Zan shirya da wuri nagode".
Ya juya ya fice daga parlourn.
Zahra tayi mamakin ganin favourite drinks dinta da aka kawo, more especially farm
fresh Amma Bata kawo komai ba ta dauki abin arashi ne kawai.
Bayan Sameer Rukayyar tabi suka fice daga parlourn.
Saida suka sauka daga steps din gurin sannan Rukayyar ta dubi Sameer tana fadin
"big bro Dan Allah wacece wannan din? Meye matsayinta a gurin Ya Mahmud nasan wlh
ba banza ba yace a bude Mata wannan apartment din nasa".
Tsaki Sameer yayi "na dauka want important Abu Zaki fada min Ashe tsabar gulma ce a
cikinki, ba abinda yayi Miki zafi a lamarin yarinyar Nan yanda Kika ganta haka Nima
na ganta bansan ko wacece dinsa ba tunda baiso in sani ba, Dan haka kada rawar
kanki tasa ki fadawa Dr Haseena wani Abu Koda zata tambayeki kice Baki San komai
ba".
Tunda ya Fara magana Rukayya tayi zuru tana kallonsa yanda ya kiciccife yasa tayi
masa alamar (?) Tasan there's something behind.
Amma fadan dayafi karfinka sai ka mayar dashi Wasa.
Dan jinjina Kai tayi tana fadin shake Nan Bari na koma kada suga an barsu su
kadai".
Ta juya ta koma Zuciyar ta fall da tambayoyin da Babu Mai Bata amsarsu.

Lokacin da ta shigo sun gama suna Dan hira.


Cikin bada uzuri Rukayyar tace "kuyi hakuri na barku ku kadai Bari na Fara rakaki
naki masaukin kafin na dawo na rakaki Aunty ta fada tana kallon zulai".
"Babu komai muje na shigar Mata da jakar kayanta.
Rukayyar ce a gaba su Zahra suna bayanta, saida suka wuce parlour uku kowanne Yana
wane na Bata zulai da abin harya daina Bata tsoro tunda taga abin bana karewa bane,
wani corridor ta nufa suna biye da ita wasu steps suka gangara suka shiga, wani
parlourn suka shiga Mai azabar kyau fiye Dana baya, kofofi biyu ne a cikin wani arc
suna kallo juna, kofar hannun dama Rukayyar ta nufa saka Kati ta bude kofar tana
tana fadin Bismillah". Tana murmushi.
"Mu shiga Mana". Zahra ta fada.
"A'a iyakata Nan, dakin na manya ne bani fa hurumin shiga ciki".
Jin haka yasa zilai Jan burki, itama jagabar da tasan ciki da Bai na gidan tana
fadin haka inaga ita 'yar karere.
Aje luggage din tayi tana fadin. "A fito lafiya uwar dakina".
Suka juya Rukayyar na fadin Bari muje sai kin fito.
"Ok, nagode.
Zahrar ta fada tana janye da luggage din ta murda handle din da siririyar sallama a
bakinta. Bata iya karawa ba taja ta tsaya tana waro idanu waje na mamakin abinda
idonta yayi arba dashi...
AUREN HUCE HAUSHi.

MAMAN FATEEMAH.

Page 38.

A hankali ta ringa tafiya kamar wadda ke tsoron kada a kamata, abinda ta gani ne
ya Bata matukar mamaki wannan bed room din tamkar an dauko na can Azare na Mahmud
an aje a Nan, hatta da curtains din windows din iri daya ne ba banbanci, Abu daya
wannan yafi wancen shine girma wannan yafi balance akan wancan, Amma tamkar an
dauko shi an aje, ita abin da farko tsoro ya bata hatta kamshin turarensa taji a
dakin jiki ba kwari ta dosana ta zauna a gefen bed din tana Kara karewa dakin kallo
tabbas a gizo idanunta ke Mata ba abinda ta gani haka yake, bata Kara tabbar da
kamshin Mahmud takeji ba Saida ta zauna kamar lokacin ya saka ya fita daga dakin.
Dan dam tayi Jin ta Fadi sunan Mahmud fatsal sai taji wani bambarakwai a bakinta
duk sai wani irin Abu ya darsu a zuciyar ta.
A shagwabe kamar tana magana da wani ta Fara fadin "to me ma zance masa ne? Kuma
Wai Nan din dakin waye da suke kamanceceniya da nasa har kanshin ba banbanci?.
Ba Mai Bata amsar tambayar Dan haka ta Dan zamo kadan tana janyo luggage dinta tana
fito da abinda ke ciki,wanka take sonyi duk jinta take a takure indai tana period
sai a hankali sam Bata da sakewa ko misqalazarratin, Banda dole Babu abinda ze
sakata barin gida a irin wannan condition din.
Luggage dinta ta janyo a hankali ta Fara fito da abinda ke ciki, na Kan mirror ta
Fara diba ta nufi inda yake lokacin data karasa ba karamin mamaki tayi ba ganin
irin kayan shafar da take amfani dasu har da wasu daga cikin irin turarukanta ta
gani Banda su freshner na fesawa.
Bata fasa aje na hannunta ba, gurin kayan ta dawo ta bude cloth set din data gani
tana budewa tayi arba da kayan Mata Babu abinda Babu, harsu shoes da bags, dasu
inner wears.
Mayarwa tayi ta rufe ta dawo da kayan a hannu ta mayar inda ta dauko su.
Wanka ta shiga Nan ma wata duniya ce aka hada, ta jima tana gasa jikinta Dan idan
Tana irin wannan condition din Bata kaunar abinda ze hadata da ruwan sanyi ko
kadan.
Bata wani Bata lokaci ba gurin shiryawar ta saka doguwar Rigar atamfa glitter
purple, Rigar tayi Mata das a jiki mayafi light brown ta saka touching din jikin
atamfar sai takalma suma light brown din plat, haka nan taji tana son saka
turarensa Mai sanyin kamshin Nan dauka tayi ta fesa ta nufi hanyar ficewa daga
dakin.
Saida ta fito yanzu ta karewa wannan parlourn kallo yafi duk Wanda ta gani a baya
tsaruwa kunjerun dake ciki ko rantsuwa tayi bazatayi kaffara ba Bata taba ganin
irinsu ba duk kuwa da gidajen Alfarma data shiga ta bangaren Ummee.

A hankali ta ratsa ta wuce tabi hanyar da suka biyo suka shigo.


Ba kowa a parlourn lokacin data shiga sai dai tana jiyo Dan Karan plates haka kamar
ana wanke-wanke.
Zama tayi taga ta inda wani ze gitta tunda ita dai ba sanin Kan gidan tayi ba. Wata
Mata taga ta fito daga wajen dining ta wata kofa da manya food warmers a
hannunta,ta aje a kan table din har zata juya ko jijinta ne ya Bata da mutum a
gurin yasa ta juyo tana duban cikin parlourn, Ido suka hada da Zahra da sauri matar
da gangaro daga steps din dining din tana fadin "Masha Allah, ko surukar tamu ce ta
fito?".
Ta fada tana nufo Zahra dake zauna tana murmushi, itama iya Rahanen murmushi take
har ta karaso gurin zahrar.
"Sannu Mama Ina yini"
Zahrar ta fada.
"Yauwa sannu yarinya ya kukazo?"
"Lafiya kalau Alhamdulillahi".
"To Masha Allah, sunana iya Rahane nice mommy ta turo na zauna dake kafin ki gama
abinda ya kawoki".
Ta fada tana Dan tsugunnawa a gefen zahrar.
"To Mama na gode, Amma Dan Allah ki daina tsuguna mini kinyi jika Dani idan Ni ban
Baki irin wannan girman ba to kema bai kamata ki bani ba, Dan Allah ki tashi"..
"A'a 'yata Allah ne ya Baki Dan na tsuguna Miki Babu laifi".
Kafin zahrar ta samu zarafin Mai da Mata amsa Rukayya ta fito daga inda iya Rahane
ta fito ganinta da Zahra yasa Rukayyar ta karaso gurin su tana fadin "har kinyi
me?"
"Harna fito Ina Zan iya Zama a wancan lungun Ni kadai kamar mayya ai Naga kokarin
matar gidan nan data iya zama a cikinsa, Daman jiranki nake dakin da Kika rakani na
matar gidan ne gara ki hadani da zilai mu zauna tunda duka kwana nawa zamuyi mu
tafi kada a samu matsala kinsan halinmu Mata da zargi naje na manta wani Abu daya
danganci namu na Mata a samu rashin yarda a tsakanin masu gidan Dan na bude cloth
set Zan zaka kayana saina tarar da kayanta a ciki Kinga ai Bai kamata na shigar
Mata dakin ba ya Zama Bata da sirri kenan".
"Wannan gaskiya ne ranki shi Dade kinyi tunani me kyau a kam".
Iya Rahane ta fada.
Zama Rukayyar tayi gefen zahrar tana fadin ai gidan Mai shi ko auren fari baiyi ba,
kayan da kika gani duk nakine bana kowa bane Dan ya Sameer ya bani kudi nayo
siyayyar jiya Dan a Nan na yini nida su suhaila Dan furnitures din dakin ma jiya
aka sakasu Ina ga ba wata macen data taba zama a cikinsa Banda Mai gidan to kece
ta biyu da Kika zauna, bama a dakin yace a sauke kiba dayan yace sai Yaya Sameer
yace na Baki wannan ya wadatar kawai.

"Iya aje a fito da sauran abincin sai muje kiyi lunch din tun, shigarki ciki ya
Sameer ke kirana Wai kinci abincin Baki da lafiya na tabbar kin Sha magani ni har
mamakinsa nakeyi Bai dauki lamarinki da Wasa ba gaskiya".
Iya Rahane ce tace "Haba Rukayya yaushe Alhaji karami Zeyi wasa da lamarin iyalin
Mahmud, Nima da Mommy ta kirani Saida ta Kira shi ta fada Masa nice zanzo ya amince
kafin Nazo, ya jaddad min na kular Masa da ita yanda ya kamata, Kinga kuwa ai baiyi
laifi ba ko?".
Kai kawai Rukayyar ta iya gyadawa mamakin duniyar Nan ya gama kasheta a zaune
"matar Mahmud? Haba biri yayi Kama da mutum, tasan ba banza ba ya Sameer keta rawar
kafa ya kasa tsaye ya kasa zaune akan lamarin, Kuma da alama itama yarinyar ninketa
sukayi ta bai-bai Dan da alama batasan waye hakikanin mijin nata ba, gaskiya ta
tayata murna dan ta zama Mai sa'a duk da shima Saida ya dauko diamond a cikin
zinarai, Dan Daman wannan irin matansu ne.
Gurin dining din Rukayya tayi Mata jagora suka nufa tana fadin "kice min matar big
bro ce Amma nayi mamaki gaskiya sun lullubeni Amma ki Bari kawai bazance naji ba
Naga iya gudun ruwan ya Sameer sai wani cewa yake kanwar abokinsa ce".
Ita da zahra Dan murmushi take tunda ba gane Kan zancen tayi ba.
Abinci ne yakai kala biyar Rukayya ce ta bubbude wa zahra tana fadin "Auntyn mu ki
zabi Wanda kike so a zuba miki".
"Kaji Aunty ni basai kin zuba min ba haba dadin sai yayi min yawa hakan ma na gode,
ina Aunty zilai tazo muyi lunch din".
"A'a nan naki ne ke kadai na Kai Mata nata dakin ta tun dazu".

********

Knocking din kofar akeyi a tana zaune ta Sha uban gayu kamar wadda zata wuri dinner
ta biki sai kanshi ke fita a jikinta Mai Dadi tana rike da wayar ta tana addu'oin
yaumiyya na cikin du'aul mustajaba.
Umarnin shigowa ta bayar tana kallon kofar, Basira ce yarinyar dake aikin shara da
goge-goge a bangaren ta, tsugunnawa tayi tana fadin "barka da Asuba Ammi".
"Barka kadai Basira har kin fito da wuri haka, lafiya dai ko?"
"Lafiya kalau Ammi Daman Hajiya Inna ce tazo ita da Abie".
Littafin ta aje akan bed side tana fadin "Hajiya Inna kuma"?"
Kai Basira ta gyada alamar eh.
"Kije gani Nan fitowa in Sha Allah".
Ta nufi clothset dinta ta dauko gyale mahadin shaddar ta fito daga bedroom din.

A hankali take saukowa daga stairs din shar da ita tun kafin ta karasa saukowa
kamshinta yayi musu sallama, cikin takunta na nutsatstsiyar mace Mai aji da yarda
da kanta ta da tarin ilimi Hadi da wayewa, sallama tayi musu tana nufar gurin
Hajiya Inna ko inda general yake Bata kalla ba.
Kusa da Hajiyar ta zauna lokacin da take amsa sallamar tata.

"Ina kwana Hajiya".


Cikin nuna kauna da kulawa Hajiyar ta amsa tana tambayar ta Ina su uratu Ammin tace
Basu tashi ba tunda yau ba zuwa school.
Ammin ta Dan juya bata yarda sun hada Ido dashi ba tace Masa. "Barka da Asuba".
Shiru yayi Mata kamar beji abinda ta fada ba, itama Bata kara bi takansa ba,
Hajiyar na ankare dasu.
Ammin ce tace "Hajiya me yasa Kika fito yanzu da sassafe idan kina son ganina basai
ki turo nazo ba basai kin taso da kanki ba Dan Allah kiyi min wannan alfarmar kada
wani Abu ya taso nason ganina ki taso ki taho saboda ni".
"To in Sha Allah hakan baze Kara fatuwa ba nima ba zuwan kaina bane jiya Muhammadu
ya sameni da dare yake fada min wata maganar da banji dadin ta ba, shin da gaske ne
bakije inda yake ba tunda Kika dawo? Idan ya Kira wayarki bakya dauka, yazo da
kansa yafi sau biyar kin rufe kofa?".
Shiru Ammi tayi shi Kuma general kamar ya rungumeta a gaban Hajiyar haka yakeji Dan
gani yayi ta wani Kara yin fresh da ita bazaka taba cewa ita ta haifi wadannan
yaran ba, ta koma masa danya sharab da ita ga uwa uba ko runhu ka rike Kan sakko
bazaka taba ganinta a hargitse ba ta San kanta sosai yanda ya kamata, da kyar ya
iya saita kansa a gaban Hajiyar.
"Kinyi Shiru zainab kenan abinda ya fada gaskiya ne?"
Sadda Kai ta Karayi kasa sai Jin shashshekar ta sukayi.
"Subahaballahi haba zainab ko lokacin da lamuran suka jagule Baki zubar da hawaye
ba sai yanzu, kiyi hakuri na fada Miki duk Wanda za'ace yayi hakuri to an zalunce
shi ki yafewa mijinki wallahi rashin samun kulawar ki tasa ya runtse ido ya iya
fada min abinda Bai kamata na sani ba, na roqi arziki ki dubi girman Allah da
manzonsa ki rungumi mijinki da 'ya'yan ki kiyi boyayyiyar aure yanda Kika saba".
Sai da tayi kukanta Mai isarta sannan ta share hawayen ta sai lokacin taji wani
gululo ya fice daga kirjinta.
"In Sha Allah ya wuce Hajiya har abada ki tayani bashi hakuri hakan baze qara
faruwa ba".
Dan karamin tsaki Hajiyar tayi "Babu hakurin da za'a bashi, shida ya shuka rashin
kirki, kece dai da hakurin ai cewa nayi bana zuwa shi daya Bata yaje ya gyara
kayansa tunda Allah yasa kikazo gidan Nan Baki taba kawo min qararsa ba sai shine
gemai gemai dashi ze dauko jiki ya kawo korafi ashe Babu dadi king...
Dan gyaran murya yayi "Hajiya kiyi Shiru komai ai ya wuce basai kince komai ba,
tunda dai nayi abinda takeso ai shike Nan kowa ya ganni a Nan da ranar Allah na
taso tsohuwa ta gaba ta min biko".
Ammi dai Shiru tayi Bata tanka ba sai Hajiya Inna ce tayi dan murmushin su na manya
Wanda suka San jiya suke ganin yau. Ammi duk sai taji wata kunya ta lullubeta, wani
lokacin maza kunyarsu kadan ce wallahi duk girmansu idan sukayi wani abun sai kaji
kamar kananun yara, kome ya fadawa Hajiya ya taso ta da wannan safiyar?.
"To shike nan sai ka bamu guri ko tunda Allah yasa taga girmana ta yafe".
"To shike nan yaushe Zaki koma gida?".
Kafin Hajiyar tayi magana Ammi ta rigata.
"A Nan zata wuni da magari ba za'a maidata gida".
",To kaji sai ka tafi naka uzurin tunda 'yata ta yanke hukunci".
Baice komai ba ya nufi part dinsa da yake bangaren ta, harya danyi nisa ya juyo
Yana kallonta ido cikin Ido da wani yanayi a tattare dashi.
"Kuyi breakfast Dani a kawo min ciki".
Kai ta gyada masa ya wuce ciki.

Yi Hajiya Ina tayi kamar bataji me yake fada ba ta cewa Ammi.


"Muje ki bude min dakin ko lazimi ban Gama ba yaje ya daukoni Dana ce yaje za'a
kawoni ma cewa yayi A'a".
Ita dai Ammi ba baka sai kunne tare suka shiga dakin da Hajiyar.

*******

A qalla sun dauki minti kusan Sha biyar kafin Zahra ta Gama. Parlour na biyu
Rukayyar taja Zahra suka shiga Bai Kai na farkon girma ba Amma ba karya Shima ya
hadu kamar jira ake su zauna wayar zahrar ta dauki sansanyan kidan ringtone din ta.
"Amma"
Ta fada tana picking din Kiran sallamar Ammar ta amsa tana fadin "kiyi hakuri Ammah
wallahi yanzu na fito daga wanka naci abinci, yanzu nake son kiranki na fada Miki
mun sauka lafiya".
Daga can Ammar ta amsa Mata da "babu komai da fatan dai komai lafiya ba wata
damuwa? zilai ce taso daga min hankali Wai wani gida aka kawo ku gari guda bata
taba shiga ko kwatankwacin irinsa ba kamar Kuna wata kasar ita tsoro takeji".
Dariya sosai zahra tayi Jin yanda zilai ta nadi zance ta fesawa Ammah.
"Kai haba Ammah kyale Aunty zilai rudunta ne kawai, gidan Dan babba Kam babba ne
Amma komai normal Ina Jin gidan wani friend din oga Sameer ne aka kawo mu, Kuma
momin su oga Sameer ma Saida ta turo Mai aikinta daya da kanwarsa daya Aunty
Rukayya gata ma nuna tare ku gaisa".
Wayar zahrar ta mikawa Rukayya suka gaisa da Amma, godiya Ammar ta dinga yiwa
Rukayyar har kunya ta kamata tace Kuma ta bawa Zahra number din mommy ta kirata
tayi Mata godiya.
Sallama sukayi da Ammar suna kashewa Kiran ya shigo international tana gani tasan
shine.
Dagawa tayi tana masa sallama Jin muryarta ba kamar jiya ba ya sauke ajiyar zuciya
a hankali da Bai yarda ba da Sameer ya fada masa kamar batayi ciwo ba sai yanzu da
yaji muryarta tana fita ba kamar jiya ba.
Sallamar ya amsa Yana fadin "my previous...".
Wani deeply saida tsikar jikinta ta bada wani yarrr. "Wash" ta fada.
Kara Kiran sunan yayi a hankali ciki wata murya Mai tada zaune tsaye "me ya faru ne
to jikin ne"?".
"A'a ba komai" ta fada a shagwabe.
Rukayya na ganin haka ta Miki tana nuna Mata tana zuwa Dan ta barta ta sake yanda
ya kamata.
"Alhamdulillahi haka nake son ji, ya ciwon ya daina ko yanayi kadan kadan".
"Ya M na warke yanzu ba wani Abu da yake damuna dama mu koma gida kawai tunda ya
wuce, kawai naje Naga baby muje mu gaishe da mommy da Umman sajida zuwa jibi mu
koma, Dan Allah kace to kaji Kuma fa kaga gidan da oga Sameer ya kawo mu gaskiya ka
fada Masa ya mayar damu gidansa ko gidan mommy wallahi yayi girma Ni tsoron inda
aka kaini nakeyi gurin yayi nisa da main parlour Kuma wani abin mamaki kasan
funitures din dake dakin irin na dakinka ne na Azare komai da komai".
Dan Jim yayi kafin yace irin nawa Kuma wace unguwa ya kaiku?".
Dan Jim itama tayi. "Ina ga ko Dawako Road Nasarawa G.R.A.

"Ok nasan gidan na wani friend dinsa ne, wane bedroom din aka Baki?".
" Bangaren dama daga can ciki sosai".
Shiru yayi wato Sameer be bude Mata master bedroom din ba kenan.

"Precious ki hakura a duba min ke kinsan kuwa tension din dana shiga akan ciwon nan
naki? kiyi hakuri ayi bincike akai kawai sai nafi samun kwanciyar hankali, gida
Kuma nasan shi Baki da matsala dashi Dan cike yake da tsaro ba wata kafa da za'a
shigo cikinsa".
"Baka Gane ba nifa ni kadai ce bazan iya kwana a gurin ba sai dai Aunty Rukayya
tazo mu kwana".
Ta fada kamar zatayi masa kukan shagwaba.
"A'a ban Amince ki kwana da kowa ba, ba abinda ze kamaki matsoraciya kawai kice na
shirya nida nake fatan Allah ya hore min nayi Miki Wanda yafi wannan girma yanda
Zaki sake ki walwala keda yaran mu, to kina tsoron wannan ma inaga Wanda nake fatan
ajiye sarauniyar Mata a ciki Zahra fa kike ko cikin taurari keta dabance, haka
kawai ki janyo min wata ta hanani rawar gaban hantsi da dare so nake ki ragemin
zafi idan da wata a dakin ai kin sabautani ko baza'a taimawa dan malam ba?".
Ya fada cikin wata irin kasala wadda ta saka Zahra Jin wani irin Abu a jikinta. "Ya
Ilahiy Ajib"
Ta fada cikin kasakalliyar murya.
"Yan Mata yaya dai Kona gudo ne kina bukatata a kusa"
Ya fada Yana huro Mata iskar Bakinsa ta cikin phone din, da sauri ta cire wayar
daga kunnanta, Dan da gaske sakon yaje inda aka aike shi kashe Kiran tayi bako
sallama.

AUREN HUCE HAUSHI.

MAMAN FATEEMAH.

Page 39.

________Wurin karfe takwas Sameer ya shigo gidan, wayar Rukayya ya Kira yace su
fito doctor tana jiransu, lokacin suna bedroom din da zahrar take suna cakusawa da
Zahra akan wata Rigar shadda 'yar Mali da Rukayyar ta daukowa Zahra cikin kayan da
Sameer ya bada ta sawo haka Nan Rukayyar taga zata Dace da zahrar shi yasa ta nace
akan ta sakata ita kuma tana ganin tayi Mata girma da yawa, Jin Kiran Sameer yasa
ta hakura ta saka sai gashi tayi Mata das kamar an gwadata aka Dinka.
Shar ta fito kamar ka dauke ka buye saboda kyau sai yarintarta ta Kara fitowa,
dauri mai kyau Rukayya tayi Mata tunda ta kware har makeup din amare takeyi, light
makeup tayi a fuskar ta sai ta fito kamar amarya ranar a yini.
"Masha Allah" kadai Rukayya ke fada ba karya kyau daban yake ko ita mace zahra ta
tafi da imaninta to yayi namiji Kuma? Bata yarda da kyau idan yayi yawa hadari bane
sai yanzu da Zahra ke gaban ta Dan babu namiji da ze ganta Bai Kara kallonta ba.
Kasa hakuri Rukayyar tayi Saida ta magantu.
"Allah yasa kiyi ta haifowa big bro Yara masu Kama dake gaskiya Ya Mahmud ya Dace
ai shi wallahi gaba ta kaishi gara da aka samu wannan incidence din da Bai faru ba
yaushe ze gano Mana ke".
Ita dai zahra murmushi kawai takeyi, amma Kasan zuciyar ta tambayoyi ne fal, Ta Ina
Mahmud ya zama big bro din Rukayya da alama akwai wata dangantaka Mai karfi a
tsakanin Sameer dashi bawai aikin NGOs din Nan bane gaskiya.
A haka suka fito main parlour suka tarar da Iya Rahane da zilai suna kallon Arewa
24 suna program din mata a yau.
"Masha Allah, Allah ya kade mugunji da mugun gani".
Iya Rahane ta fada tana kallon Zahra.
"Allahumma Amin. Allah ya tsare uwar dakina ya Baki lafiya yasa a dace".
Zalai ma ta fada, Rukayya tace "Allahumma Amin, sai mun dawo".
Suka nufi hanyar fita, a cikin mota suka iske Sameer, gaba Rukayyar ta shiga ita
kuma zahra ta shiga back seat.
Basuyi wata tafiya Mai nisa ba suka shiga cikin Asibitin, bayan sun fito daga
motar number Dr. Haseenar Sameer ya Kira, saiga wata sub-staff da wayar a hannunta
tana fadin "sunnunku da zuwa doctor tace na tafi daku office dinta tana zuwa suna
wani aiki ne"
"Ok mun gode".
Rukayya ta fada.
Har cikin office din ta kaisu ta fita Nan Sameer yabar su yace zeje yaga wani
friend dinsa Dr. Sulaiman.
Bai jima da fita ba aka turo kofar su duka suka juya suna kallon Mai shigowa macece
wankan tarwada Mai matsakaicin tsawo fuskarta doguwa ce da maidadaicin idanu da
hanci tana sanye da doguwar Rigar material coffee Mai haske tayi rolling da milk
din veil fuskarta fal fara'a ta shigo tana fadin " wa nake gani kamar Rukayya a
office dina rabon daki tako Nan harna manta Sai dai a waya".
Dariya Rukayyar tayi tana fadin "Ina laifin Kiran wayar ma Shima zumunci ne yafi
ace ba'ayin ko daya".
Direct gurin da suke zaune ta nufa " Kinga kin dauke min hankali Ina ta zuba ban
yiwa bakuwa ta sannu da zuwa ba, sorry na barku a zaune ta fada tana kallon zahra"
"Lah haba doctor ba komai yanayin aikinku ne hakan".
Zama tayi kusa da Rukayya tana maida hankalinta akan Zahra.
Patient din dangen ce?"
Ta jefawa Rukayya tambayar, da alamun mamaki a fuskar ta.
Kai Rukayyar ta gyada mata.
"Anyway Bismillah ta fada tana tashi daga gurin ta nufi table dinta.
Zahrar ta Mike tabi bayanta.
Tambayoyi sosai ta rinqa yiwa zahrar wasu har kunya take kamata ta kasa Bata amsa,
tambayar data fi Bata mamaki shine inda take tambayar ta meye tsakanin ta da Mahmud
Dange?"
Kafin zahrar tayi magana Rukayya ta rigata "sister din abokinsa ce daga Bauchi,
kuma matar aure ce Dan naji Baki tambqyeta ba, ita Kuma Bata fada Miki ba".
Wata ajiyar zuciya ce ta kubcewa Dr Haseenar har Saida Zahra ta kalleta.
"Ai ban sani ba Ruky Naga DANGEN yayi matukar damuwa ne ko yanzu kafin na shigo
saida ya kirani yana fada min Kuna Nan Kuna jirana na dubata sosai".
Dan smile zahra tayi kawai ita Kuma Rukayya tace "kinsan halinsa baya Wasa da
rashin lafiya komai kankantar ta, kinsan suna China Aunty Fateeha ta haihu sending
Ya Sameer yayo Nigeria shi ya wuce Dubai".
Dan murmushin itama Dr din tayi "zeyi abinda yafi haka in dai Dange ne yanda ya
damu Zaki dauka matarsa ce wallahi duk yafa rikice kamar ba dangen da Mata ke fada
a kansa ba ko kallo basu isheshi ba Sanda muna school a UK da yawa mutane sunyi
mamakin yanda muka Dade dashi ba wani matsalar data faru fatana ya dawo su hadu da
Daddy ayi a wuce gurin kawai, kinsan halinsa tunda aka samu matsala Nima fa ta
shafeni tunda lokacin da abun ya faru munje gida sokoto shiya Hana ayi abinda
za'ayi ta fice yabar kasar Kinga Banda case din Nan ta sister din friend nan tashi
Bai Kara kirana ba wlh na tura Masa sako ta email dinsa Amma ba reply".
Ita dai zahra ba baka sai kunne wata magana sukeyi wadda ta jefata a kogin tunani
akan Mahmud abinda kunnen ta keji daban abinda yake nuna mata daban.
"Hum lamarin big bro sai a hankali kin sanshi da zuciya kafin dai yayi fushin ana
dadewa Amma idan yayi jam'i yakeyi gurin yanke hukunci sai hakuri komai ze Zama
normal".
Rukayyar ta fada.
Forms ta cikewa Zahra ta test-test Wanda za'ayi Mata ta Mike ta fito daga
mazauninta tana fadin kuzo muje ayi wannan testses din Sai Kuma muje ayi scanning
mu gani akwai abinda nake tunanin yana kawo matsalar Amma bazamu tambbatar ba sai
mun duba.
"To Allah yasa a Dace" Rukayya ta fada.
Sai da suka Fara zuwa lab sannan suka nufi radiology department inda za'ayi hoton
cikin.
Dr karima ce tayi mata scanning din tambayoyi ta Riga yiwa Zahrar harta gama.
Basu jira karbar result din ba, da safe doctor Haseena zata shiga dasu can Asibitin
malam Aminu inda za'a mata saura gwaje-gwajen Nan sun Dan rage ne saboda cunkoson
can din.
Har gurin mota doctor ta rakasu suna 'yar tsama da Sameer, sannan sukayi sallama
Sameer na Mata godiya saboda taki yarda ya biya ko sisi tace patient din DANGE nata
ne, itama Zahrar godiya tayi Mata Rukayyar ma haka.
Har Sameer yayi ribas doctor Haseena ta daga Masa hannu alamun yazo gyara parking
yayi ya fito ya nufo inda take a gefen baranda.
"Yana zuwa Bata jira komai ba ta Fara tambayarsa cikin nuna damuwa Dan idanunta har
Dan ruwa ya taru a ciki da gani tana cikin damuwa da tashin hankali.
" Wannan yarinyar wacece a gurin DANGE?"
Iska ya Dan huro daga Bakinsa ya hade hannuwansa a kirji Yana kallonta kawai.
"Me yasa Kika yi min wannan tambayar?"
"Just pls answer me who's she?"
"Abinda ya fada Miki da farko yanzu ma dai shi zan maimaita Miki, kanwar friend
dinsa ce daga Bauchi sukazo Kuma matar aure ce abinda na sani kenan".
"To Amma me yasa ya shiga damuwa akan lamarin ta ya hanani sakat Ni Kuma nasan
wannan ba d'abi'ar DANGE bace".
"To ki Kira shi kiji gaskiyar magana daga Bakinsa Mana".
Ya fada Yana kokarin barin gurin.
"Kada kaji haushina na kasa samun nutsuwa ne"
Bai tsaya ba Dan da gaske nema take ta karya Masa gwiwa har yayi abinda baze musu
Dadi ba, gara taji daga baya a bakin wani ba shi ba, Daman yasan za'a Rina dole ta
kawo wani Abu a ranta yanda ya nuna damuwa akan lamarin Zahrar.

Jiki ba kwari ya dawo motar ya tada yabar gurin, har lokacin tana tsaye Bata bar
gurin ba. Shi kansa yaji Babu dadi a ransa yanda Haseena ta mace akan Mahmud tun
suna UK yasan idan taji yayi aure ba Kara min tashin hankali zata shiga ba.
Sai da sukayi nisa da Asibitin sannan Rukayya tayi magana "Dan Allah Yaya kaimu
murtala Muhammad way zanyi sayayya a Nameer Sale".
Tsaki yayi kadan da gani ranshi ba dadi, "nifa baba son yawo kinga ai saimun koma
baya, me yasa Baki fada min ba tun kafin mu fito nasan da zuwan".
"Kayi hakuri mantawa nayi Amma muje gobe in Sha Allah naje kawai".
Bai Kara kulata ba haka zahra Bata tofa tata ba.
Yana zuwa round yayi ya dawo ya nufi murtala Muhammad way din, tare suka shiga da
Sameer din yace zahra ta duba abinda take so, har Rukayya ta Gama daukar abinda
tazo nema zahra Bata dauki komai ba, ganin haka yasa Rukayyar ta daukar mata kayan
shafa dasu turarikan gashi Dana wanka shi Kuma Sameer ya daukar Mata dangin su
wafer da ice cream, a hanya hira sosai Rukayya keyi musu Amma ita Zahra hankalinta
Yana Kan maganganun doctor ita fa abin yafi karfin tunanin ta ke nan da lauje cikin
nadi, shin waye uban gidan wani tsakanin Mahmud da Sameer idan ba kunnenta ne baiyi
daidai ba taji Rukayya na cewa Mahmud ya Turio Sameer gida daga China ya wuce Dubai
zance yayi dai dai Dana Fateeha matar oga Sameer lokaci tafiyar su.
Har suka shigo unguwar hankalin ta baya tare da ita tayi zurfi cikin tunanin
makomarta kodai yanda ya taba fada Mata Yana yaudarar matan ne ya gudu dasu tunda
yanzu yasa an dauko su ba Wanda yasan inda ya kawo su daga Rukayyar har Sameer din
ba Wanda yasan takamaimai Ina ne asalinsu an kawo su ita da baiwar Allah an killace
su a wannan uban gidan kamar resident na matar shugaban kasa.
Sai da Rukayya ta Dan tabata lokacin da suka tsaya a kofar parlourn Dan da gaske
tayi mugun zurfi a tunanin Dan zabura tana Fadi. "wallahi har naji tsoro".
"Ai ke dince Ina ta magana Amma kinyi Zurfi a cikin tunanin, ki rage yawan tunani
saboda lafiyarki kinsa Yana shafar lafiyyar Dan Adam".
"In Sha Allah Zan Dena na gode".
Ta yungura ta fito Bata jira ba ta nufi kofar shiga tana fadin oga Sameer sai da
safe kaina yake Dan Sara min a shafa min Kan Abeed"
Dariya Sameer.
"Zeji in Sha Allah Banda mamansa ko?"
"Kaina bisa wuyana na Isa ayi min gaisuwa, zanzo muyi jegon tare".
Wani kallo Rukayya tayi Mata tayi wani killer smile ta matso daidai kunnen ta
"saurin me kikeyi in dai jego ne kamar yaune kinsan Yayana ba rago bane daina
gaigaye zakiçi tumo".
Tayi gaba abinta kamar Bata Fadi komai ba. Ido Zahra ta zaro tabi bayanta da kallo,
ta fuske kamar ba ita ta Fadi maganar ba.
Ganin haka yasa Sameer ma ya basar ya dauko wasu ledojin yabi bayan Rukayya data
dauko wasu.
A Nan parlour sukayi sallama da Sameer ya tafi, su zilan Basu tashi daga kallon ba
suka Yi musu sannu da zuwa tare Da tambayar ya jikin nata, bata jima ba ta dauki
kedar cosmetic din da robar ice cream Daya da biscuits da chocolates ta nufi hanyar
masaukinta tunda yace Mata ba komai a gidan da tsaro sosai ta Sami kwari gwiwa da
kwanciyar hankali, tana barin gurin ta dauko wayarta ta kasheta gaba daya tana
fadin.
Wallahi kwana kusa ba zasu gaisa ba tunda shi wani irin mutum ne marar Alqibla.
Kuma tafiyar ta zatayi ta koma inda ta fito haka kawai Kullum ita kenan cikin
matsala gara ta koyi jajurcewa itama kowa ya samu dama saiya ringa dokata kamar
wata ball impossible wallahi".
Ta fada tana zura katin bude kofar ta shige ciki, a Kan sofa ta zube kayan ta shiga
cire kayan jikinta Daman duk sun dameta, wanka ta shiga Dan wallahi barci takeji,
barcinta zatayi tasan mutum Bata wuce kaddararsa.

******

A gajiye ya shigo masaukinsa yau throughout bai samu hutu ba, hankalinsa gaba Daya
yayi gida so yake ya ganta ra'ayal ain bawai ta wayar ba yaji dumin jikinta ya
tarairaiyi kayarsa suyi barci tare su tashi tare ya gaji da watangaririyar Nan gara
ayi wadda za'ayi kawai game din ya Zama over.
Saida yayi wanka yayi order coffee sannan ya janyo wayar ya shiga nemanta da gaske
yayi kewarta ba kadan ba, shifa yana ganin yarinyar Nan itace weakness dinsa duk
inda take tana manne a kirjinsa ko barci yake itace a cikin barcin idan ba ganinta
yayi ba ko yaji muryar da da akwai damuw, yaga alama any nan gaba ze iya kulla wani
abun arziki kuwa? tun yanzu da gishiri bai Sha Kan kazar ba yana jinsa haka Yaya
idan labarin ya sauya salo?
Abin mamaki wayar switch off.
Zuru yayi Yana kallon wayar "me kenan?"
Yasan dai ba matsalar charge bane, Sameer ya Kira, duk da basu Dade da Gama waya
ba.
Sameer yayi mamakin ganin wani Kiran nasa.
Kafin Sameer ya Kai ga magana Mahmud ya Riga shi.
"Meya faru ne a Asibitin naji wayarta a rufe ko jikin ne ta tashi da akayi Mata
gwaje-gwajen?"

"A'a gaskiya normal muka dawo har muka biya nan Murtala Muhammad way sukayi sayayya
Kasan Rukayya bataso a zauna lafiya,idan tajita da kudi ba zaman lafiya. Dan Allah
ka daina turo mata kudi har madam tabar garin nan, kasan Ruky da yawo Kullum aka
fita saita qirqiro zuwa wani gurin, wani Abun ne ya faru yanzun ?"

"A'a ba komai, kada ka manta da maganar kayan da za'a sauke gobe a Nan kanon a
turasu can Azaren munyi magana da Habib dazu".
"Ok in Sha Allah".
Sukayi sallama, ji yayi baze iya fada masa komai ba. Wayar ya aje kusa dashi wani
tunani yayi sai yaji dariya ta kubce masa "zakiyi bayani da yaren garinku yarinya
duk yanda akayi taji wata maganar yanzu a Asibitin yasan Haseena farin sani yanda
yaji ta damu da sanin relationship din dake tsakanin sa da zahra yasan zatayi duk
yanda zatayi ta shigo da wata maganar wadda zatayi touching dinta tunda shekarun da
wayonsu ba Daya bane.

Itama Zahra kasa cin komai tayi fridge ta bude ta saka ice cream din da chocolates
tayi kwanciyar ta bayan tayi Addu'a, amma barcin Kuma yace baisan zancen ba, tashi
tayi zaune a tsakiyar gadon tana tariyo rayuwarta ta baya "ko yaushe Zan Zama
stable a rayuwata? sai hawaye suka zubo Mata "Ubangji ka hanani ganin bakin cikin
gidan Aure, lamarin Yana neman yafi karfina ka jibinci lamurana Dan isar fiyayyan
halitta Annabin Rahama Muhammad s a w.w.
Bansan ko waye ba wannan bawan naka, kafini saninsa ka amintar Dani a cikin
lamarinsa daka barni na tozarta, ka kareni daga dariyar makiyana Ubangiji kasan ko
suwaye suke mini yankan Bata a cikin lamarina, kayi min kariya ka bani juriyar
abinda ka jarrabeni dashi kasa ya zamar min kaffara.
Tasa tafin hannunta a fuskarta taAUREN HUCE HAUSHI.

MAMAN FATEEMAH.

Page 40.

______ karfe takwas saura Zahra ta fito cikin shigarsu ta asali doguwar Riga
baka Mai aikin zare maroon sai kananan stones har kasa,tayi rolling da maroon din
veil, cikin takunta na rausaya take gannaro steps din, tana baza sansanyan kamshi,
ba kowa a parlourn sai wani sanyi da kamshin freshners ke tashi, Dan Jim tayi tana
tunanin ta koma kota zauna sai Kuma ta jiyo alamun motsin kwanuka a kitchen gurin
da taga suna shiga ta nufa tunda ba sanin Kan gidan tayi ba, tunda ta shigo
iyakarta Nan sai Kuma bedroom din da take, tana dosar gurin wani kamshin girki yayi
Mata sallama, babban kitchen ne na zamani Mai kunshe da na'urori birjik kamar a
wani babban Hotel ko irin modern restaurant din nan iya Rahane ta gani tana yanka
wani Abu yayin da zilai ke tsaye tana duba wani abu a tukunya.
Sallama tayi musu tana fadin "Ina kwanan ku".
A tare suka juyo suna amsawa tare da fadin "ya Kika kwana da jikin?".
Dan juya Kai tayi tana fadin. "Nifa Babu abinda ke damuna kawai dai Dan a dunga
yawo ne da Bata lokaci, wallahi har kunya nake ji" .
"A kul Kika Kara fadar haka tunda mijinki yace Kizo a duba aga menene matsalarki
kada ki watsa Masa qasa a Ido ki sage Masa gwiwa akan kokarinsa, kije idan Allah
yasa Babu komai shike Nan idan Kuma anga abinda ke kawo ciwon a magance shi".
"Wannan gaskiya ne".
Zilai ta fada tana sauke girkin.
"To in Sha Allah na daina iya".
"Yauwa kokefa fa ai idan Kika Fara da haka ko lalular da tafi haka baze Maida
hankalinsa ba duk da ba fata ake ba".
"Dan Allah Aunty zilai bani wayarki na Kira Ammah tawa tun jiya ta kashe kanta taki
kunnuwa".
Ta fada tana istigifari a zuciyar ta Dan tasan karya ta shara.
" To Bari na dauko Miki tana can a daki"
Ta wanke hannunta ta nufi kafar fita Zahrar tana biye da ita, sai da suka fito
zilan ta kalli Zahra "uwar dakina Dan Allah Wai Kinga kuwa dakin da aka ajeni a
ciki Dan Allah muje kiga wannan duniyar da aka sakani kamar dakin gidanki,to acan
dai bana Hawa gadon Amma wannan akai na kwana har naso in makara Allah yasa ita Iya
Rahane Bata makara ba".
Dariya Zahra tayi tana fadin "daina fada Aunty zilai sai a Raina mu wallahi, muje
Naga dakin naki Daman ban San inda kike ba Koda tsoro ze kamani sai nayo gudun
hijira".
A parlour na biyu suka shiga wani corridor bazaka taba cewa da dakuna a gurin ba
steps ne kamar goma suka haura sama Nan ma wani parlourn ne da two three bedrooms
biyu suna kallon juna sai Daya daga gefe.
"Masha Allah" Zahra ke fada a zuciyar ta tana mamakin gidan Wai wane irin gida ne
wannan gari guda compartment guda kawai ya hada irin wadannan mahaukatan falukan da
bedrooms din Nan to yaya sauran parts din suke?.
Dakin dake hannun hagu ta nufa ta bude, daga inda Zahra take ta hango wani Royal
bed milk Mai azabar kyau, Bata Kara gaskata maganar zilan ba Saida ta shiga ciki, a
gefen bed din Zahra ta zauna tana fadin "Bari na Dana gadon Aunty zilai".
Dariya sukayi su suka "kin gani ko wallahi nifa a jiya da kyar nayi barci duk
zulumi ya isheni ji nayi Ina tsoron gidan yayi girma da yawa, na jinjinawa matar
gidan".
"Wai Mai gidan Bai taba aure ba a gaba dai ze kawo matar".
Baki zilai ta Kama tana fadin "to shi wane irin kudi ke gareshi da ze Gina irin
wannan gidan Yana saurayinsa".
"Bani wayar Aunty zilai wannan hirar ba karewa zatayi ba kada lokaci ya kure yau
daga Asibitin cikin gari zamu gidan su oga Sameer na gaishe da mommy". Wayar ta
Bata suka fito tare ta Kira Ammah suka gaisa sun jima tana fada Mata abubuwan da
akayi mata jiya da Kuma komawar da zasuyi yau, karfafa Mata gwiwa itama Ammar tayi
tana fada mata ta kwantar da hankalinta In Sha Allah ba komai.
Lokacin da suka fito har Iya Rahane ta shirya table din Rukayya ma ta fito.
Kallon su Rukayyar takeyi ganin daga bangaren da suka fito.
"Aunty Rukayya Ina kwana?"
Zahra ta fada.
",Lafiya kalau matar big bro, ya Naga kin fito daga bangaren mu".
"Au kema a can Kika zauna kika ki zama a dayan dakin kusa Dani".
Baki ta bade tana kallon Zahra. "Na shiga dakin Mai gidan na zauna tab ai wannan
part din sai ku".
"Mu suwa daga zuwa bakunta sai mu zaqe Ina laifin can din wallahi transfer zanyi,
Ina dalili Ni kadai kamar mayya kufa Nan ku uku ko ihun neman taimako kayi an
taimaka maka amman Ni kuwa ko kasheni za'ayi sai dai a dauki gawar da safe".
"Tab wallahi ba inda Zaki zauna a Nan ba haka big bro yace ba,a can yace ki zauna
Dan haka Babu Mai canza wannan Umarnin".
Dan turo Baki tayi "Ni na taba ganin haka mutum ya ringa saka doka a gidan mutane
inaga baisan girman gidan ba shi yasa yake bada wannan Umarnin, gaskiya da sake".
Time Rukayya ta duba a waya kizo muyi break yanzu zakiga ya Sameer yazo tunda da
wuri za'ayi Miki sauran gwajin".
Suna cikin break din Sameer yazo Saida ya jira a mota suka Gama sannan suka tafi, a
ANC department suka samu doctor Haseenar sun awon ciki.
Ba yabo ba fallasa ta tarbesu ba kamar jiya ba ko yanda suka ringa Yi jiya da
Rukayya yau ba haka bane daga gaisawa Bata Kara cewa komai ba, itama Zahra saita
Kama kanta Rukayyar ma haka. Gwajin jini ta Kara tura Zahrar ta hadasu da wata
ma'aikaciyar su ta rakasu main lab aka dauki jinin.
Lokacin da suka dawo sun Gama ante-natal din gwajin jira ta dauko da scanning din
ta Kira Sameer tana fadin mu hadu a office dina".
Ta kashe tana fadin Bismillah Ruky muje office dina tunda mun Gama da Ante-natal
sai zuwa anjima zamu Fara gyne".
A kofar office din suka samu Sameer din ya rigasu zuwa.
Sai da suka zauna sannan suka gaisa da Sameer din, bayani ta farayi Masa na gwaje-
gwajen jinin jiya "a cikin jininta ba wata cuta ko kadan kawai scanning ne ya nuna
Mana akwai matsala a mahaifarta ta fibroid amman be wani girma sosai ba za'ayi aiki
a cire mata tun kafin ya girma Amma zamuyi admitting dinta zuwa one week tana
karbar magani kafin ayi surgery din, Dan haka sai ta Kira mijinta ta fada masa yazo
da mutane muna son jini leda biyu, zamu jira results din Nan ya fito total blood
count za'ayi Mata".
Rukayya ce tayi farat ta tambayi doctor Haseenar "yanzu dole sai tiyata baza'a iya
Shan magani ba a warke?"
Kallon tsab Dr Haseenar tayi Mata kafin tace "hanya mafi saukin rabuwa dashi ta sai
dai aikin gaskiya".
Tunda doctor Haseena ta Fara bayani gaban Zahra ya yanke ya Fadi idan da abinda
taki jini a rayuwar duniyar Nan to tiyata ce.
Nisawa Sameer yayi kafin ya samu karfin halin fadin.
"Thank you so much doctor kome kenan zakiji idan munyi communicating da mijinta
saina kiraki later"
"Ok.ba damuwa Allah ya sauwaqe".
"Amin".
Rukayya ta fada Dan zahra ba bakin magana har suka shiga mota tana cikin tashin
hankali, kuka takeyi irin na zuci din Nan sai dai hawaye kamar an bude famfo.
Saida suka fita daga Asibitin har sun shiga court road sannan Sameer ya Dan juyo,
Madam kiyi hakuri in Sha Allah ba wata matsala idan Allah yasa yin surgery din ne
yafi Alkhairi ayi kawai Kinga kema saiki huta da zulumin ciwo duk wata".
Rukayya ce juyo tana fadin "gaskiya kada ki yarda a yanka ki haka kawai Ni banma
yarda da maganar Haseena ba, kawai ta jawo Miki wahala Ni Daman da anyi shawara
Dani da Babu abinda zesa Haseena ta duba matar big bro haka kawai taje ta jawo Mata
matsala da gangan bakaga yau sai wani share mutane takeyi ba, wani ya Hana big bro
din ya aure ta".
Wata uwar harara Sameer ya zubawa Rukayya "Billahillazi Zan saukeki a Nan ke wace
irin mutumce da bakinki bashi da controlto me kikayi ke Nan? wannan ai shashanci ne
keda Zaki kwantar Mata da hankalinta shine Kika sokawa zancen wuqa".
Ita dai Zahra maganganun Rukayya sun daga Mata hankalin kenan da wata jikakkiya a
tsakanin wannan likitar da Mahmud.
Wallahi ko likitoci sun Kare wannan ba zata Kara dubata ba shi yasa Kennan jiya ta
damu da sanin waye mijinta da dangartakar ta da Mahmud.
Tunda Sameer ya yiwa Rukayya buyagi Bata kara magana ba har sukazo junction din
gidan shatima. "Wai yaushe mommy taje gidan Hajyr makwararin?".
"Dazu da safe na kaita Wai zasu karbi lefen mujahida".
"Ok Allah ya Sanya Alkhairi. Dan Allah ya Sameer Zan sayi alawar Madara idan ka
tsallaka Zan kaiwa Hajiyar makwarari".
"Kice dai Zaki saya bawai Zaki sayawa Hajiyar makwararin ba".
"Allah tana son shi sosai"
A kofar gidan Hajiyar yayi parking Babar mommy ce.
Da karadi Rukayya ta shigo gida yayin da Zahra da Sameerke biye da ita a baya,
suna runfa ana hira da kunnen Rukayya da 'ya'yan dangi da mommy masu karbar lefen
basu Fara zuwa ba gaishe dasu yaran sukayi suka fice, sukabar mommy kawai. Cikin
nuna kulawar mommy ta kalli Rukayya dake gaba. "Ba dai har kun gama da asibitin
ba?"
" Mun Gama kin ganta Nan Wai doctor Haseena tace zata yankata tayi Mata tiyata Dan
nace ban yarda da ita ba shine ya Sameer yake ganin bekena".
Sallama Zahra tayi tana Dan tsugunnawa tana gaishe da mommy cikin muryarta Mai
sanyi da nutsuwa da Kuma alamun tasha kuka.
Mommy kallonta tayi tana fadin "Masha Allah tabarakalla sannu ya jikin naki?"
Da sauki sosai".
To Allah ya Kara lafiya naji Rukayyar na fadin tiyata za'ayi Miki".
"Eh haka suka fada"
Hajiyar makwararin ce ta fito tana fadin "wa nakeji kamar Rakiya a gidan nan waye
ba lafiya naji ana magana tiyata".
" Kin ganta Hajiya, matar Mahmud mutumin ki ce".
Mommy ta nuna zahra.
" Wai Amaryar ce? Sannu kinji menene ya sameki?"
Rukayya ce ta fada Mata.
Mommy ta kalla "Ni Zan hada Mata maganin wannan lalurar ba sai anyi Mata aiki ba,
ki huta Rukayya ki shiga Nan kurmi ki sawo min abin hada maganin a Nan na hada Mata
insha Allah sai dai ya narke yabi jinin al'ada.
"Amma gaskiya ba wanda ze yanka ta Kamar kabewa ku 'ya'yan zamani komai a yanka ta
haka ne daji yake shiga ai ta fama da rai idan yazo da karar kwana kiga an mutu,
daina kuka, samiru kiwawo min mijin nata na fada Masa da bakina Babu me yi Mata
danyan aiki ko haihuwar fari Bata yi ba a jawo mata tsuguniya mazan yanzu marasa
hakuri".
Ta fada tana nufar uwar dakanta.
Ita dai mommy Shiru tayi Saida Hajiyar ta shige sannan ta dubi Rukayya "Wai Ke Sai
yaushe hankali ze Gama Miki jiki? Kinzo kin kwatsa zance gashi Nan kin tubzura
Hajiya Mai hanata hada maganin Nan sai Allah, itama Kuma Mai lalurar maimakon ki
kwantar mata da hankalinta A'a tashin farko kin sokawa zancen wuka, ai kin kyauta".
"Wallahi ba haka bane mommy Kinga dai muna good term da Haseena amma wallahi yau
kamar ma Bata taba gani na ba sai cin magani take yiwa mutane da dacin rai want ya
Hana Ya Mahmud din ya aureta taga yarinya ta gigice zatayi mata illa haka kawai".
Maficin dake kusa da ita Mommy ta jefawa Rukayya tana fadin fita ki bani guri tunda
kin Zama babbar kwabo kin tasa yarinya gaba kina fadar abinda be Dace ba".
Wata uwar harara Sameer ya saukewa Ruky ji yake kamar yayi Mata duka duk ta cakude
lamarin tana kokarin ta saka jinin yarinyar mutane ya hau, tun sassafe Mahmud ya
Kira shi Yana fada Masa ya kira Rukayya yace ta fadawa Zahra ta bude wayarta ya
manta shaf sai fa yanzu ya tuna.
Wayarsa ce ta Fara ringing "shine ya kira" ya fadawa mommy.
"Ka dauka kayi Masa bayanin halin da ake ciki".
"Nasan Haseena ce ta fada Masa shine ya Kira yaji".
Wayar ya saka a speaker yanda zahrar ma zataji.
Bai jira komai ba ya Fara fadin "Sameer wace magana naji Haseena tana fada min?
kada ka Bari su taba min yarinyar nan Zan kaita inda ya Dace, naji tana fada min
wasu nonsense wallahi idan na shigo saina Bata Mata rai, ita harta isa ta fada min
son ranta who is she? Yanzu ina ita zahran take? Tun jiya jikina ya bani an samu
problem wayar ta fa ta rufe ta Hana nayi magana da ita fa".
Tashi Sameer yayi tsam ya fita ya cire wayar daga speaker saboda kada yayi
katobara.
"Gamu Nan a makwarari gidan Hajiya Zahrar sai kuka takeyi,ita Kuma Ruky sai tinzira
ta take kada ta Bari a yankata har Hajiyar makwarari taji tayi tsallen Albarka tace
bata san wannan magana ba, ita zata hada Mata maganin hausa Wanda ze narke ciwon,
wallahi sun caza min kai har na rasa yanda zanyi da rigimar Hajiyar, yanzu haka
kasuwar kurmi zata aiki Rukayya ta sawo Mata mahadin maganin da zata hadawa
zahrar".
"Yanzu dai bazan Gane kome kake fada ba hadani da Zahrar muyi magana"
"Ok Bari na kira ta dakin mujahida Naga ba kowa a ciki ka kwantar Mata da hankali
duk ta shiga damuwa sosai sai kuka takeyi"
Rukayya dake zaune a tsakar gida ya yiwa nuni data Kira Zahra, lokacin da suka fito
Yana tsaye suna ciga da maganar.
Wayar ya Miko Mata ya nuna Mata dakin mujahida yayi nufi waje.
Tana shiga cikin dakin tana Jinsa Yana faman hello, hello tayi shiru karshe ma ta
sakata wayar a flight mood tayi kwanciyarta a katifar mujahadar tana goge hawaye.
"Me kake son fada min Kuma? naji komai me Za'ayi bazan zauna a garin Nan ba
wallahi, gida Zan tafi kuma idan ma ciwon ne ai Ina da inda za'ayi min maganin ba
sai Nan ba, da gata na da komai na zauna sai watangaririya nake yi Dani".AUREN HUCE
HAUSHI.

MAMAN FATEEMAH.

Page 41.
________Wani irin barci me nauyi yayi awon gaba da zahra, sai da Sameer ya shigo
yace Rukayya ta duba Masa Zahra oga ya Kira yace Masa da matsala.
Dakin Rukayya ta shiga ganin Zahrar tana barci ga wayar Ya Sameer a gefen ta,
daukar wayar tayi tana dubawa a airplane mode taga wayar 'yar dariya tayi tana
fadin "good yarinya kinsan kanki kenan ai Ina bayanki ki tsaya tsayin daka akan
wannan mijin naki idanun Mata a kansa suke kinyi dai-dai wallahi".
Wayar ta cire daga flight mode din tayi waje da sauri tana fadin "gashi ya Sameer
wallahi barci takeyi" .
Wayar ya Karba Yana dubawa gashi Nan a kunne take haka datar itama ba wani matsala.
Tsaki yayi kadan Yana fadin "duk nema suke su dagulamin lissafi wallahi har na rasa
Yanda zanyi" .
Rukayya najinsa tayi Shiru haushinsa takeji tun buyagin da ya yi Mata dazu,waje ya
juya ya fita Yana kokarin Kiran waya.
Hajiyar makwarari ce ta fito daga daki da manyan tabarmin roba a hannu tana fadin
"zo Nan Rakiya ki shimfida su cikin baranda kafin mutane su Fara taruwa".
Zuburo Baki tayi "Allah ki daina fada min sunan nan ni sunana Rukayya haka a ringa
batawa mutum suna".
Ta taso tana karbar tabarmin.
"Gidanku, nace Rakiya ba sunan ki bane, Kizo ki shiga kurmin ki karbo min masoro
gurin Alhajin Baba nayi na hadawa yarinyar Nan magani na Bata tun yau ta Fara
amfani dashi ba'a bori da sanyin jiki".
Saida ta Gama shimfidar ta shiga gurin Hajiyar cikin falonta suna duba kayan da
za'a bawa masu kawo kefen robar da aka zuba chicken pepper ta bude tana fadin
"bari na dauki Daya naji kamshin yayi min Dadi".
"Ki rufe wannan gashi can a kitchen a waje ki diba harda snacks din duka, Amma ki
Fara karbo Mata sakon a kasuwar tukunna kuje da sadiya ta rakaki ku shiga a dai
daita tunda ba nisa ga cunkoson cikin kasuwa Kuma kinsan Sameer baze Baki motarsa
ba, wadda mukazo da ita Kuma Aliyu yayi nasa gurin da ita".
Basu dauki minti talatin ba suka dawo da sakon har lokacin Zahra barci take sai da
jama'a sun Fara taruwa a gidan duk dangi need sai dai-daikun Yan uwan mahaifar
mujahidar.
A blender hajiyar taba mommy ta nika Mata masoron ta juyo mata shi a cikin robar da
Hajiyar ta bada a zuba a ciki.
Lokacin da mommy ta kawo Mata Hajiyar da kanta ta nufi dakin mujahidar tana fadin
"Ina matar Mahmudun take?.
Barcinta take sadidan Dan tabata Hajiyar tayi tana fadin. "Tashi 'yar nan ga
maganin lalurar ki da izinin Allah".
Tashi zahrar tayi tana bin Hajiyar da kallo lokacin data aje robar kusa da ita.
"Bude ki gani sai nayi Miki bayanin yanda za'ayi dashi".
Batayi musu ba ta bude robar taga garin masoron.
"Kina jina? Abinda za'ayi dashi ki ringa diba Kashi Daya bisa hudu na karamin
cokalin shayi kina zubawa a ruwab zafi tafasashshe cikin kofin ok ki barshi yayi
minti ashirin a ciki sai ki tace ki Shanye ruwan,haka Zaki ringa yi har ya Kare in
Sha Allah ze narke yabi jinin al'adarki ya fice, ki rabu da wannan shirmen komai
ace za'a yanka mutum kamar kabewa"
'yar dariya Zahra tayi tana fadin in Sha Allah zanyi na gode madallah Allah ya saka
da Alkhairi".
"Allahumma Amin. Allah ya Baki lafiya,ayi ta hakuri irin mijinki Mata Ido rufe suke
nemansu sai kin kauda Kai zakiçi ribar zaman aurenki. Amma kada ki kuskura ki yarda
a nuna Miki San iyawa akan mijinki, ki kula da sukarki Bata da damuwa ko kalilan ki
girmama Masa danginsa da kakarsa jiya ya wannan suna gidan Nan sunzo ganin Mai
sunan mijinki na wurin Sameeru, Ni cewa nake can wurinku zasu sauka ma sai naji
Sameeru na maganar su fito zasu koma a jiyan kinsan sha'anin tafiyar iska, ba wani
nisa ke gareta ba".
Ita dai Zahra Jin Hajiyar take Dan ba komai ta fashimta ba.
Rukayya ce ta shigo da Abinci dasu snacks a babban tray tana fadin " Ai tunda naji
shiru Hajiya Baki fito ba nasan kin hanata barci kawai wallahi ke idan Kika so Abu
ba sauki saina Allah idan kinyi hakuri zata tashi ki bata".
"Ke tafi can waya fada Miki ana bori da sanyin jiki Baki San hadarin wannan abun
bane baya barin haihuwa fa ba dole a tari abun ba tunda wuri, wannan yarinya
tubarakallah haka ai ba'aso a samu abinda ze kawo Mata cikas a zaman aurenta ba, ni
tunda na ganta ta kwanta min har maganin tsarin jiki Zan karbo mata a Sanka, nan
babban gida".
Baki Rukayya ta rike tana kakabin Abun "Ikon Allah to ke Hajiya fada Miki tayi tana
son na tsarin jikin? Da kike faman fadin Zaki karbo Mata".
Kafin Hajiyar ta Kara magana Zahra ta rigata.
"Haba Aunty Rukayya Ina laifin Hajiya kuwa tunda na sako Qafa gidan Nan Bata huta
ba hidimata takeyi".
"Eh haka ne kam tunda har kasuwar kurmi ta aikeni, da girnana da komai nace bazanj
ba tace nayi mata kiwa dan rabon da naje cikin kurmi tun Ina secondary Dan ma ban
manta shogon ba"
Ficewa Hajiyar tana fadin kyaji dashi idan Kaya ne".
Tashi zahrar tayi tana fadin Bari na dawo, ta fice daga dakin.
Toilet ta shiga ta Kara gyara Kanta, lokacin data fito dai dai lokacin masu kawo
lefen suka karaso suma Nan da nan gudan ya dauki jama'a Dan makota ma Wanda suka
makara suka ringa shigowa.
Ganin gidan ya kacame da jama'a yasa Zahra tayi amfani da wannan damar ta nufi
hanyar soron gidan, a soron ta tsaya ta Ciro wani face mask da yake cikin jakar ta
da eyeglasses dinta ta saka ta fice daga gidan.
Ba Bata lokaci tana fita Dan sahu Yana kawo Kai, ta dafe shi ta shige, tana fadin
"Janbulo zaka Kaini".
"Hajiya sai dai drop gaskiya Dan hanyar ta baude ni rimi na nufa".
"Muje Zan baka kudin drop din".
Ta fada tana Dan leken gefenta kamar narar gaskiya, hankalinta be kwanta ba sai da
taga sunyi nisa da unguwar, ajiyar zuciya ta sauke tana "na barka da Dr Sai ku
cinye kanku haka kawai za'a sabautani saboda Kai,Wanda har yanzu bansan daga wace
bahiyar ka bullo ba, ayi min sakiyar da Babu ruwa a cuceni a cuci rayuwata shi yasa
na taho da hirina idan tayi ruwa rijiya idan batayi ba ta Zama Masai"
Kafin su karasa layin su Ssjida tacewa Mai adaidaita din ya taya gurin me P. O.S
zata ciri kudi.
Har kiofar gate din gidan ya kaita 10k ta bashi, cikin mamaki ya dubeta "Hajiya
kudin sunyi over dari bakwai ne kudin, Hala ke bakuwa ce?"
Gaga tayi Tana fadin na sani kaje kawai nagode Allah ya tsare".
"Na gode Allah ya rufa asiri ya kara Miki daukaka".
Tana tafiya tana fadin. "Allahumma Amin".
Ta shige gidan shi Kuma ya juya Kan mashin dinsa ya wuce Yana Fadin "Bari na koma
na sallami gidan sai na Kara fitowa".

***********

Bayan tafiyar masu kawo lefen an baje anata kallon kayan arzikin da suka kawo
Masha Allah kayansu sunyi kyau sosai Dan akwatuna set hudu suka kawo da manyan
jakunkuna uku har da adudu biyu.
Saida komai ya lafa sannan hankalin Rukayya ya dawo jikinta ta shiga neman zahra,
abin mamaki ba zahra ba alamarta Abu kamar Wasa ya Zama gaske Nan da Nan tashin
hankali ya wanzu a gidan Dan mantawa akayi da murnar wani lefe Nan da Nan Rukayya
ta Fara share hawaye.
Mommy ce ta Farayi Mata fada "Haba Rukayya menene haka Zahra Karamar yarinya ce ku
shiga makota Mana ko taron jama'a ne bataso ta shiga can ta zauna ba kince toilet
tace Miki zata shiga ba? Kafin ta fito Kuma bakin sun shigo?"
"Eh haka ne Amma Naga fitowarta harta tsaya a can daga Nan mutane sukayi yawa ban
sake ganinta ba".
"Ke Zubaida maza ku shiga gidajen kusa ku duba ko can ta shiga ku kirawota".
"To mommy". Ta fada sukayi waje su uku.
Hajiyar makwarari kuwa cewa take "Ina yarinyar nan ta shiga ko masu kawo kayan tabi
suka tafi".
Wani kallo Rukayya tayi Mata "kaji Hajiya da wani zance kamar wata 'yar baby ce
zahrar da zatabi wasu mutane".
"Ungo Nan".
Abu kamar Wasa karamar magana tana neman Zama babba, duk kukkuken babu it's Babu
dalilinta komai Kama da Zahra Babu.
Mommy da Kanta ta Kira Sameer tace duk inda yake yazo yanzu tana son ganinsa.
Daman ba nusa yayi ba Yana tare da abokansa na unguwar Dan a hannun Hajiyar ya
girma harya Gama secondary school dinsa.
A tsakar gida ya samu su mommy anyi cirko-cirko.
"Gani mommy lafiya na ganku haka?".
Hajiya ce ta Fara fadar "Ina fa lafiya ba'aga matar Mahmudu ba har makota anbi baku
ko alamarta".
Mommy ya kalla. "Kamar ya ba'a ganta ba? To Ina ta shiga?"
"Allahu A'alam, da farko abin ban dauke shi haka ba sai yanzu da naga da gaske ne
yasa nace Bari na Kira ka".
"Ok, Bari naje Nan Ina zuwa"
Ya juya ya fice da sauri, cikin tashin hankali me ze fadawa Mijinta Ina ta tafi?.
Tambayar mutanen kusa masu sana'a a kofar gidan ya rinka yi, har ya juya sai wani
Mai sayar da Mai yace yaga fitowarta da face mask da glass a Ido ta hau a dai-
daita sahu sunyi hanyar nan ya nuna hanyar gidan shatema.
Dafe Kai yayi cikin tashin hankali, "wannan wace irin masifa ce haka kawai an
tadawa yarinya hankali har ta yanke Shawarar tayi tafiyar ta, to tana Ina? Ina ta
tafi? Ba wani ta sani a garin Nan ba ga Babu waya a hannunta, Saida ya fada masa ya
fito Mata a mutum sak a wuce wannan wasan yaran ya kaita inda ya Dace a duba Masa
ita amma ya gano ya yiwa Haseena waya ta a duba Masa ita yasan karshen film din ba
Mai kyau bane"
Jiki ba kwari ya koma ciki..

***** ***** *****

Hankalin Zahra be kwanta ba so sai Saida ta ganta a cikin falon gidan su Sajida,
Mai aikinsu ta bude Mata parlourn tana fadin "A'a marhabin maraba da Amarya sannu
da zuwa".
Ta fada tana murmushi, tare suka shigo ciki.
"Yauwa Mama Hauwa sannu da gida, ya naji gidan naku Shiru ko su Mamar basa nan
ne?"
"Wallahi sunje Rimin sumaila duba kanin Baffa bashi da lafiya,a nan ya kwanta a
Asibitin Murtala to shine sukaje su Kara duba shi da jikin".
"Allah sarki ko kawu Musa?"
"Shine Ashe kin sanshi".
Eh nasan shi Mana, har a gidansa mun kwana lokacin da mukaje da sajida. Allah ya
bashi lafiya yasa kaffara ne"..
"Allahumma Amin, Bari na bude Miki dakin mutuniyar ki shiga na kawo Miki abinci
can, inaga sai dare zasu dawo tunda suka Kai har wannan lokacin".
Wanka ta shiga ta Dade a toilet din kafin ta fito tana tsane jikinta da towel,
lotion ta shafa ta dauko Rigar material marar nauyi ta saka a cikin kayan sajida.
Jallop din kuskus aka kawo Mata wadda Tasha kayan lambu da pepper soup na kayan
ciki da kunun aya Mai sanyi da ruwa.
Abincin taci ta koshi ta dora da kayan sanyi tayi hamdala ga Allah ta kishingida
jinta take fresh idan Allah ya kaimu safiya ta karawa motarta Mai, ganinta a araha
yasa ake garata kamar kwallo.AUREN HUCE HAUSHI.

MAMAN FATEEMAH

Page 42.
_______Abu kamar Wasa har kusan karfe taran dare ba zahra ba labarinta, iya Rahane
mommy ta Kira tana tambayarta kosu Rukayya sun dawo? Dan bazata fada ba direct tace
ana neman zahrar hakan dabara ce ta tambaya a fakaice.
Amsar data Bata ita ta Kara tadawa kowa hankali cewa tayi "Basu dawo ba tun fitar
safe da sukayi ga zulai ma duk ta shiga damuwa tace tun yamma Ammarta ke Kiran
wayar zilan tace wayar zahara'un Bata shiga".
"Yanzu ya za'ayi kenan?"
Rukayya ta tambaya.
"Ni damuwa ta Daya kada ta fada mugun hannu Dan ma dai ba lallai ansan matar waye
ba Amma yau abin tsoro ce kiransa zanyi kawai na fada Masa halin da ake ciki ko
yasan wasu 'yan uwansu a nan kanon, tunda barin Kashi a ciki baya maganin yunwa
gara ya fada kawai asan Yanda za'ayi tun guri be kure ba.
Number dinsa yayi ta try Amma amsar Daya ce a rufe take.
Da kyar ya mayar dasu mommy gida har Rukayya a gidansu ta sauka, to ta koma tacewa
baiwar Allah da sukazo tare zahrar ta Bata ko me?"
Duk wani lissafi ya gama suncewa Sameer, duk wannan Abu be tashi faruwa ba Saida
sukazo gidan kakarsa, ita kanta Hajiyar makwararin tashi Dan kukanta tana mitar
yarinyar Nan Bata kyauta Mata ba ta rasa a inda zatayi irin wannan shegantakar sai
a gidanta.
Jiki ba kwari Sameer ya shiga gidansa, sau Daya Fateeha ta kalleshi ta dauke Kai ta
cika fam da fushi tun safe Daya fice Bata Kara sakashi a idanunta ba, ta kirawo shi
ya Kai sau biyar sai dai yace Mata gashi Nan Amma bezo ba sai yanzu wurin Sha dayan
dare.
A kusa da ita ya zauna ta kauda Kai, hannu yasa ya dauki yaron a Kan cinyarta, yasa
hannu Daya ya tallabota ta hada da babyn ya rungumesu, Jin ajiyar zuciyar da yake
saukewa a jajjere yasa Fateeha ta gane da matsala.
"Wai menene?"
Ta fada cikin damuwa.
"Bari kawai wlh hankalina a tashe yake, tun bayan Azzahar Zahra ta fice daga gidan
Hajiyar makwarari bamu San inda ta nufa ba, duk inda muke tunanin zataje munje Bata
nan".
Itama mantawa tayi da fushin da takeyi dashi ta Fara sallallami "Yanzu Ina ta tafi?
Kadafa wani Abu ya sameta kasan mutane yanzu gaskiyar su kadan ce".
Dafe kansa da yake Sara Masa yayi "Bana tunanin haka gaskiya da Kanta ta fita ta
tafi kawai dai an Bata Mata Rai ne ban Kuma yi tunanin abin yayi Mata zafi haka ba
da bazan barta a gidan Hajiyar ba, amfani tayi da masu kawo lefen mujahida ana can
gurin karbar lefe ita Kuma ta fice daga gidan Dan akwai Wanda ya fada min Yanda ta
fito nasan da niyya ta fice abunta".
Zuru Fateeha tayi tana sauraren mijinta.
"Ka Kira ka fada masa?"
Kai ya girgiza Yana fadin na kasa samunsa nafi one hour Ina nemansa ban same shi
ba".

*** *** *** ***


Karfe Tara su Umman sajida suka shigo gidan lokacin Zahra na parlour suna hira
da Mama Hauwa, turus Maman tayi ganin zahra ko rantsuwa tayi Babu kaffara, wannan
ba zuwan arziki bane amma sai ta share tana fadin "wa nake gani haka?"
Dariya Zahra tayi tana fadin "Umman mu sannunku da hanya".
"Yauwa sannu,aike za'a yiwa sannu kin sha doguwar tafiya".
Shiru zahrar tayi batace komai ba, kannen Sajidar ne suka Fara gaisheta suna
fadin "Aunty kin rigamu zuwa munata cewa idan Ya Abba ze Kai Miki sakonki da Baffan
Rimi ya bada a Kai Miki zamu bishi sai gashi Kuma kinzo"
Karamar kanwarsu ta janyo tana fadin "ai zakuje ko mutuniyar tunda anyi min
Alkawarin zuwan".
"Eh zamuzo Aunty zahra".
Nusaiba ta fada suna Zama kusa da zahrar, yayin da Maman su ta wuce bedroom dinta
tana cike da tunani barkatai a zuciyar ta.
Tana shiga jakar hannunta ta zuge ta Ciro wayar ta, Ammah ta Kira Dan bazata Zama
uwar banza ba da alama gudowa yarinyar Nan tayi.
Lokacin da Kiran ya shigowa Ammah tana duba wasu kaya da Hajiya kaltume ta Aiko
Mata dasu ne.
Ganin Umman sajida ne yasa ta aje kayan ta dauki wayar tare da sallama.
"Wa'alaiki Salam warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu".
"Hajiya ya gida ya wajen Amare? Ina ta son na Kira mu gaisa Allah Bai nufa ba sai
yau, itama zahrar mun kwana biyu bamu gaisa ba".
"Wallahi kowa lafiya, Amare Kuma suna nan kusa daku Bata jin dadi ne mijin ya matsa
suzo Nan Kano a dubata ni tun safe da muka gaisa da wayar zilai ban Kara samunta
ba, na Kirawo zilan ma tace min har yanzu Basu dawo ba duk ta tada hankalin ta,
nace ita da ba ita kadai ta fita ba tare suke da amininsa da kanwarsa, Kinga duk
inda suke ai suna tare".
Shiru Maman tayi kenan hasashenta ya kusa Zama gaskiya Kenan.
"Hajiya ga zahrar a gidan nan,yanzu muka dawo daga Rimi Sai na tarar da ita Ina
ganinta nasan ba lafiya ba Ashe garin sukazo ta kawo min ziyara".
Jim Ammah tayi tana jinjina lamarin.
"Anya kuwa ki dai saka Mata Ido zuwa safe kome ke nan sai ki fada min idan anzo
daukarta to da sanin mijin tazo idan Kuma tace zata tafi ki hanata ki fada min na
gode kwarai Allah yayi Mana jagora ya Raya Mana zuri'a".
"Allahumma Amin". Sukayi sallama.
Zuciyar Ammah sai bugawa takeyi a hankali ta furta "meke Nan Kuma? Ni Asma'u
Allah ka taimaki 'yar marainiyar Allah, matsaloli daga an toshe wannan sai waccen
ta bulle Allah yayi Mana maganin wannan matsaloli yanzu kuma ko menene damuwar
datasa ta tsallake tabar inda suke gashi ta Kama wayar ta rufe Dan ma kada a San
inda take,ai kuwa zamu gauraya bazan dauki shashanci ba".
Ta hada duk kayan ta zuba a ledar da aka kawosu ta fice daga dakin ta nufi dakin
Abban Yara tunda ita keda girki.

Saida Umman sajida tayi wanka tayi sallah sannan ta fito har lokacin suna falon da
yaran direct dining ta nufa taci abinci sannan ta dawo falon.
Gaisheta zahra ta Karayi tana tambayar ya Mai jikin,
Dasu Baffa.
Sun dauki lokaci suna hira kafin Ummar tace "Wai daga Ina kikazo ne daga can Azaren
ne ko Kuma kinzo nan garin ne?"
Shiru zahrar tayi kafin tace "ganin likita nazo akan wannan ciwon marar da bakeyi
duk wata".
"Ikon Allah kuma ke kadai Kika taho ganin likitan kamar marar gata".
"A'a bani kadai nazo ba tare da Aunty Zilai Mai aikin Ammah mukazo tana can a
Nasarawa G.R.A".
"Ok, to mryasa baku taho tare ba Nan din".
Shiru tayi Bata ce komai ba, ganin da Yara yasa itama ummar tabar zancen.
Kafin kowa ya tashi Zahra ta tashi tana fadin "Umma Bari naje ba kwanta barci
nakeji"
"To Allah ya tashemu lafiya.
Basu Dade ba Suma suka shige daki Daman duk sun gaji.

Lokacin da Ammah ta shiga dakin Abban samun Mama tayi kane -kane tana ta zuba zance
da kudi a hannunta masu Dan yawa da gani a gurin Abban ta Karba, cikin alamun
rashin gaskiya mamar ta Fara fadin. "Aina leka parlourn ki naji Shiru nayi zaton
kina Nan wallahi Ashe Baki shigo ba"
Fuska ba annuri Ammah tace. "Eh ban shigo ba idan kin gama na dawo ta juya har
Takai kofar ficewa Abban yayi gyaran murya Yana fadin "dawo ki zauna Ina Kuma Zaki
ita ta tashi ta tafi tunda ta gama abinda ya kawo ta"
Jiki ba kwari Mama ta tashi tana fadin "ai Kam na Gama Allah ya tashemu lafiya
nagode Allah ya Kara arziki".
Ta nufi inda Ammah ke tsaye tana fadin "mu kwana lafiya ki tayani yiwa Abban yara
godiyar abin arzikin Daya bawa Najjahi na kudin registration".
"Masha Allah! An gode Allah ya bada sa'a".
Ta fada fuskar ta Babu walwala ko alama, da gaske ta kule Abun Yana so ya Zama
rainin hankali tayi noticing dinta duk ranar girkinta sai ta dunga Karakaina a part
din Abban Amma idan tasan wata ai Bata San wata ba.
Dawowa tayi ta zauna kusa dashi "meya Bata Miki Rai ne Kika juya Zaki bar dakin?"
"Ba komai".
Ta Bashi amsar in short.
Haka Nan yabar zancen badan ya gamsu da abinda ya fada ba.
"Neman izinika na shigo zanje Kano gobe in Sha Allah"..

Saida ya Kare Mata kallo tsab sannan yace. "me akeyi a kanon da zakije?"
Kai ta girgiza ba komai zanje barka ne na yaron nan Sameer ranar da yazo daukar su
Zahra yake fadawa magaji anyi Masa haihuwa an samu takwaran mijin Zahra".

"Kai Masha Allah, ai ban sani ba da nayi Masa barka ranar da yazo".
Tashi tayi zata fice Abban ya mayar da ita "Wai me yake faruwa ne Naga ranki a
bace tun shigowar ki".
"Ba komai zanje na dawo ne yanzu in Sha Allah".
Ta Mike ta nufi kifar ficewa, haka Nan yayi Shiru badan ya yarda da ba yasan da
abinda yake damunta taqi fada Masa ne kawai".
Ammah na shiga part dinta ta Kirawo Abdul Hakeem, lokacin Yana kofar masallaci tare
da Habib.
A parlour ya samu Ammar ta zuba tagumi.
Saida yayi sallama biyu sannan taji.
"Wa'alaika Salam".
Ta fada tana kallon Abdul Hakeem din, kusa da ita ya zauna Yana fadin "lafiya kuwa
Ammah Ina sallama bakya jina?"
Ajiyar zuciya ta sauke tana fadin "yanzu ba dadewa Umman Sajida ta kirani waiga
zahra taje Mata zata kwana a can Kuma ita kadai ba tare da zilai ba, na Kira zilan
tace min tun fitar safe Basu dawo ba har dazun, ka Kira Sameer kaji shin yasan da
tafiyar ko Kuma wani Abu ya faru tayi musu yqji nasan halin kayana zatayi abinda
yafi haka ma in dai zahra ce, Dan haka ka kwana da Shirin Kano sakko zamuyi ko
Abban KU ban fada Masa wannan maganar ba ina tsoron ta fito duk da nasan ba lallai
ta fito din ba amma sha'anin mace da miji sai Allah"
"Allah ya rufa asiri".
Abdul Hakeem ya fada Yana Kiran Sameer duk da lokacin ya ja Sha Daya ta gota.
Ringing Daya saneer ya daga kafin Abdul Hakeem ya Fara magana Sameer ya rigashi Dan
ko sallama Babu ya Fara fadin "Abdul Hakeem zahrar tazo Nan ne?.
"Easy my man! Tana Nan Kanon a Janbulu gidansu Sajida, yanzu Umman su sajidar ta
Kira Ammah ta fada Mata saboda hankalin ta be kwanta da ganin zahrar ba duka yaushe
akayi Abu da zata wani zo yawon ziyara tasan da wata a kasa, shine ta Kira zilai ta
fada Mata tun fitar safe baku dawo ba".
Ajiyar zuciya ya sauke, sai Yanzu ya samu nutsuwa dan Yanzu suka gama wayar da
mommy akan ko akwai wani cigaba? Yace Mata Babu Kuma tun lokacin da abun ya faru
yake ta kokarin ya Sami Mahmud Abun ya faskara.
"Na gode kwarai Abdul wallahi muna nan hankalin mu a tashe tun bayan Azzahar muke
Abu Daya, Dan Allah kayi min godiya gurin Ammah, kace Kuma tayi hakuri ba sai tazo
ba Dan Allah ga mommy ta Isa tayi komai ka fada Mata laifi akayi mata amma in Sha
Allah hakan baze Kara faruwa ba wannan ma tsautsayi ne".
Kai kawai Ammar ta gyadawa Abdul Hakeem ya gane me take nufi tunda handsfree ya
saka wayar".
"To ba damuwa tace ayi maka godiya da kwaramniya"
"Ba komai yiwa Kaine ka turo min da address din gidan Yanzu na gode".
Sukayi sallama ta kashe Kiran Yana Maida hankalinsa a Kan Ammah.
"Ammah lokaci yayi daya kamata a zauna da Mahmud asan who's he? Aure ba Abun Wasa
bane asan asalinsa Kinga muna tare sosai wallahi be taba fada min asalinsa ba kawai
dai nasan he's educated fiye da tunanin mu badai ya nunwa ne kawai anyway kome
Kenan dai kiyi abinda ya kamata kawai".
*** **** ***

Suna Gama waya Sameer ya lalubo Number Rukayya tana dauka yace ki fadawa mommy
gani Nan zamuje mu taho da Zahra tana janbulo gidansu friend dinta".
Bai jira tayi abinda zata fada ba ya katse Kiran ya saka jallabiya ya dauki key din
motar yayi waje.
A kofar parlour ya tarar da Rukayya da Mommy.
Fitowa yayi yana fadawa mommy Yanda sukayi da Abdul Hakeem da Ammah.
"Dan Allah ki zauna mommy muje da ya Sameer kawai ana ganin mu dake za'a San ba
lafiya ba Kinga ai itama zato takeyi kawai muce Mata ya Mahmud ne ya dawo yace muzo
mu taho da ita tinda da saura lokaci".
"To shigo mu tafi tsari mistress".
Saida suka dauki titin rijiyar zakin sannan Sameer ya mikawa Rukayya wayar da
address din da aka turo Yana fadin " duba ki gani ko kinsan laying kune masu yawo
lungu da sako na garin nan".
Dubawa tayi tana fadin " Nasan gurin layin gidan su saliha sani Musa ne tare
mukayi Excel da ita".
Cikin ikon Allah suna tsayawa a kofar gate din motar ya Abba ta shigo shida Abie
dinsu sun dawo daga kwangwalam bodar NIGER inda sukaje gaisuwar mahaifar amininsa
data rasu jiya, sun biya ta kazaure gurin wani abokin aikinsa daya kwanta a Asibiti
Shima a Nan sukayi dare.
Ganin mota a kofar gidan yasa Abie yace Abba ya tsaya yaje yaji ko lafiya Yana fita
Mai gadi ma ya fito Yana ganin Abba ya karasa gurin da sauri, fitowa Sameer yayi ya
tarbesu Yana Mika musu hannu sukayi musabaha Yana fadin "Ayi hakuri munzo cikin
dare ba sanarwa,Daman munzo mu tafi da zahra ne tun Rana tazo Bata Fadi zata kwana
ba sai Yanzu mijinta ya dawo gashi ba waya a hannunta, ganin da sauran daren yasa
muka biyo samunta".
,"Ok. Ba damuwa muma Yanzu shigowar kenan munje unguwa tare muke da Abie".
"To mu karasa Mana na gaishe shi ya juya yabi bayansu suka nufi gurin Abie din,
Rukayya gani tayi kamar akwai rashin kyautawa ace tana kallo aje a gaishe da babban
mutum tana zaune sai kawai ta fito ta rufa musu baya.
Cikin girmamawa Sameer ya gaishe da Abie din sai Jin muryar Rukayya sukayi daga
baya tana gaishe da Abie din, hankalin Ya Abba biyu ya kasu ga wata murya data
fizgeshi lokaci Daya ga Kuma bayanin da yake yiwa Abie.
""Ba wani Abu Bari a Kirawo Umman tasu saita fada Mata ta fito wannan ai shashanci
ne ya za'a bar yarinya ta nemi gurin kwana da mijinta da komai".
Sameer ne ya Dan shafa Kai.
"Ayi hakuri Abie mijin ne baya Nan sai yanzu ba dadewa ya shigo kasar".
Mazaunin direba Abban ya koma suka nufi ciki tunda Daman Mai gadi ya bude gate Yana
jiran su shigo.
A waya Abie ya Kira Umma har lokacin idanunta biyu da wuya tayi barci matukar tasan
mijinta baya Nan da sauri ta dauki wayar tana Masa sannu da zuwa.
"Yauwa ya amsa a takaice Yana fadin. "ki taso bakuwar da kikayi a gidan mijinta ya
dawo gasu Nan a gate". Ya kashe Yana nufar part dinsa.
Shiru tayi waye ya fada masa da bakuwar a gidan jiki ba kwari ta nufi dakin sajida,
barci ta Samu tanayi sadidan kamar Nan duniya Bata da damuwa Kota sisi dakin ta
shigo tazo bakin gadon ta tsaya tana Kiran sunan ta a hankali, tana fadin "tashi
ki kimtsa ki fito ga Mai gidanki can zaku tafi gida". Idanun tadan zaro tana fadin
"wallahi bazani ba Umma kice musu bana nan
sai hawaye"..

AUREN HUCE HAUSHI.

MAMAN FATEEMAH.
Page 43.
_______ kuka zahra keyi ba kakkautawa a hankali Umman ta zauna kusa da ita, ki
daina kukan Nan kiyi hakuri ki tashi ku tafi, kiyi ta addu'a Allah ya kawo Miki
saukin ko menene damuwar, kada ki Kara tunanin yin irin haka idan Abu ya dameki ki
tafi kibar gida ba shine maslaha ba kinji, tashi ki cire Rigar barcin ki canza suna
jiranki Kinga dare ya farayi inaga tun Rana suke bulayin nemanki sai Yanzu suka
samu inda kike".
Kai ta gyada tana goge hawayenta, Bata taba tunanin yau zata koma gidan Nan ba Dan
ita a budget dinta daga Nan gaba zatayi Dan kasar tayi niyyar tsallakewa tayi gaba
abunta tunda passport dinta yana jaka, to Wai ta Yaya suka gano tana gidan Nan Wama
yasan gidan a cikinsu, to shi yaushe ya dawo?
Haka zuciyarta ta dunga sake-sake.
Fita Umma tayi ta Bata guri ta canza Kayan, jiki a mace ta fito ta iske Umma da Ya
Abba a parlourn, gaishe da Ya Abban tayi ya amsa Yana fadin "wallahi kin wahalar da
mutane da wannan Daren Kika sakasu fitowa har da mace Ina jinma mijinta ne"
.ita dai zahra Shiru tayi Masa ta nufi Hanyar fita daga parlourn tana fadin "ummah
na tafi Saida safe".
Ta fada tana yin gaba "to Allah ya tashemu lafiya kiyi hakuri da safe idan Allah ya
kaimu ki bude wayar zamuyi magana".
"To Ummah in Sha Allah Zan bude". Suka fice daga Fallon. Ya Abban Yana biye da ita
tun kafin ta karaso Rukayya ta taho cikin sassarfa ta ringume Zahra tana fadin
"wallahi kin dauki alhakina da Hajiyar makwarari Kinga kukan da muka Sha yau?
Tambayi Ya Sameer kiji duk kin tashi hankalin mu".
Wani sanyi ya ratsa Ya Abban Jin Rukayya ta ambaci Sameer da yayanta, daman Kuma
yaga Kama ta zahiri duk da dare ne Bai Hana shi ganin kamannin nasu ba.
Shiru zahrar tayi Mata ita sai Yanzu taji wata kunya duk ta rufeta, me kenan tayi?
Shike Nan zasu dauka fa tayi yaji ne dole ta magantu.
"Wai Dan Allah Aunty Rukayya ku kasa barina nayi kwana ko Daya ne a gurin Ummata
nifa bada wata manufa ba na taho kawai dai nasan idan nace zanzo ba Bari Oga sameer
zeyi ba zece saina nemi izinin....."
Sai tayi Shiru.
"Izinin wa za'ace ki nema?".
Gaba tayi kawai ta nufi gurin da Sameer yake tsaye jikin kofar driver, da wannan
damar Ya Abba yayi amfani ya matso kusa da Rukayya yana fadin "Ashe Aunty tasha
kuka zanso Naga kina matse hawaye".
Kallonsa tayi haka nan taji yayi Mata kwarjini.
'yar dariya tayi tana fadin "Ina yini?"
"Lafiya kalau beauty, ki saka min number ki Zan kira naji ya kukaje gida tunda
sister Zahra har wayar tayiwa tawaye".
Ya karasa Yana murmushi itama murmusawar tayi tana karbar wayar, number ta saka
Masa ta Mika Masa wayar tana fadin "bari na wuce ya Sameer Yana jirana"
Tayi gaba.
"Ok saina kira shima gurin Sameer din ya nufa sukayi sallama, ya leka ta window
Yana yiwa Zahra magana.
Tunda suka dauki hanya ba Wanda ya Kara magana sai ajiyar zuciyar Zahra ke sauka
kadan- kadan.
A hankali zahra ta bude Baki tace "Dan Allah oga sameer kayi hakuri na Bata maka
Rai bada niyya nayi ba kawai dai Ina son Naga Ummah ne Naga kuma kamar bazaka yarda
naje na kwana ba".
"Ba komai kawai, Daman Yanda su mommy suka tada hankalin su ne ya daga min hankali
nasan ba Bata zakiyi ba tunda da kafarki Kika fice".
Shiru tayi tasan magana ce ya fada Mata a kaikaice, tasan a kule yake da ita kawai
dai Batasan dalilin Daya hana yayi Mata buyaji ba, Dan taga alama ya iya tijara
Yanda ya karewa Rukayya dazu ko shi yasa taja bakinta tayi shiru Yanzu.
Sha biyu da minti goma yayiwa Mai gadin gidan horn Saida ya leko shima Sameer din
ya fito Yana ko waye sannan ya bude.
Yana shiga da motar Maimakon yaje kofar main parlourn sai taga yabi ta baya ya nufi
wani gani Mai azabar kyau ko Ina tar kamar dauko ginin akayi aka aje ga wata 'yar
baranda data hade ginin biyu an saka glass anyi kamar katanga da wasu irin flowers
masu kyau a jere ana ganinsu gurin yayi matukar kyau da burgewa a kusa da steps din
da ze sadaka da
Main parlour, Zahra ba tayi kokarin bude side din da take zaune ba, dan juyowa
Sameer yayi "Dan Allah kada maganar nan ta fita kawai da safe ki fada musu mun Dade
a Asibitin ne yasa Kika bamu dawo da wuri ba sun kulle, kiyi using da Nan kawai ki
barsu su a can, Rukayya zata kawo Miki kayanki da safe kiyi idan Allah ya kaimu".
"To nagode".
Abinda ta iya fada kenan, ta bude ta fita Rukayya man ta fito tana fadin "
Bismillah kizo muje na rakaki".
Tare suka jera suka hau zuwa kofar, ita Kanta kofar abin kallo ce ita Yanzu zahra
abin har ya daina Bata mamaki so take taga iya gudun ruwan bayin Allah nan Kullum
lamarin su ba baya yake ba gaba yakeyi daga Nan sai can suna shiga ta Kara jinjina
girman lamarin Wai shi wannan abokin nasu wane irin kusancin ne a tsakanin su da
za'a dunga sauke ta a duk inda akayi ra'ayi. Wannan part din yafi wancan komai
parlour sun Kai hudu, a cikin parlour na uku ne suka taka steps ya Kai shida sannan
suka shige want korido ko Ina tadal sai wani special kamshi ke tashi bedrooms ne
guda biyu a jere, Rukayyar ce ta Dan juyo tana murmushi "to madam gasu Nan saiki
shiga Wanda kike so ki kwanta, tunda kin samu muna yawon dare kamar marasa gaskiya,
Zan Baki shawara sai kin Zama jaruma fa a gidanki Dan Ya Mahmud wallahi Mata
rubibinsa suke, idan kikace Abu kadan Zaki fece kece ki tafi kece a kwana Dan idan
yayi wata tafiyar sai ki kwana hamsin Baki saka shi a idonki ba, pls you have to be
very strong gaskiya kada ki yarda a gano Ina kike da lapse akwai damuwa kwarai ki
rike mijinki da kyau ki mutunta shi ki girmama iyayensa zakiji dadin Zama dashi in
Sha Allah, zabi na rakaki dakin na wuce barci Kuma nakeji tunda Allah yayi Mana
gyadar dogo ya rabamu da kwanan zaune to matar big bro ta Bata Ina Ni Ina barci ai
sai kwana sallah".
Ta fada tana 'yar dariya.
"Ki sakani kowanne Wanda za'a sanwa ya taba cewa way gutsiri nan? Duka zaman na yau
zuwa gobe ne Dan gida zamu koma bana son wani surgery a Nan idan ma yimin din
za'ayi ba wannan Mai fuska kamar Jan karas din zatayi min ba muma muna da qualified
a can Dan dai kada nayi musu dashi ne kawai".
"Kinga mu Shiga na koma dare Karayi yakeyi gara naje na kishingida".
Dakin da yake facing dinsu ta bude MashaAllah" ta fada Tana karewa dakin kallo
sannan ta juyo tana fadin mu kwana lafiya"

Kallonta Zahra keyi tana son tayi Mata tambaya Amma ta rasa ta Ina zata Fara, Dan
Yanda tasan gudan Nan da Yanda take fadar wasu abubuwan akan Mahmud ga Kuma abinda
Hajiya kakarsu ta fada Mata dazu maganganun suna kamanceceniya da juna amma Bari ta
Adana tambayoyinta da sauran lokaci.
"Nagode Aunty sai da safe, Amma fa Ina Jin tsoron gurin nan fiye da can din
wallahi, Kinga Nan ba kowa. Allah mu kwana tare ko kin tafi bazan iya barci ba".
Dan Jim tayi tana tunani ita Kanta Bata San dalilin Ya sameer na kawota Nan ba,
amma tasan dole da dalilinsa nayin hakan.
"Ok ba damuwa Bari naje na dauko sleeping dress Dina da naki saina dawo"
"Ok, yauwa Aunty ki taho min da phone Dina tana cikin bedside".
Ta nufi Hanyar fita, wayarta ce ta dauki ringing number ce tasan Wanda ya Karba ne
dazu a ta daga da sallama suka Kara gaisawa ya tambaye ta ya suka zo gida ta fada
masa lafiya kalau sukayi sallama ta fice.
Kofar ta rufe ta farko tayi gaba tana fadin "kamar wata Rukayyar mahaukata na shigo
wannan part din na kwanta a can ma naki kwana ballentana a Nan yarinya Allah ya
kawo mijinki ki tarairayi kayanki kuna gefe Naga alama sai nayi Mata budedden
karatu sannan zata gane mace har Mace ta fita kunya Amma ki tsaya kina Wasa da
damarki".
Ta wannan barandar Mai glass ta Shiga Daya part din da yake tasan wanancin lambobin
kofofin tunda duk sati suke zuwa da sauran yaran gidansu suna gyara bedrooms din
kawai sauran Kuma da masu aikin da sukeyi dakunan kwanan ne dai Batasan dalili ba
masu aiki basa shiga.
Ko Ina tsit a gidan baka Jin komai sai kukan kananun kwari da dai daikun tsuntsaye
ta gefen inda zahrar ta kwana ta wuce da gaske ko ita data Saba da Shiga gidan wani
lokacin tsoron Yana kamata bare a irin Nan da sauri ta shige parlourn na uku ta
wuce corridor da za sadata da dakunan.
Tana bude dakin zilai ta bude ta fito tana fadin "sannunku da dawowa, Dan Allah
lafiya kuwa tun rana sai Yanzu sha biyu ta wuce?'.
"Lah ba wani damuwa munje unguwa ne motar ta samu matsala sai dazu muka shigo garin
muka biya gidan mommy a can muka Shantake Sai Yanzu ya Sameer ya kawo mu".
Wani sanyi zilai taji a ranta, "to ai shikenan Allah huta gajiya da ko barci na
kasayi ina ta tunani barkatai".
"Kai haba ba komai Allah ya tashe mu lafiya ta bude kofar ta shige itama Zilan ta
Koma ciki.

Tun bayan fitar Rukayya zahra ta dosana gefen ta zauna ta zabga uban tagumi, da
sauri tashi ta fito ta dauko handbag dinta ta biyo Hanyar da suka shigo kofar fitar
ta murda tajita bam ko motsi batayi, tayi tayi taji kamar tana taba dutse, hakuri
tayi ta juya sai lokacin tsoron ya rufeta da gudu ta shige dakin tana turo kofar,
dube-duben makulli kofar ta Farayi ita dai bataga gurin wani key ba har zata hakura
taga wasu numbers a jikin wani Abu kamar switch din kunna wuta numbers din ta Danna
Yanda suke a jere taba taba ta karshe taji want Dan sound daga jikin kofar handle
din ta Kama zata bude taji ta rufe gam, sai lokacin ta Dan samu peace of mind, ta
nufi gadon ta aje jakar a gefe ta nufi toilet dole saita sake gyara jikinta. Tana
Shiga ta cire rogar material din sajida data sako ta taho da ita ruwan zafi ta hada
tayi wanka ta fito da towel a jikinta sanin ba wasu kayan sakawa a Nan yasa ta Haye
gadon daga ita sai towel ta rage hasken dakin ta janyo lallausan bargo ta rufe
jikinta sai fuskar kawai ta Bari a hankali ta Fara Addu'oin kwanciya barci, kafin
ta Gama barcin yayi awon gaba da ita.

Karfe Daya da rabi daidai jirgin Max air ya sauka da duban jama'a daga kasahe daban
daban na duniya, cikinsu harda Muhmud Muhammad Dange, a hankali yake tako stairs
din jirgin sanye yake da kananun Kaya Ash T- shirt da black jeans a jikinsa sai
jakar laptop dinsa a kafadarsa.
Yana karasa saukowa wani matashi fari marar jiki ya nufe shi Yana fadin "barka da
sauka yallabai, ga key din motar Nan a hannunta oga yace na kaika gida, sai
Balarabe ya bimu da wata motar sai mu dawo tare dashi".
Hannu ya mikawa Mai bayanin Yana fadin "bani key din kawai kace masa na gode kwarai
da kulawasa, zanyi driving da kaina".
Mika masa Yana fadin "Allah ya tashemu lafiya kayi min godiya sosai ya Ciro kudin
America ya mika Masa sannan ya bar gurin.
Lokacin Daya fito daga airport din Daya da minti ashirin da bakwai, tuki yake cikin
nutsuwa sau biyu kawai ma'aikata suka tsayar dashi, har yazo gate din gidan ba
Wanda ya Kara tsayar dashi, sau Daya yayi Horn Mai gadin ya falfalo da gudu yana
leken waye a Nan baisan motar ba Dan haka ya koma ya dauko abinda ze Bashi kariya.
Kafin ya bude ya fito, Mahmud ya fito ya harde hannusa a kirjinsa ai Mai gadin Yana
ganinsa yayi sauri ya koma da gudu Yana Fadin "barka da sauka fari Mai farar Aniya
Allah ya Kare gabanka da bayanka baya Mai goya marayu"
Dan murmusawar Mahmud yayi Yana fadin "wani Abu sai Malam Musa shi Babu ruwansa da
dare". Ya fada Yana kunna Kai harabar gidan wadda take kamar rana, mutane hudu ne
suka bullo daga mabambantan gurare. Parking lot suka nufa sun San Mai gidan ne
tunda suka jiyo hargagin Malam Musa. Shima da gudu ya karaso gurinsa Yana cigaba da
Yi Masa kirari.
Sun gaisa sosai dasu har kusan minti biyar sannan yayi musu sallama Saida safe ya
nufi babban part din, Murtala ne yayi sauri ya sameshi "yallabai Ina ganin madam
din kamar tana can sabon gurin can Dan Nan Naga Sameer ya ajesu dazu ita da Rukayya
kanwarsa, can ya nufa Yana mamakin me yasa Sameer ya kaita can alhalin yace a barta
a tsohon part din.

AUREN HUCE HAUSHI.


MAMAN FATEEMAH.

Page 44

_________ kamshinta ya Faraji Yana shigowa parlourn, wani limshe idanu yayi Yana
ayyana abubuwa da yawa a ransa, direct ya wuce bangaren bedrooms din Yana jinsa
cikin nishadi, wato Sameer Yana expecting dinsa ne a kasar shi yasa ya bude Mata
nan kenan, a hankali ya taba handle din kofar farko ya jita a bude Shiga yayi komai
tsab, iska ya huro daga Bakinsa ya aje jakar laptop dinsa a Kan sofa da take dakin,
ya zauna a gefe Yana cire takalman kafarsa, wanka yake son ya Fara kafin ya Shiga
gurin waccen danger girl din "yar yarinya ta Hana shi sakat duk ta birkita Masa
Lissafi" ya fada a fili Yana rage kayan jikinsa.
Wanka ya shiga bai wani dauki dogon lokaci ba ya fito saboda dare ya Fara nisa ga
gajiyar zaman guri daya, pyjamas ya saka masu kalar sky-blue ya fesa turarensa ya
dauki wayoyinsa ya fice daga dakin ya nufi dakin da zahrar take, wani Abu ya taba
mai Kama da socket din electric na kunna wuta sai kofar ta bude,a hankali ya shige
Yana Jin kamshinta yanda ya cika dakin, shi dai yawanci duk matan da suka zamar
Masa dolensa suna bala'in son kamshi, yana ida shigowa kofar ta rufe Kanta Wai Abu
ya taba ba Wanda zahra ta taba ba, yayi gaba Yana nufar gadon inda ya hangeta ta
kudundune cikin bargo, da gani a tsorace tayi barcin, wayoyinsa ya aje a Kan bed
side ya zauna a gefen gadon Yana Kare Mata kallo, shifa duk hankalinsa ba a kwance
yake ba tunda aka fada masa matsalar dake damunta yaji ba shida sauran nutsuwa idan
ba zuwa yayi ya ganta ba, Kuma Dole ma yasan abinyi akan ciwon Nan ko ana Wasa da
wasu lamuran Banda lafiya baik'i tasan kowaye shiha a wannan lokacin dole ya
dauketa ya kaita inda za'a dubata Masa ita duba na gaske.
Remote din AC ya dauka ya rage gudunta dakin yayi sanyi da yawa duk da Yana son
sanyi amma wannan yayi yawa, a hankali ya saka hannu ya janye bargon daga fuskar ta
barcinta takeyi shower cap din dake Kanta ta cire sai gashi Baki sidik Yana ta
walqiya a cikin Dan hasken data Bari a dakin, Kara zame rufar yayi har zuwa
kirjinta jikin sai wani glowing yakeyi Jin sanyi Yana shigarta yasa ya juyo da
fuskar ta inda yake zaune "ya Salam". Ya fad'a a hankali, gani yayi ta Kara yi Masa
wani kyau na musamman, Kare mata kallo yayi yaga daga ita sai towel a jikinta,
murmushi yayi da gani Batasan da Kaya a dakin ba.
Kayan jikinsa ya cire ya Zama daga shi sai boxer short ya shige jikinta ya janyo
lallausan bargon ya rufesu Yana sauke ajiyar zuciya, a cikin barci taji an
rungumeta gaba dayanta jikinta ne ya dauki rawa shikenan tasan tata ta Kare shi
yasa suka nemota da tsohon dare suka kawota Nan Yan ko wane irin ihu zatayi ba Mai
jinta, cikin murya Mai rauni tana cracking ta Fara farin "innalilllahi na Shiga
uku wayyo Allah na....
Bata katasa fadin abinda tayi niyyar fada ba taji yace "shittt...Ni ne fa cool
down precious ba abinda ze sameki a cikin gidan Nan sai ikon Allah, akwai
kyakykyawan tsaro".
sansanyan kamshin turarensa ne ya shiga hancinta, kokarin kwace jikinta takeyi
Dan yayi Mata kane-kane so take taga zahirinsa Amma ya Hana hakan, ita mamakinta
Daya yaushe yazo garin kuma ta Ina ya shigo Dan ita dai tasan ta rufe kofar nan.
Dai dai kunnenta ya saka Bakinsa "ki kwanta muyi barci na gaji da yawa kin hana
duniyata kwanciyar hankali kina min kisan mummuqe ko wayar ma kin haramta Mana
yinta, tunda Naga alama Nima Mai laifi ne". Ya fada yana shafa gashin kanta zuwa
bayanta, hannu Daya yasa Yana zare towel din data daura a jikinta da sauri ta rike
tana girgiza Masa Kai.
"Dan Allah ka Bari bafa kyau muyi barcin to".
Wani guri ya taba a jikin gadon wasu irin fitilu suka Kama kamar star masu haske
sosai, Bata ankara ba ya fizge towel din gaba Daya daga jikinta Yana Mata wani
mayen kallo hannu tasa ta kare kirjinta cikin matsananciyar kunya tace Masa "Dan
Allah ka kashe hasken Nan wallahi kunyarka nakeji".
"Ni kike Jin kunya?"
Kai ta gyada Masa, 'Well done Yanzu kuwa Zan cire kunyar nan daga idonki".
Wani bed sheet data gani a gefen gadon ta janyo da sauri ta lullube jikinta dashi
tana Kara sadda Kai kasa Dan da gaske ya saka taji kunya sosai.
Wutar ya kashe ya matso sai Jin mutum tayi ya shigo cikin Bedsheet din data rufa
dashi ya hanye shi ya maye gurbinsa da lallausan bargon.
"Ki hanani Zama a gurin neman abincina sannan na dawo ki Kama guduna, ai impossible
wallahi muyi barcin da safe mayi bayanin".
Ya Kara mannata a jikinsa suka samu body contact da kusancin zahiri.
Sun jima yana sarrafata.Tayi laushi iya laushi dan da gaske da kishirwarta ya shigo
garin tamkar mayunwacin Zaki badan tana cikin rashin tsarki ba da Babu abinda ze
Hana labarin sauya salo, dan tuni ya wani manta da Alkawarin da ya daukarwa Kansa,
Saida tafiya tayi nisa ya ji abinda yayi Masa cikas Dole ya saurara Mata, sun kai
kusan karfe uku da rabi a haka shi Mai fad'ar barci ya keji sai gashi ya bige da
Hana Mai barcin yin Bata barcin.
Sai sauke ajiyar zuciya suke su duka har lokacin hannunsa Bai daina shafe shafe ba,
wani irin yanayi jikinta keyi har mararta ciwo ta Dan Fara Mata cikin dashashshiyar
murya mai dauke da salon shagwabar da Batasan iya ba,ta kankame Shi jikinta na
wata irin tsuma muryarta ta dishe tamkar me yin mura ta Fara magana.
"Dan Allah ka bari wallahi marata ciwo takeyi...".
Baiyi magana ba sai kakkameta da yayi kamar ze shige jikinta shima ya hade bakinsu
Yanda ba Yanda za'ayi ta iya furta wata maganar ba, hannunsa ya tura Yana shafar
marar ji yayi tadan tasa kamar ta Dan kumboro, hannun ta rike tana girgiza Masa
Kai.
Zare hannun yayi ya dawo dashi sama yaci gaba da sabgarsa ya Kuma ki sakin bakin da
zatayi korafin, suna haka har wayarsa ta Fara rera kiran sallah.
A hankali cikin muguwar kasala ya saki bakinta yana Maida numfashi da sauri da
sauri gefe ya margina Yana dafe da tasa marar idanunsa a rufe, Zahra naji ya raba
jikinsu ta Kara takurewa a cikin bargon wani irin tsoro ne ya lullube ta da gaske
yazo Mata da wani lamari Mai girma, ita ai ko idanu bazata yarda su hada ba ai da
kunya wallahi duk yabi ya tsorata tas ya lalube ko Ina na jikinta, Ashe can baya
Wasa ne kawai yayi Mata yanzu ne ya nuna Mata true colour dinsa tana ganinsa salihi
Dan bawan Allah Ashe shima guda ne ba gyale ba, kirjinta sai zogi da ciwo sukeyi
mata yayi son ransa da jikinta.
Tana jinsa ya tashi ya shige toilet ya jima tana jiyo motsinsa, sannan taji ya fito
alamun tsayuwarsa taji a Kanta,a hankali ya saka hannu ya janye bargon kankame
jikinta tayi Dan daga ita sai pant Kare Mata kallo yakeyi take yaji alwalarsa na
neman warwarewa, laimar hannunsa ya Dan yarfa Mata a jikinta "wash...Allah na!".
Mayar Mata bargon yayi ya shige clothset din dakin jallabiya ya sako Fara tas da
hula mahadinta raka'atanul fajri yayi, jikin gadon ya matso ya Dan zauna "zanje
masallaci".
A dawo lafiya tayi Masa tana kudundune Yanda take, tanaji ya fice daga dakin.
Sai ta tabbata ya Kai masallacin sannan ta yunkura ta tashi ta nufi toilet,
tsabtace jikinta tayi sannan tayi wanka ta fito,lotion din data gani ta shafa sai
body mist na itacen sandal wood Dana oud ta hada ta fesa kayan da zata saka ne ya
zama cikas Dan bazata iya mayar da Wanda ta cire ba Kuma bazata Kuma Zama da towel
ba tunda taga abinda hakan ya janyo Mata, Shawarar duba clothset din tayi idan taga
Kaya sabo Kona waye zata saka, tana mamakin ace Mai gidan Nan bashi da Mata Kuma ya
sakarwa abokai irin haka baya gudun a ring aikata fasadi a cikinsa, were Dan wannan
sai ka shekara a ciki ba'asan kana nan ba.
Ba karamin mamaki tayi ba ganin kayan Mata masu yawa har Sunfi na wancen apartment
din ba wani d'ar undies ta saka ta saka doguwar Rigar material Bata daura Dan
kwalinba wasu hulina na Mata ta gani da yawa ta duba kalar ash irin flowers din
jikin material din ta saka a Kanta, barci takeji sosai Dan tunda Allah yasa ya
tasheta da aalonsa Bata Kara rintsawa ba shiko gogan Allah besa an raba barcin jiya
dashi ba.
Harta juyo zata bar gurin taji tana son ta bude dayan side din, kayan make up ne
dasu turarika shoe and bags turaren ta dauka tana dubawa duk yawanci irin nata ne
sai wasu irin nasa ga Kuma kayan maza nan Lodi Lodi dasu underwears tana tsayen
tana dubawa taji kawai an rungumota ta baya, ajiyar zuciya ta sauke tana lumshe ido
Sam bataji alamun bude kofa ba ko takun tafiyarsa, Kansa ya Dora a kafadarta Yana
Dan hura Mata iskar Bakinsa a kunne "Good morning my previous".
"Morning Yayana".
Ta fada da wani salo, juyo da ita yayi suna facing din juna.
"Bude idonki ki kalleni ki fada min waye yayan naki? Wato har yanzu da sauran Rina
a kaba kenan ko? Nifa bazaki tauyeni ba Ni ba wani Yayanki bane a bani special
name Dina, kodan kinga mu 'yan gargajiya ne "ya'yan Alarammomi Malam soro, bamu da
wayewa irin taku ko?"
Batasan lokacin data sauke ifanunta a Kan nasa ba, tana jinjina maganarsa.
"Wayewar saita kasheku".
Tayi subul da baka ta fada harga Allah a zuciyar ta tayi niyyar fada bakinta ya
subuce ya fada.
"Kai! Nine wayewar saita kashemu to nida waye zata kashe din?"
Kauda Kai tayi tana Jin kunyar maganar.
*Ni ba haka nake son fada ba Bakina ne ya furta hakan".
*Ok, zomu kwanta barci nakeji tunda kin hanani barci da fitinarki".
Rigar ya zuge zif din ya cire mata ita ya barta daga ita sai undies kawai ya
dauketa can ya nufi bed din da ita tana mutsulmutsultun ya sauketa ya kiya Saida ya
dangana ta da saman bed din, shima jallabiyar ya zare ya janyota ya lullubesu da
gaske barcin za'ayi Dan tunda ya sakata a jikinsa Bai Kara yi Mata komai ba.

*** *** ***

Tunda Ammi tayi sallah Bata Koma barci lazimi ta zauna tana yi amma zuciyar ta Babu
dadi kwanan nan kusan Kullum sai tayi mafarkin Mahmud da wata yarinya budurwa Yana
rike da ita da hannu Daya dayan Kuma Yana ta faman fada da wasu irin halittu mara
kyawun gani, to yau ma shita Karayi Saida taga wasu mutane dattijai guda biyu sunzo
sun Taya Shi kashe wadannan halittun sun tasa su shida yarinyar har wani gida sai
da suka shige sannan suka juyo suka tafi.
A haka Mai gidan ya sameta Saida ya zauna ya Kare Mata kallo yasan da akwai damuwa
a tare da ita sai dai tana kokarin biyewa.
"Ammin Yara me yake damunki duk kwanakin Nan Baki da walwala Sam ko kula dani ma
tayi baya ko Baki huce bane har yanzu?".
Kai ta girgiza "A'a kawai dai lamari Hussain ne yake damuna kofa da Rana Daya Bai
taba kirana ba ko sako ta email Bai taba Yi min ba, gashi a kwanakin nan sai wasu
irin mafarkai nakeyi dashi marasa dadi abinda yafi tsaya min a Rai Kullum da wata
yarinya budurwa kamar 'yar India nake ganinsa da ita Ina tsoron wani Abu wallahi na
rasa yanda zanyi Dan Allah kayi wani Abu akai".
Sai hawaye sharrrr.
"Subahaballahi! Haba zainab ya Zaki ringa yi Masa kuka kinsan masifar zubarwa da
d'a hawaye kuwa ko wani abun yake aikatawa ai saiya karu idan kina Masa kuka,
addu'a zamuci gaba da Yi Masa nifa jikina Yana bani Yana Dubai Dan last week na
samu leakage akan Yana can din Dan yayi wasu ziyarorin bazata a can harya dakatar
da wasu ma'aikatansa sai dai duk kokarin a gano min masaukinsa sabo hakan yaci tura
Dan ba'a inda yake sauka ya sauka ba tunda gudun hijira yayi".
Hawayen ta goge ta tashi tana ninke sallayar ta zauna kusa dashi. "Shikenan Allah
ya shiga cikin lamarin ya kureshi daga sharrin zinace zinacen zamani wallahi badan
komai nufin Allah bane Wanda yaso yake bawa kyautarsa danace dama bashi ya samu
wannan budin ba da kananun shekaru to yanda yaso haka yake tsara kayansa, Amma ga
yayunsa Nan ba Wanda ya takura musu Suma ai suna da wadatar,tunda Allah yayi muku
karfin arziki waye talaka a cikin family din nan?".
Dan murmushi general yayi Yana kallon yanda take fadin magana abinda ba halinta ba
inda akan twins ne sai dai wani yayi magana Amma ta zage tana fadin son ranta.
"To ya zamuyi da hukuncin Allah shi yaso ya daukaka a cikin zuri'ar da Wanda ya Isa
yace a'a Ina cewa Alhaji Ishaq ne ya bashi jarin Daya Fara sana'a dasu tun Yana
hannun Hajja, Amma yanzu zaki hada arzikinsu ko kusa ko alama Babu Hadi,.koni Dana
haifeshi ya mallaki abinda bani da kwatqnkwacinsa, Keda Kika haifeshi kin mallaki
abinda yake dashi? To kiyi istigifari ga Allah tunda shine yace Yana azurta Wanda
yaso ba tare da hisabi ba,ai kin gane?".
"Na gane Allah ya Zama gatansa a duk inda yake,Amma fa yarinyar Nan ta tsaya min a
rai idan Yana kusa da wannan ai zai manta da kowa ne tunda cikin bacin rai yabar
gida ga Kuma kudi a tare dashi kaga sai Allah kadai ze kare shi".
Dariya ta bashi sai da yayi sosai kafin yace.
*In Sha Allah in dai Zina gado ce to Alfarmar Manzon Allah s.a.w.w zuri'ar mu
bazasuyi ba Ni ba mazunaci bane haka kema ba ita bace in Sha Allah.Allah baze
jarabcemu da ita ba, Kika sani ko bushara ake Miki ke uwa kin samu sirika".
"Haba dai har abun ya Kai haka yayi aure ba sanin iyayensa ai kuwa da lamarin ya
lalace".
'yar dariya yayi.
"Kedai kije ki shirya min breakfast daurin Aure zamuje kabba na Dan gidan sanata
Abdul Aziz"

"Ok.bari na shiga kitchen din"


Ta tashi ta fice tana baza kamshinta as usual.

******

Tun idar da sallar Rukayya ta taso ta nufo part din da zahra ta kwana,abin mamaki
an canza pin kofar dan ta kwada yafi sau goma Amma taki budewa. Nan da Nan taji
hankalin ta ya tashi me Kenan badai wani bane ya shigewa 'yar mutane ba gashi jiya
Taki Kai Mata wayarta da ba saita kirata ba, gudun kada tace sai sun kwana ya hata
ta Kai mata.
Number ya Sameer ta lalubo lokacin Yana barci,
Yana dauka ko gaishe shi bata tsaya yi ba ta Fara fadin "Ya Sameer ka taimakeni
wallahi tun sassafe bake kokarin shiga part din da zahra take Amma kofar kofar
kamar an canza pin din na saka yafi sau goma Amma yaki budewa".
Tsaki yayi "Waike Dan Allah Ruky yaushe Zaki girma ne? to oga ne ya shigo cikin
dare Nima da asuba naga text message dinsa Dan haka ki Zama ready idan na shigo
saimu wuce tare Amma yanzu kada kuyi komai za'a kawo abinci".
"To ai su Iya Rahane har sun kusa gamawa baka fada min ba tun dazu".
Ok, ba komai sai a hada tunda gidan da jama'a, yauwa zuwa an Jima ki bude musu part
din Nan na kusa da parking lot sai su zauna a nan tunda shima ogan Bai san ze shigo
kanon ba harsu Gama su koma to matsalar madam din ce inaga ta caza Masa Kai Wai
cewa fa yayi daina amsa Masa waya tayi".
"Kamar ya Bata amsa masa waya? Batasan kowaye bane da zata ringa yi masa haka?"
"Eh kusan hakan ne gaskiya"
"Allah ya rufa asiri" ta fada.
Sukayi sallama ta kashe Kiran tana dariya "su oga anzo hannu ana walagigi da
rayuwar 'yan Mata gashi kaima kazo hannun yarinya tana juyaka son ranta, nasan bana
raba Daya biyu saboda shi ta rufe wayarta jiya, taki magana dashi a wayar Ya Sameer
karshe ma ta sakata jirgi, yes! Haka nake son irin matansu su kasance, idan suka
samu wadda ta mace a kansu ta Zama sorry Amma wannan ta shuka mulkinta yanda takeso
tunda Batasan waye shi ba".
Ya juya ta koma kitchen inda tabar su zilai suna aiki, tana shiga zilan tace Wai ni
lafiya yarinyar Nan? naji shirun yayi yawa ko dai rakani zakiyi na gano lafiyarta
kada na Zama babbar kwabo an hadoni da yarinya nayi wasarere da lamarinta".
'yar dariya. Rukayya tayi "gaskiya kinaji da matar big bro irin wannan shiga damuwa
jiya fa ko barcin kirki bakiyi ba kina zaman jiranmu yau ma tun Asuba kike ta
nemanta, ki kwantar da hankalin ki Aunty sirikinki ne ya taho ba Shirin wannan 'yar
taki tsaye ce taki saurarensa ko a waya dole ya tsallake hidimominsa ya nufo
Nigeria".
Iya Rahane ce ta aje Wukar hannunta tana duban Rukayya "kikace uban gidan mu ya
shigo garin?"
"Kwarai kuwa iya jiya cikin dare ya shigo Kinga kuwa sai ki fadawa Aunty ta kauda
Kai kawai gurin son ganin 'yarta ba yanzu ba gaskiya, Dan haka da an gama aikin Nan
zamu bar Nan Bangaren mu koma wancan".
"Wannan gaskiya ne inba tayi dalili ba yaushe zamu shigo wannan guri harda kwana a
cikinsa, Amma dalilin uwar dakinmu mun dangwali arziki ai wannan ba komai bane akan
gidan da aka sauke mu a sokoto, Kai Naga inda arziki ya amsa sunansa wannan yaro
uwarsa tayi farar haihuwa wallahi Nan kusa Banga mutane masu karamcin su ba, uwarsa
yarinya karama sai halin girma".
Ita dai zilai sai ta rasa Wai wannan maganar dawa ake ne waye suke zance a kansa ne
ita fa maganar Zahra take musu su Kuma sun kamo wata tashar Ina hadin zahra ba
Wanda suke magana a kansa ko dai Mai gidan ne ya dawo Basu gane me take nufi ba,
ita Zahra matar Almajirin Malam Bukar Wanda gidan zaman ma na Baba Malam ne mutanen
da yaje yiwa aiki turawa suka gyara Masa shi, to Ina shi Ina wannan Aljqnnar
duniyar suda aka kawosu zaman 'yan kwanaki na ganin likita.
Cikin nuna mamaki zilan tace "ikon Allah ai ban sani ba kice da anyi uwar banza
gara da Kika fada min kada naje nakai kaina girma ta Fadi".
"Ai Koda kin shiga basa Nan ba a nan suka kwana ba".
Wayar Rukayya ce tayi qara ta dauka ta fice daga kitchen din shine abinda ya Hana
zilai fadar abinda tayi niyyar tambayarki Rukayyar.
Hira iya rahane taci gaba da yiwa zilai a Kan Mahmud amma ko Daya zilan Bata gano
ainishin waye take magana a kansa ba.

You might also like